Sashe 38
Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ciroma na zaune a dakinsa yana jijjiga kafarsa ya kalli Muddibo rai a bace yace."Gabadaya al'amarin beyi min dadi ba naso ace Shi wanda akayi aikin dominsa shine ya mutu ba bawan sa ba, amma babu komai insha Allahu hak'an mu sai ya cimma ruwa a kansa."
Muddibo cikin rashin jin dadi yace."Nima wallahi gabadaya al'amarin beyi min dadi ba amma ina ganin dole ne mu d'auki shawarar mu ta biyu akansa amma ba zamu gabatar da komai ba yanzu sai 'kura ta lafa tukkuna."
Ciroma shuru yayi yana kumbura fuska, hannu ya mika ya dauki tufa yasa a bakinsa yana taunawa yana girgiza kansa yaso ace Yarima ne ya sheqa barzahu da yafi jin dadin hakan amma babu damuwa shima ba zai tsallake tarkonsu ba.
Kai tsaye bangaran mahaifiyarsa ya nufa, koda ya shiga samun iyayen nasa yayi sunyi jugum! kana ganinsu kasan suna cikin alhini da damuwa, zama yayi kansa a kasa ya gaishe su, suka amsa suna binsa da kallon tausayi da jin kai irin na iyaye da tuni ma'kiya sun samu galaba a kansa,
A nutse yace." Ranka ya dade ya mukaji da wannan mummunan al'amari daya faru.'' maimartaba ya sauke ajiyar zuciya yace."Sai godiyar Allah kuma muna nan muna addua akan Allah ya bayyana mana wa'inda suke da hannu a cikin wannan al'amarin shi kuma wannan yaro daya riga mu gidan gaskiya muna rokon Allah ya jikansa da gafara.""
A nutse ya amsa da ameen kafin yace.'' Ranka ya dad'e kafin na fito daga asibiti nayi binkice sosai akan abincin da ya janyo faruwar al'amarin sosai nayi binkice na gane matsalar daga cikin man da akayi amfani dashi ne ina tunanin ya samu matsala ma'ana yayi expire shine dalilin daya janyo yayi musu lahani a ciki
Cike da mamaki suke kallonsa, Fulani tace"Yanzu kana nufin man suya shi ka dai zai iya janyo a rasa rai suma fa sauran Allah ne yayi da sauran kwanansu a gaba da da tsautsayi da tuni sai da labarinsu gaskiya ban yarda da maganarka ba."
Maimartaba yace."Anya kuwa Yarima kayi binkice yanda ya kamata nima ina ganin man suya shi kadai ba zai janyo hakan ba
Murmushi yayi yana kokarin danne damuwarsa yace."Ranka ya dade ku yarda da maganata gaskiya ce dan kafin na yanke hukunci sai da nayi binkice sosai akan abinda ya janyo faruwar al'amarin nan man suya zai iya kisa mutukar ya tashi daga aiki ma'ana lokacin sa ya wuce ranka ta dade ka tuna kayan abincin dake bangare na a store suke a rufe shi kansa man a gwangwani yake a rufe kuma ya dauki lokaci mai tsayi a ajiye yarinyar nan da tayi aikin abincin bata da ilmin da zata duba ta ga lalacewar abu ta dauka tayi amfani dashi bayan ya gur'bata wannan dalilin yasa na yanke shawara kan cewa gobe idan Allah ya kaimu duk zan sa a fito da kayan abincin dake cikin store d'ina a fita dasu can wani guri a zubar sabida gudun afkuwar wata matsalar." Maimartaba shuru yayi duk jikinsa yayi sanyi tabbas hakan na iya kasancewa
"Babana nifa ban yarda da wannan maganar taka ba, har yaushe ka dawo garin da kayan abincin ka zasu lalace kuma me yasa lokacin da wannan yarinyar Sumayya take maka girki ba'a samu matsala makamanciyar wannan ba, nidai ina zargin wannan yarinya Suwaiba da Safiyya ta kawo maka."
