Sashe 45
Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Sai misalin sha biyu da rabi muka tashi daga gurin karatu ji nayi kamar naje gida na kwanta na huta saboda gajiya da tunani duk sun sa karatun ma bana ganewa, har na nufi gurinmu sai kuma na sanja shawara 'bangaransa na nufa domin gabatar da aikina idan yaso idan na gama sai na huta gabadaya.......koda na shiga gurin samun su Haruna nayi a zaune suna hira kallo guda nayi masa naga ramar da yayi girgiza kaina nayi muka gaisa sama-sama na shigesu.
Yana zaune a falo yana kallo nayi sallama, ya amsa tare da 'kure ni da ido, babu yabo babu fallasa na gaishe shi, ya amsa min fuskarsa a sake kamar bashi ba, kicin na nufa, ya dakatar dani.
Cikin 'kosawa na tsaya ina kallonsa yace."Me ya hanaki kizo ki had'a min breakfast. " ?
"Kayi hakuri naje gurin karatu ne kasancewar yau lahadi duk rana irin ta yau muna zaunawa da wuri mu tashi da wuri wannan dalilin yasa banzo akan lokaci ba.''
Yace." Me zai hana kizo gurina duk ranakun asabar da lahadin na dunga karantar dake." cike da mamaki nake kallonsa. Yace."Ko kina ganin ba zan iya ba."! girgiza kaina nayi nace" ba haka nake nufi ba kawai abar maganar yanzu ka fadi abinda kake bukatar kaci."!
"Bana bukatar naci wani abu.'' Na dinga kallonsa ina mamakin maganarsa ganin yana min shu'umi kallo yasa na 'bata rai juyawa nayi zan bar gurin yace." Kin san d'azu muyi magana da mahaifinki ko."?
Wani irin kallo na watsa masa, 'bata fuska yayi yace."Abun naki kuma nema yake ya wuce gona da iri ni kikewa wannan kallon.
Tsaki nayi niyyar ja sai na fasa, nace"To kunyi magana da babana sai akayi me."? Cikin nuna isa yace."Ya tabbatar min da cewa ya mallaka min ke ko kina da ja ne."? girgiza kaina nayi nace"Bani da ja sai abinda Allah ya kaddara a kaina amma ka sani idan ka samu nasarar aurena to zaka sha mamakin abinda zai biyo baya."
Kai tsaye yace."In dai ta bangaranki ne ban damu ba saboda duk girma da karfin da kike dashi baki fi karfina ba." Girgiza kaina nayi na wuce kicin zuciyata nayi min zafi! babu shakka guy nan da gaske yake aurena zaiyi ya lalata min rayuwa, koda na shiga kicin din kasa kata'bus nayi na nemi guri na zauna tare da zabga uban tagumi! iyayena na farin ciki zan auri dan sarki! ni kuma ina 'bakin ciki domin nasan da aniyar da zai aureni babu shakka ina jin tsoran ranar da zai sako musu ni a matsayin bazawara shin wane irin hali zasu shiga idan haka ta kasance wannan shine babban abinda ya dame ni, to a takaice dai sai da na shafe kusan rabin awa a zaune a kicin din ina sa'kawa da kwancewa kafin na mike da sanyayyan jiki na fara aikace aikace na.
Magajin sarki sai da dare ya samu zama da mahaifinsa cikin nutsuwa ya sheda masa abinda yake tafe dashi, maimartaba ya dinga kallonsa yana mamakin maganar dake tafe dashi.
Magajin sarki jikinsa ne yayi sanyi dan ganin yanda Maimartabar ya nuna a lokacin da yaji maganar dake tafe dashi, yace."Ranka ya dad'e naga kamar maganar da nake tafe da ita bata gamsar da kai ba."
Maimartaba yace."Kwarai kuwa maganar bata gamsar dani ba Magajin sarki ka duba wata yarinyar wannan da kake magana akanta ka hakura tsayin wata uku iyayen yaran suka same ni da maganar auran 'ya'yansu nasa albarka a ciki sannan daga baya kai kuma kazo da wata magana, bana so na amince maka jama'a suga rashin adalcina yarinyar nan Sumayya ba ita kadai bace mace a masarautar nan ka duba da kyau ka samo wata sai na shige maka gaba amma wannan dai tunda wani ya rigaka sai ka hakura."
