Sashe 35
Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cike da mamaki yace."Ban fahimci maganarka ba." Shatima da murmushi a fuskarsa yace."Kana son yarinyar nan alamu sun nuna min hakan wannan dalilin yasa na fadi wannan maganar.
Baki a sake yake kallonsa yana mamakin yanda akayi yayi saurin gane shi.
Shatima yace."Yanayin yanda aka kasa 'boye bacin ranka da kishinka yasa na gane tsananin son da kakewa yarinyar naji dadin hakan sosai kuma yarinyar ta dace da kai domin duk ta had'a abubuwan da ake bukata ina maka fatan alkairi."
Rai a 'bace yace."Shatima kai yanzu ta ina ka hango dacewa ta da yarinyar nan ka dube ta da kyau kuwa ka gani na rasa wacce zan aura sai ita."
Shatima yace."Gaskiya ka bani mamaki Ali yanzu dan Allah wace dacewa kake nema bayan wannan ? meye aibun yarinyar nan Sumayya ta cika mace kuma ta kai ta zama matar Sarki governor ko shugaban kasa, tana da kyau daidai misali kana tana da kyawawan halaye to me kuma ake nema a gurin 'ya mace."?
Girgiza kansa ya shiga yi yace."Shatima mu bar wannan maganar dan Allah yarinyar nan bata dace dani ba saboda bata da ilimin da zatayi goyayya dani ta kowane fanni."
Shatima yace."Mutukar tana da ilimin addini to baka da matsala dan wani ilimin boko ba wani abun damuwa bane ilimin addini shine abin dubawa saboda haka ina me baka shawara akan kayi wani abu akai idan kuma ka tsaya wasa nima zan shiga kawai dan dab'iun yarinyar da kyawun halayenta na burgeni ina so na aureta mace mai hankali da nutsuwa kodan na samu 'yaya masu tarbiya.
Yarima Ali shuru yayi yana kallon Shatima da ya dage yana ta gwarzanta kyawu da kyawawan d'abi'un yarinyar..........Yace."To shikkenan naji maganarka zan zauna nayi nazari akai." Shatima yace."Yawwa ko kaifa wallahi sosai nayi maka sha'awar auran yarinyar saboda kun dace da juna."
Bayan fitar Shatima tunani ya shiga yi akan maganarsu, shima yasan yarinyar nada kyawawan halaye wanda ko wane namiji zai sha'awar auranta, to amma ai idan ya zauna yayi duba na tsanaki zai fahimci cewar yarinyar bata dace da ta zama matarsa ba saboda ita din ma'kas'kanciya ce a gurinsa a kasan sa take babu yanda za'ayi ya auri baiwarsa a matsayinsa na Yarima dan Sarki babu macan data dace dashi sai Yar sarki ko yar wani mai mulki ko Lawisa ma zai aureta ne badan yana sonta ba kawai dai abinda yasa ya kwantar da hankalinsa da auranta saboda ya hango akwai mamora a jikinta shine dalilin da yasa bai damu ba, amma abin kunya ne abokananshi su san matsayin matarsa Sumayya sam ba tsaran auransa bace, amma zai duba ya gani yana ganin ko ya aureta ba zaiyi yarda ya haihu da itaba zata zame masa matar biyan bukatarsa. wannan shawarar ya yankewa kansa.
Bayan kwana biyu al'amura sunyi sauki kullum da safe idan na fita daga gurinmu gurin karatu nake tafiya acan nake yini nayi ta karatun al'kur'ani da sauran littafai sai yamma likis nake dawowa, Tambaya da babana duk basu san da cewar na daina zuwa sashen Yarima ba tinda kullum ba'a gida nake yini ba shiyasa basu gane komai ba..........Koda Haruna ya same ni da maganar kasa 'boye masa nayi saboda na riga nasan irin kaunar da yake min, Haruna ya dinga mamaki al'amarin yace."Sumayya a gaskiya nima ban goyi da bayan ki cigaba da zuwa ba, kiyi zamanki idan Fulani ta kira ki kan maganar sai ki san abinda zaki ce mata." nace"To shikkenan da wannan muka rufe maganar Yarima muka shiga hirar soyayyarmu.
Yarima Ali tun bayan damuwa da rashin zuwanta har abun ya soma damunsa kullum idan zaici abinci sai yayi takaici da bacin rai dan Suwaiba sam bata iya girki ba wani sa'in inda ta ajiye abincin haka take zuwa ta tarar da abunta beci ba, wani lokacin kuma idan yaci loma daya yaji babu dadi kiranta yake yayi tai mata masifa irin wacce yake min akanta yake huce fushinsa, Suwaiba ta dinga data sanin zuwanta sashen dan komai tayi masa bata gwaninta.