Girgiza kansa yayi yana kokarin kawar da damuwarsa yace."Mamma dan Allah ki daina zargin kowa akan faruwar wannan al'amari na fad'a miki ga dalili ki yarda a haka ke dai kawai ki cigaba dayi min addua akan Allah ya kare ni daga kowane abin qi."
Jikinta ne yayi sanyi tace"To shikkenan babana Allah ya kare ka da kariyarsa." Maimartaba yace."Da har nasa an rufe yaran guda biyu to tunda gaskiyar lamari ta bayyana idan ka fita sai kasa a bud'e su." Yace."To godiya suke ranka ya dad'e." Sarki jijjiga kansa yayi yana kallon yaron nasa tare dayi masa addua a cikin zuciyarsa, mikewa yayi a nutse yace."Ni zan shiga gurina na huta a tashi lafiya." Fulani tace"To babu damuwa yanzu zan aiko maka da abinci nasan dai kana bukatarsa." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Mamma tsabar fargaba da tension ya sanya cikina ya cushe amma babu damuwa ki aiko zanci insha Allah.'' maimartaba yace."Ka daure kaci abinci kada ka zauna da yunwa komai yayi tsanani maganinsa Allah.'' Yace."Insha Allah." Sallama yayi musu suka bishi da kyakkyawar addua.
*Na kudi ne..*!
Kada ki karanta min littafi sai kin biya, keda ki ka fita da book din keda Allah....idan kina so ki biya ga yanda abin yake...vip group #600 normal #300 accont..0542382124...Binta umar gtbank....Idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
67&68
kame-kame ya fara yana so ya tuna tsayin kwanakin da yarinyar ta dauka bata zuwa aiki, ganin yana kwane-kwane yasa ta 'bata fuskarta a kaurare tace"Babana baka da gaskiya duk yanda akayi kaine ka kore ta da 'bakin halinka."
Da sauri yace."Haba mamma kada kiyi min wannan shedar mana wallahi ni banyi mata komai ba kawai wayar gari nayi naga bata zuwa aiki shiyasa ai nace ki aika a kirata a gabana idan nayi mata wani abu sai ta fada."
Fulani jikinta ne yayi sanyi tace"Yanzu duk tsayin wannan lokacin a'ina kake samun abinci ni dai baka ta'ba zuwa ka nemi abinci a gurina ba." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Mamma ki kwantar da hankalinki na gane abinda kike gudu insha Allah babu abinda zasuyi ya same ni." Tace"Insha Allah ka dai fada min inda kake samun abinci."
takarashe maganar idonta a tsaye a kansa
"Mamma Lawisa ce take kawo min daga 'bangaransu." Fulani shuru tayi tana kallonsa tana girgiza kanta shikkenan tasan sun wanke sun bashi yasha sai dai kawai ta dage da addua a kansa ba tun yau ba tasan wacece Hajiya Karima macece mai biye biyen malamai duk ta d'ora 'ya'yanta a turba mara kyau shiyasa gabadaya bata kaunar auransa da Lawisa saboda tasan zasuyi tayi wa yaron ta surkulle......."Mamma akwai matsala ne naga kinyi shuru kina girgiza kai."
Ajiyar zuciya ta sauke tace"Bani da abinda zance sai dai addua akan lamarin Lawisa ita zaka aura dan ta baka abinci kaci ba laifi bane amma kafin kaci duk abinda zata kawo maka naci ko nasha ka dinga addua tukkuna."
A sanyaye yace."Insha Allah zan kiyaye." Wayarta dake kusa da ita dauka ta kira Jakadiyarta, taba umarnin kiran Sumayya.