Wani irin gumi ne ya shiga tsatstsafo masa bai ta'ba tsammanin zai samu matsala daga gurin mahaifin nasa ba, yace."Ranka ya dad'e yanda na yarda na amince da yarinyar nan ko Lawisa ban yarda da ita ba, yarinyar nan sumayya tana tsaye a kaina sosai take bani kulawa ta kowane fanni wannan dalilin ne yasa naji ina sha'awar auranta."
Maimartaba ya sauke ajiyar zuciya yace."Nima nasan da haka domin mahaifiyarka na fada min irin kokarin da yarinyar take a kanka babu shakka zanso ka aureta domin ta cigaba da kula da kai sai dai kash!! ba zan iya shige maka gaba akan al'amarin ba saboda dalilina dana fada maka idan nine mahaifinka to na umarceka daka janye maganar auranta ka nemi wata."
Magajin sarki kasa motsi yayi a gurin ya dinga jin zazzabi mai zafi na nema ya rufe shi, Mamma dake gefe guda a zaune tace"Magajin sarki kabi umarnin mahaifinka ka janye maganar auran yarinyar nan kamar yanda ya bukata idan so kake ka had'a mata biyu sai ka duba wata koda a cikin bayin ne insha Allahu zamu shige maka gaba."
Murya na rawa yace."Mamma ke kin san mahimancin yarinyar nan a tare dani ke kika hadani da ita ina ganin duk wacce zan nema ba zata kama kafarta ba yarinyar nada gaskiya da rikon amana mamma kiyi wani abu akan wannan al'amarin."
Girgiza kanta tayi tace"Magajin sarki zan fi kowa so ka auri yarinyar nan saboda ni nasan wacece ita amma a yanzu ni bani da wata magana tunda mahaifinka ya yanke hukunci shikkenan magana ta kar'e sai dai mu roki Allah yasa haka shi yafi alkairi." shuru yayi tare da sunkuyar da kansa kasa
Washe gari da wurwuri na shiga saboda nasan da wuri yake tafiya aiki yasa na shiga sashen da wuri, shuru lokacin dana shiga kai tsaye kicin na wuce na fara aikina, kunun gyada na dama masa na soya masa kosai a gurguje na shirya komai a tire na dauka na fito kenan na hangoshi yana saukowa yanda naga fuskarsa a murtuke yasa nasha jinin jikina! kai tsaye hanyar futa ya nufa, baki na na rawa nace ranka ya dade "Barka da asuba zaka fita baka karya ba kayi hakuri dan Allah bangama akan lokaci b.......kafin na 'karasa ya juyo a fusace! ya doki! tire din hannuna! a take fulas din kunun ya tintsira murfin ya cire ya kwaro min a kirjina mazubin 'kosan kuwa tuni ya fad'i a kasan gurin k'osan ya watse a gurun, rad'ad'in zafi ya gigita ni da sauri na jefar da tire din a kasa ina kiran innalillahi! gami da yarfe ruwan kunun dake rigata ......Fulas din kunun ne ya gangara kusa da kafarsa ya sameshi da yake Takalmin dake kafarsa mai yatsa ne! da sauri ya janye 'kafarsa yana dubawa
Ido jawur nake kallonsa tsabar takaici da bakin ciki yasa hawaye ya kwace min, kallonsa kawai nakeyi bakina na rawa , bangaransa kuwa bai tsammaci hakan da yayi mata zata samu tsautsayi ba yayi mata ne dan ya huce fushinsa sai gashi kuma ya 'kona mata kirji da ruwan kunu!!! a sanyaye ya dinga bin kirjinta da kallo fatar duk tayi ja! ta soma tashi, sai yaji gabad'aya ya saduda dan ya lura ta k'one sosai! Inda nake ya nufo yana karasowa na daga hannu da niyyar marin sa, rike hannuna yayi yana kallona!!! a marairace yace."Sorry banyi tsammanin zaki 'kone ba." Fuzge hannuna nayi da sauri na tureshi na kama hanya zan bar gurin, kawai naji ya ru'ko 'kuguna tsam! ya d'ora ha'barsa a kafad'ata, bakinsa yasa daidai kunnena a sanyaye yace."Kiyi hakuri." Gabadaya ji nayi jikina yay sanyi na dinga zubar da hawayen bakin ciki babu shakka Yarima ya zame min karfan 'kafa ya shiga rayuwata yana yanda yake so da ita.............