Umartar Gimbiya Lawisa yayi data dinga kawo masa abinci dan baya tsammanin zai iya tunkarar mahaifiyarsa da maganar daina zuwa yarinyar yasan dole ta binciki dalili shiyasa ya kasa tunkararta sai ya Umarci gimbiya Lawisa da ta dinga kawo masa daga sashen su, Lawisa abin nema ya samu kullum xata zauna ta tsara masa girke girke safe da rana da dare ta barbade da maganin mallaka ta kawo masa sashensa, ta zauna yana ci suna hira babban burinta maganinta yayi tasiri a kansa, aikuwa ha'kan ta ya cimma ruwa dan yanzu sun daina fad'a yana nuna mata kulawa farin ciki tamkar ya kasheta......
Bayan wata biyu al'amura suna ta tafiya cikin nutsuwa yanzu na manta na daina fargabar abinda zai biyo baya tunda naga har an dauki tsayin wannan lokaci fulani bata kirani da wata magana ba sai hankalina ya kwanta sosai na cigaba da karatuna maganar auranmu da Haruna kuwa an tsayar da lokaci wata shida mai zuwa Mahaifina da Mahaifin Haruna har gaban Sarki sukaje suka sheda masa abinda ke faruwa, Sarki ya nuna farin cikinsa kana kuma yasa mana albarka.......Tsakanina da Haruna soyayya mai karfi ta sake 'kulluwa Bangaran Lahira kuwa abun nata sai a hankali dan daukar gaba tayi dani ta daina yi min magana, na tambayeta dalili taki fada min sai nima kawai na tattarata na watsar da ita na cigaba da sabgogina hankalina a kwance..
Bangaran Magajin Sarki kuwa sai godiyar Allah Cikin nasara da yardar Ubangiji ya fara aiki a asibitinsa yayin da jama'ar gari ke zirga zirga cikin asibitin domin nemawa kansu da 'ya'yansu lafiya kamar yanda ya fada a ranar Walima haka Asibitin na dauke da 'kwarrarun ma'aikata wa'inda suka san aikinsu wannan dalilin ya sanya hatta da manyan mutane masu kudi suke zuwa a dubasu a asibitin, alhamdulillhi bukatarsa ta biya ta kowane b'angare sai abu guda dake damunsa shine yanda zai tunkari Hadimarsa ya fada mata cewar ya yanke hukuncin auranta kamar yanda ta bukata ya amince zai aureta ita da Lawisa a rana daya, kullum da tunanin yanda zai tunkare ta da maganar yake kwana yake tashi gabadaya kunyar hada ido yake da ita sabida abin da yayi mata, amma yana ganin tilas yaje ya samu mahaifiyarsa ya shirya mata wata maganar akan rashin zuwan yarinyar gurinsa.
Karfe takwas da rabi na dare ya samu mahaifiyar tasa a kishingide akan dadduma ta idar da sallah tana jan carbi, a nutse ya zauna a gabanta tare da mika gaisuwarsa, ta amsa da fuska a sake tace"Babana aiki ya 'boye ka bana ganin ka a kan lokaci."
Murmushi yayi yace."Wallahi kuwa Mamma wannan dalilin yasa ma na yanke shawara cewa kullum kafin na fita zan dinga shigowa mu gaisa sabida wani lokacin bana shigowa gida da wuri sai can dare.
Tace"Aikuwa dai hakan shine daidai ina fatan komai yana tafiya cikin nutsuwa da kwanciyar hankali." Yace."Alhmdullhi mamma komai na tafiya daidai jama'a da yawa najin dadin alkairin da kukayi musu kullum cikin yi muku addua sukeyi." Murmushin jin dadi tayi tace"Alhamdullhi dama babban burinmu shine mu faranta ran mabukata kaima Allah ya saka maka da alkairi ya baka ladan abinda kake yi.".
"Ameeen Mamma na." Dakin ne yayi shuru na minti biyu kafin ya dago kansa a nutse yace."Mamma wannan yarinyar dake yi min hidima kwana biyu ta dauke kafarta ta daina zuwa ni ban san dalili ba rashin samun zama yasa ban shigo na sheda miki ba sai yanzu dana shigo gidan da wuri nace bari nazo na sheda miki halin da ake ciki ko zaki aika a kira ta gani gata gaki sai ta fad'i abinda akai mata ta daina zuwa tayi aikinta ."
Fulani mikewa tayi zaune tana kallonsa da mamaki a fuskarta tace"Babana har tsayin wane lokaci sumayya ta dauka bata tare da kai."?
*Na kudi ne*
Idan kika karanta baki biya ba Allah ya isa! idan kina so ki biya ga yanda abin yake...VIP gruop#600 normal group #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
63&64
'Bangaran Yarima Ali kuwa al'amarin ne ya dinga bashi mamaki! kamarshi yarinyar nan ta fitar da hannu ta tsinka masa mari! wannan al'amari ya girgiza mutuka kaf a tarihin rayuwarsa ba'a ta'ba cin mutuncinsa kamar na yau ba amma babu komai yasan duk abinda ya faru shine ya janyowa kansa kamar yanda yarinyar ta fada kafin ta fita, yana ganin dole ya hakura da ita komai k'ulafucinsa kuwa tunda raini da wulakanci ya soma shiga tsakaninsu, lallai dole ya kafa tarihi da yarinyar dan tunda yake babu 'ya macan da ta ta'ba yi masa abinda ta aikata masa, mari!! abin ya bashi mugun mamaki ta yanda har ya rasa wane irin hukunci zai yanke akanta
........Yana ganin ko kawai yabi shawarar ta ta farko wato ya aureta tunda taki bashi hadin kai idan ya biya bukatarsa sai ya saketa dan shi abin kunya ne a gurinsa ace itace matarsa sam bata kai matsayin da zaiyi zaman aure da ita ba, amma dole zai zauna yayi nazari da tunani akan al'amarin yanzu babban burinsa ya wulakantata kamar yanda ta wulakanta shi ta mare shi ba tare da taji tsoron abinda zai biyo baya ba, da kyar ya iya barin falon duk jikinsa yayi sanyi nadama da kunyar hada ido da yarinyar duk ya dameshi.