Ina zaune tsakar gidanmu ina bitar karatun al'kur'ani Jakadiya ta shigo, ganinta ya sanya min faduwar gaba, al'kur'anin na rufe a nutse muka gaisa da juna tace"Fulani ce tace kizo tana neman ki." Kafin nayi magana Tambaya tace Allah yasa dai lafiya." jakadiya tace."Lafiya lau babu wani abu insha Allah." Ganin yanda Tambaya ta razana yasa nayi saurin daidaita kaina nace"To shikkenan kice mata ganin zuwa." Jakadiya ta amsa da to ta tafi. mikewa nayi ina yar dariya na kalleta nace"Wai mai yasa duk sanda aka aiko kirana daga cikin gida kika tsorata."
Cike da kulawa tace"Dole na tsorara Sumayya bana son wani abu ya same ki na sharri na fahimci mutane nayi mana hassada saboda kawai kina kula da Yarima Lami da sauransu duk sun daina amsa gaisuwata ko haduwa mukayi a gurin rabon abinci basa kulani wani lokacin ina ji suna gulmar mu shiyasa nake jin tsoro kada a shirya miki wani sharrin."
Murmushi nayi nace"Kada ki damu insha Allahu babu abinda zai faru sai al'kairi maganar su Lami kuma ki ajiye ta a gefe kiyi abinda ke gabanki Hassada sukeyi idan sun gaji zasu bari."
Tace."To shikkenan Sumayya amma ki 'kara kula kinji ko." Nace"Insha Allah zan kiyaye." Takalmana nasa nayi mata sallama na tafi.
Cikin nutsuwa nayi sallama na shiga falon, 'kamshin turaransa ya tabbatar min da cewa yana gurin, kaina na sunkuyar kasa na cigaba da tafiya a nutse har na karasa inda suke na zube a gabanta cikin ladabi nace"Barka da dare ranki ya dad'e."
Cikin kulawa kamar koda yaushe ta amsa da "barka dai Sumayya ina fatan kuna lafiya.?
" Lafiya lau ranki ya dade Jakadiya ta sanar dani kina nema na.'' a nutse na fadi maganar ina kara yin kasa da kaina ban yarda na kalli gefan da yake zaune ba ta gefan idona nake ganin irin kallon da yake min cikin zuciyata nace "Kallo sai kace sabon makaho."
Falon ne yayi shuru na minti biyu kafin naji muryarta a nutse ta kira sunana.
Amsawa nayi ba tare dana dago ba, Tace."Inaso ki fada min dalilin da yasa kika daina zuwa aikin sashen Yarima ashe kin watsar da amanar dana baki ban sani ba."
A sanyaye nace"Ranki ya dade ki gafarce ni ba daina zuwa aiki nayi ba wallahi kwana biyu ne nake ta rashin lafiya shine dalilin da yasa na daina zuwa."
A yanda ta fadi maganar tana rawar murya yasa ta gane karya take, Tace"Haba Sumayya mai cuta ai ya fita daban ki dube ki fa a dan tsayin kwanakin da nayi banganki ba kin 'kara girma ban yarda baki da lafiya ba kina 'boye min wani abune ki fad'i min gaskiyar magana shin me babana yayi miki kika daina zuwa ki kula dashi."
Shuru nayi dan gabadaya ta daureni da jijiyoyin jikina, tace"Kina jin tsoron ki fada min kada yayi miki wani abu ko."? Da sauri nace"ba haka bane Mamma ki yarda da maganata ta farko bani da lafiya ne amma ni Yarima beyi min komai ba kuma insha Allahu gobe zan cigaba da zuwa aikina."
Murmushi tayi tana girgiza kanta tace"Shikkenan tunda kin 'boye kin kasa fada min gaskiya ni zan baki hakuri akan laifin da yayi miki dan Allah ki daure ki cigaba da kula dashi har lokacin da Allah zai kawo lokacin auransa insha Allah kin kusa hutawa tunda an tsayar da rana wata uku masu zuwa idan matarsa nada ra'ayin zamanki domin ki cigaba da yi musu hidima to sai ki cigaba da zama idan kuma bata da ra'ayi sai ta kawo sabbi su cigaba da gabatar da aikin da kika bari ina fata kin fahimce ni kuma kin huce fushin ki."