Yana zaune a falo yana kallo nayi sallama, ya amsa tare da 'kure ni da ido, babu yabo babu fallasa na gaishe shi, ya amsa min fuskarsa a sake kamar bashi ba, kicin na nufa, ya dakatar dani.
Cikin 'kosawa na tsaya ina kallonsa yace."Me ya hanaki kizo ki had'a min breakfast. " ?
"Kayi hakuri naje gurin karatu ne kasancewar yau lahadi duk rana irin ta yau muna zaunawa da wuri mu tashi da wuri wannan dalilin yasa banzo akan lokaci ba.''
Yace." Me zai hana kizo gurina duk ranakun asabar da lahadin na dunga karantar dake." cike da mamaki nake kallonsa. Yace."Ko kina ganin ba zan iya ba."! girgiza kaina nayi nace" ba haka nake nufi ba kawai abar maganar yanzu ka fadi abinda kake bukatar kaci."!
"Bana bukatar naci wani abu.'' Na dinga kallonsa ina mamakin maganarsa ganin yana min shu'umi kallo yasa na 'bata rai juyawa nayi zan bar gurin yace." Kin san d'azu muyi magana da mahaifinki ko."?
Wani irin kallo na watsa masa, 'bata fuska yayi yace."Abun naki kuma nema yake ya wuce gona da iri ni kikewa wannan kallon.
Tsaki nayi niyyar ja sai na fasa, nace"To kunyi magana da babana sai akayi me."? Cikin nuna isa yace."Ya tabbatar min da cewa ya mallaka min ke ko kina da ja ne."? girgiza kaina nayi nace"Bani da ja sai abinda Allah ya kaddara a kaina amma ka sani idan ka samu nasarar aurena to zaka sha mamakin abinda zai biyo baya."
Kai tsaye yace."In dai ta bangaranki ne ban damu ba saboda duk girma da karfin da kike dashi baki fi karfina ba." Girgiza kaina nayi na wuce kicin zuciyata nayi min zafi! babu shakka guy nan da gaske yake aurena zaiyi ya lalata min rayuwa, koda na shiga kicin din kasa kata'bus nayi na nemi guri na zauna tare da zabga uban tagumi! iyayena na farin ciki zan auri dan sarki! ni kuma ina 'bakin ciki domin nasan da aniyar da zai aureni babu shakka ina jin tsoran ranar da zai sako musu ni a matsayin bazawara shin wane irin hali zasu shiga idan haka ta kasance wannan shine babban abinda ya dame ni, to a takaice dai sai da na shafe kusan rabin awa a zaune a kicin din ina sa'kawa da kwancewa kafin na mike da sanyayyan jiki na fara aikace aikace na.
Magajin sarki sai da dare ya samu zama da mahaifinsa cikin nutsuwa ya sheda masa abinda yake tafe dashi, maimartaba ya dinga kallonsa yana mamakin maganar dake tafe dashi.
Magajin sarki jikinsa ne yayi sanyi dan ganin yanda Maimartabar ya nuna a lokacin da yaji maganar dake tafe dashi, yace."Ranka ya dad'e naga kamar maganar da nake tafe da ita bata gamsar da kai ba."
Maimartaba yace."Kwarai kuwa maganar bata gamsar dani ba Magajin sarki ka duba wata yarinyar wannan da kake magana akanta ka hakura tsayin wata uku iyayen yaran suka same ni da maganar auran 'ya'yansu nasa albarka a ciki sannan daga baya kai kuma kazo da wata magana, bana so na amince maka jama'a suga rashin adalcina yarinyar nan Sumayya ba ita kadai bace mace a masarautar nan ka duba da kyau ka samo wata sai na shige maka gaba amma wannan dai tunda wani ya rigaka sai ka hakura."