Muddibo cikin rashin jin dadi yace."Nima wallahi gabadaya al'amarin beyi min dadi ba amma ina ganin dole ne mu d'auki shawarar mu ta biyu akansa amma ba zamu gabatar da komai ba yanzu sai 'kura ta lafa tukkuna."
Ciroma shuru yayi yana kumbura fuska, hannu ya mika ya dauki tufa yasa a bakinsa yana taunawa yana girgiza kansa yaso ace Yarima ne ya sheqa barzahu da yafi jin dadin hakan amma babu damuwa shima ba zai tsallake tarkonsu ba.
Kai tsaye bangaran mahaifiyarsa ya nufa, koda ya shiga samun iyayen nasa yayi sunyi jugum! kana ganinsu kasan suna cikin alhini da damuwa, zama yayi kansa a kasa ya gaishe su, suka amsa suna binsa da kallon tausayi da jin kai irin na iyaye da tuni ma'kiya sun samu galaba a kansa,
A nutse yace." Ranka ya dade ya mukaji da wannan mummunan al'amari daya faru.'' maimartaba ya sauke ajiyar zuciya yace."Sai godiyar Allah kuma muna nan muna addua akan Allah ya bayyana mana wa'inda suke da hannu a cikin wannan al'amarin shi kuma wannan yaro daya riga mu gidan gaskiya muna rokon Allah ya jikansa da gafara.""
A nutse ya amsa da ameen kafin yace.'' Ranka ya dad'e kafin na fito daga asibiti nayi binkice sosai akan abincin da ya janyo faruwar al'amarin sosai nayi binkice na gane matsalar daga cikin man da akayi amfani dashi ne ina tunanin ya samu matsala ma'ana yayi expire shine dalilin daya janyo yayi musu lahani a ciki
Cike da mamaki suke kallonsa, Fulani tace"Yanzu kana nufin man suya shi ka dai zai iya janyo a rasa rai suma fa sauran Allah ne yayi da sauran kwanansu a gaba da da tsautsayi da tuni sai da labarinsu gaskiya ban yarda da maganarka ba."
Maimartaba yace."Anya kuwa Yarima kayi binkice yanda ya kamata nima ina ganin man suya shi kadai ba zai janyo hakan ba
Murmushi yayi yana kokarin danne damuwarsa yace."Ranka ya dade ku yarda da maganata gaskiya ce dan kafin na yanke hukunci sai da nayi binkice sosai akan abinda ya janyo faruwar al'amarin nan man suya zai iya kisa mutukar ya tashi daga aiki ma'ana lokacin sa ya wuce ranka ta dade ka tuna kayan abincin dake bangare na a store suke a rufe shi kansa man a gwangwani yake a rufe kuma ya dauki lokaci mai tsayi a ajiye yarinyar nan da tayi aikin abincin bata da ilmin da zata duba ta ga lalacewar abu ta dauka tayi amfani dashi bayan ya gur'bata wannan dalilin yasa na yanke shawara kan cewa gobe idan Allah ya kaimu duk zan sa a fito da kayan abincin dake cikin store d'ina a fita dasu can wani guri a zubar sabida gudun afkuwar wata matsalar." Maimartaba shuru yayi duk jikinsa yayi sanyi tabbas hakan na iya kasancewa
"Babana nifa ban yarda da wannan maganar taka ba, har yaushe ka dawo garin da kayan abincin ka zasu lalace kuma me yasa lokacin da wannan yarinyar Sumayya take maka girki ba'a samu matsala makamanciyar wannan ba, nidai ina zargin wannan yarinya Suwaiba da Safiyya ta kawo maka."
Girgiza kansa yayi yana kokarin kawar da damuwarsa yace."Mamma dan Allah ki daina zargin kowa akan faruwar wannan al'amari na fad'a miki ga dalili ki yarda a haka ke dai kawai ki cigaba dayi min addua akan Allah ya kare ni daga kowane abin qi."
Jikinta ne yayi sanyi tace"To shikkenan babana Allah ya kare ka da kariyarsa." Maimartaba yace."Da har nasa an rufe yaran guda biyu to tunda gaskiyar lamari ta bayyana idan ka fita sai kasa a bud'e su." Yace."To godiya suke ranka ya dad'e." Sarki jijjiga kansa yayi yana kallon yaron nasa tare dayi masa addua a cikin zuciyarsa, mikewa yayi a nutse yace."Ni zan shiga gurina na huta a tashi lafiya." Fulani tace"To babu damuwa yanzu zan aiko maka da abinci nasan dai kana bukatarsa." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Mamma tsabar fargaba da tension ya sanya cikina ya cushe amma babu damuwa ki aiko zanci insha Allah.'' maimartaba yace."Ka daure kaci abinci kada ka zauna da yunwa komai yayi tsanani maganinsa Allah.'' Yace."Insha Allah." Sallama yayi musu suka bishi da kyakkyawar addua.
*Na kudi ne..*!
Kada ki karanta min littafi sai kin biya, keda ki ka fita da book din keda Allah....idan kina so ki biya ga yanda abin yake...vip group #600 normal #300 accont..0542382124...Binta umar gtbank....Idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
67&68
kame-kame ya fara yana so ya tuna tsayin kwanakin da yarinyar ta dauka bata zuwa aiki, ganin yana kwane-kwane yasa ta 'bata fuskarta a kaurare tace"Babana baka da gaskiya duk yanda akayi kaine ka kore ta da 'bakin halinka."
Da sauri yace."Haba mamma kada kiyi min wannan shedar mana wallahi ni banyi mata komai ba kawai wayar gari nayi naga bata zuwa aiki shiyasa ai nace ki aika a kirata a gabana idan nayi mata wani abu sai ta fada."
Fulani jikinta ne yayi sanyi tace"Yanzu duk tsayin wannan lokacin a'ina kake samun abinci ni dai baka ta'ba zuwa ka nemi abinci a gurina ba." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Mamma ki kwantar da hankalinki na gane abinda kike gudu insha Allah babu abinda zasuyi ya same ni." Tace"Insha Allah ka dai fada min inda kake samun abinci."
takarashe maganar idonta a tsaye a kansa
"Mamma Lawisa ce take kawo min daga 'bangaransu." Fulani shuru tayi tana kallonsa tana girgiza kanta shikkenan tasan sun wanke sun bashi yasha sai dai kawai ta dage da addua a kansa ba tun yau ba tasan wacece Hajiya Karima macece mai biye biyen malamai duk ta d'ora 'ya'yanta a turba mara kyau shiyasa gabadaya bata kaunar auransa da Lawisa saboda tasan zasuyi tayi wa yaron ta surkulle......."Mamma akwai matsala ne naga kinyi shuru kina girgiza kai."
Ajiyar zuciya ta sauke tace"Bani da abinda zance sai dai addua akan lamarin Lawisa ita zaka aura dan ta baka abinci kaci ba laifi bane amma kafin kaci duk abinda zata kawo maka naci ko nasha ka dinga addua tukkuna."
A sanyaye yace."Insha Allah zan kiyaye." Wayarta dake kusa da ita dauka ta kira Jakadiyarta, taba umarnin kiran Sumayya.
Ina zaune tsakar gidanmu ina bitar karatun al'kur'ani Jakadiya ta shigo, ganinta ya sanya min faduwar gaba, al'kur'anin na rufe a nutse muka gaisa da juna tace"Fulani ce tace kizo tana neman ki." Kafin nayi magana Tambaya tace Allah yasa dai lafiya." jakadiya tace."Lafiya lau babu wani abu insha Allah." Ganin yanda Tambaya ta razana yasa nayi saurin daidaita kaina nace"To shikkenan kice mata ganin zuwa." Jakadiya ta amsa da to ta tafi. mikewa nayi ina yar dariya na kalleta nace"Wai mai yasa duk sanda aka aiko kirana daga cikin gida kika tsorata."