Wani irin gumi ne ya shiga tsatstsafo masa bai ta'ba tsammanin zai samu matsala daga gurin mahaifin nasa ba, yace."Ranka ya dad'e yanda na yarda na amince da yarinyar nan ko Lawisa ban yarda da ita ba, yarinyar nan sumayya tana tsaye a kaina sosai take bani kulawa ta kowane fanni wannan dalilin ne yasa naji ina sha'awar auranta."
Maimartaba ya sauke ajiyar zuciya yace."Nima nasan da haka domin mahaifiyarka na fada min irin kokarin da yarinyar take a kanka babu shakka zanso ka aureta domin ta cigaba da kula da kai sai dai kash!! ba zan iya shige maka gaba akan al'amarin ba saboda dalilina dana fada maka idan nine mahaifinka to na umarceka daka janye maganar auranta ka nemi wata."
Magajin sarki kasa motsi yayi a gurin ya dinga jin zazzabi mai zafi na nema ya rufe shi, Mamma dake gefe guda a zaune tace"Magajin sarki kabi umarnin mahaifinka ka janye maganar auran yarinyar nan kamar yanda ya bukata idan so kake ka had'a mata biyu sai ka duba wata koda a cikin bayin ne insha Allahu zamu shige maka gaba."
Murya na rawa yace."Mamma ke kin san mahimancin yarinyar nan a tare dani ke kika hadani da ita ina ganin duk wacce zan nema ba zata kama kafarta ba yarinyar nada gaskiya da rikon amana mamma kiyi wani abu akan wannan al'amarin."
Girgiza kanta tayi tace"Magajin sarki zan fi kowa so ka auri yarinyar nan saboda ni nasan wacece ita amma a yanzu ni bani da wata magana tunda mahaifinka ya yanke hukunci shikkenan magana ta kar'e sai dai mu roki Allah yasa haka shi yafi alkairi." shuru yayi tare da sunkuyar da kansa kasa
Washe gari da wurwuri na shiga saboda nasan da wuri yake tafiya aiki yasa na shiga sashen da wuri, shuru lokacin dana shiga kai tsaye kicin na wuce na fara aikina, kunun gyada na dama masa na soya masa kosai a gurguje na shirya komai a tire na dauka na fito kenan na hangoshi yana saukowa yanda naga fuskarsa a murtuke yasa nasha jinin jikina! kai tsaye hanyar futa ya nufa, baki na na rawa nace ranka ya dade "Barka da asuba zaka fita baka karya ba kayi hakuri dan Allah bangama akan lokaci b.......kafin na 'karasa ya juyo a fusace! ya doki! tire din hannuna! a take fulas din kunun ya tintsira murfin ya cire ya kwaro min a kirjina mazubin 'kosan kuwa tuni ya fad'i a kasan gurin k'osan ya watse a gurun, rad'ad'in zafi ya gigita ni da sauri na jefar da tire din a kasa ina kiran innalillahi! gami da yarfe ruwan kunun dake rigata ......Fulas din kunun ne ya gangara kusa da kafarsa ya sameshi da yake Takalmin dake kafarsa mai yatsa ne! da sauri ya janye 'kafarsa yana dubawa
Ido jawur nake kallonsa tsabar takaici da bakin ciki yasa hawaye ya kwace min, kallonsa kawai nakeyi bakina na rawa , bangaransa kuwa bai tsammaci hakan da yayi mata zata samu tsautsayi ba yayi mata ne dan ya huce fushinsa sai gashi kuma ya 'kona mata kirji da ruwan kunu!!! a sanyaye ya dinga bin kirjinta da kallo fatar duk tayi ja! ta soma tashi, sai yaji gabad'aya ya saduda dan ya lura ta k'one sosai! Inda nake ya nufo yana karasowa na daga hannu da niyyar marin sa, rike hannuna yayi yana kallona!!! a marairace yace."Sorry banyi tsammanin zaki 'kone ba." Fuzge hannuna nayi da sauri na tureshi na kama hanya zan bar gurin, kawai naji ya ru'ko 'kuguna tsam! ya d'ora ha'barsa a kafad'ata, bakinsa yasa daidai kunnena a sanyaye yace."Kiyi hakuri." Gabadaya ji nayi jikina yay sanyi na dinga zubar da hawayen bakin ciki babu shakka Yarima ya zame min karfan 'kafa ya shiga rayuwata yana yanda yake so da ita.............