Cike da kulawa tace"Dole na tsorara Sumayya bana son wani abu ya same ki na sharri na fahimci mutane nayi mana hassada saboda kawai kina kula da Yarima Lami da sauransu duk sun daina amsa gaisuwata ko haduwa mukayi a gurin rabon abinci basa kulani wani lokacin ina ji suna gulmar mu shiyasa nake jin tsoro kada a shirya miki wani sharrin."
Murmushi nayi nace"Kada ki damu insha Allahu babu abinda zai faru sai al'kairi maganar su Lami kuma ki ajiye ta a gefe kiyi abinda ke gabanki Hassada sukeyi idan sun gaji zasu bari."
Tace."To shikkenan Sumayya amma ki 'kara kula kinji ko." Nace"Insha Allah zan kiyaye." Takalmana nasa nayi mata sallama na tafi.
Cikin nutsuwa nayi sallama na shiga falon, 'kamshin turaransa ya tabbatar min da cewa yana gurin, kaina na sunkuyar kasa na cigaba da tafiya a nutse har na karasa inda suke na zube a gabanta cikin ladabi nace"Barka da dare ranki ya dad'e."
Cikin kulawa kamar koda yaushe ta amsa da "barka dai Sumayya ina fatan kuna lafiya.?
" Lafiya lau ranki ya dade Jakadiya ta sanar dani kina nema na.'' a nutse na fadi maganar ina kara yin kasa da kaina ban yarda na kalli gefan da yake zaune ba ta gefan idona nake ganin irin kallon da yake min cikin zuciyata nace "Kallo sai kace sabon makaho."
Falon ne yayi shuru na minti biyu kafin naji muryarta a nutse ta kira sunana.
Amsawa nayi ba tare dana dago ba, Tace."Inaso ki fada min dalilin da yasa kika daina zuwa aikin sashen Yarima ashe kin watsar da amanar dana baki ban sani ba."
A sanyaye nace"Ranki ya dade ki gafarce ni ba daina zuwa aiki nayi ba wallahi kwana biyu ne nake ta rashin lafiya shine dalilin da yasa na daina zuwa."
A yanda ta fadi maganar tana rawar murya yasa ta gane karya take, Tace"Haba Sumayya mai cuta ai ya fita daban ki dube ki fa a dan tsayin kwanakin da nayi banganki ba kin 'kara girma ban yarda baki da lafiya ba kina 'boye min wani abune ki fad'i min gaskiyar magana shin me babana yayi miki kika daina zuwa ki kula dashi."
Shuru nayi dan gabadaya ta daureni da jijiyoyin jikina, tace"Kina jin tsoron ki fada min kada yayi miki wani abu ko."? Da sauri nace"ba haka bane Mamma ki yarda da maganata ta farko bani da lafiya ne amma ni Yarima beyi min komai ba kuma insha Allahu gobe zan cigaba da zuwa aikina."
Murmushi tayi tana girgiza kanta tace"Shikkenan tunda kin 'boye kin kasa fada min gaskiya ni zan baki hakuri akan laifin da yayi miki dan Allah ki daure ki cigaba da kula dashi har lokacin da Allah zai kawo lokacin auransa insha Allah kin kusa hutawa tunda an tsayar da rana wata uku masu zuwa idan matarsa nada ra'ayin zamanki domin ki cigaba da yi musu hidima to sai ki cigaba da zama idan kuma bata da ra'ayi sai ta kawo sabbi su cigaba da gabatar da aikin da kika bari ina fata kin fahimce ni kuma kin huce fushin ki."