Washe gari da zazzabi na tashi na dinga daurewa domin bana so iyayena su fahimci abinda ke damuna.
Muna gama karyawa na nemi guri na kwanta ina lumshe idona babu abinda ke damuna sai al'amarin daya faru jiya har yanzu na kasa yanke hukunci.
"Sumayya ya kika koma kika kwanta kuma ki tashi kiyi wanka ki shirya jikin ki yau ai kaya zamu sa masu kyau tunda Walima za'a gudanar.
Tambaya ce take wannan maganar a lokacin da take tsaye a kaina.
bude idona nayi ina kallonta, tace" Ki tashi ga ruwa can na dora nasan yanzu yayi zafi sai kiyi wankan'' nace"Sai fa sha daya na rana za'a zauna zaman Walimar." Tace''To idan kinyi wankan ai kin huta."
Mikewa zaune nayi ina gyara daurin dankwalina.
Baki a sake yake kallonsa yana mamakin yanda akayi yayi saurin gane shi.
Shatima yace."Yanayin yanda aka kasa 'boye bacin ranka da kishinka yasa na gane tsananin son da kakewa yarinyar naji dadin hakan sosai kuma yarinyar ta dace da kai domin duk ta had'a abubuwan da ake bukata ina maka fatan alkairi."
Rai a 'bace yace."Shatima kai yanzu ta ina ka hango dacewa ta da yarinyar nan ka dube ta da kyau kuwa ka gani na rasa wacce zan aura sai ita."
Shatima yace."Gaskiya ka bani mamaki Ali yanzu dan Allah wace dacewa kake nema bayan wannan ? meye aibun yarinyar nan Sumayya ta cika mace kuma ta kai ta zama matar Sarki governor ko shugaban kasa, tana da kyau daidai misali kana tana da kyawawan halaye to me kuma ake nema a gurin 'ya mace."?
Girgiza kansa ya shiga yi yace."Shatima mu bar wannan maganar dan Allah yarinyar nan bata dace dani ba saboda bata da ilimin da zatayi goyayya dani ta kowane fanni."
Shatima yace."Mutukar tana da ilimin addini to baka da matsala dan wani ilimin boko ba wani abun damuwa bane ilimin addini shine abin dubawa saboda haka ina me baka shawara akan kayi wani abu akai idan kuma ka tsaya wasa nima zan shiga kawai dan dab'iun yarinyar da kyawun halayenta na burgeni ina so na aureta mace mai hankali da nutsuwa kodan na samu 'yaya masu tarbiya.
Yarima Ali shuru yayi yana kallon Shatima da ya dage yana ta gwarzanta kyawu da kyawawan d'abi'un yarinyar..........Yace."To shikkenan naji maganarka zan zauna nayi nazari akai." Shatima yace."Yawwa ko kaifa wallahi sosai nayi maka sha'awar auran yarinyar saboda kun dace da juna."
Bayan fitar Shatima tunani ya shiga yi akan maganarsu, shima yasan yarinyar nada kyawawan halaye wanda ko wane namiji zai sha'awar auranta, to amma ai idan ya zauna yayi duba na tsanaki zai fahimci cewar yarinyar bata dace da ta zama matarsa ba saboda ita din ma'kas'kanciya ce a gurinsa a kasan sa take babu yanda za'ayi ya auri baiwarsa a matsayinsa na Yarima dan Sarki babu macan data dace dashi sai Yar sarki ko yar wani mai mulki ko Lawisa ma zai aureta ne badan yana sonta ba kawai dai abinda yasa ya kwantar da hankalinsa da auranta saboda ya hango akwai mamora a jikinta shine dalilin da yasa bai damu ba, amma abin kunya ne abokananshi su san matsayin matarsa Sumayya sam ba tsaran auransa bace, amma zai duba ya gani yana ganin ko ya aureta ba zaiyi yarda ya haihu da itaba zata zame masa matar biyan bukatarsa. wannan shawarar ya yankewa kansa.
Bayan kwana biyu al'amura sunyi sauki kullum da safe idan na fita daga gurinmu gurin karatu nake tafiya acan nake yini nayi ta karatun al'kur'ani da sauran littafai sai yamma likis nake dawowa, Tambaya da babana duk basu san da cewar na daina zuwa sashen Yarima ba tinda kullum ba'a gida nake yini ba shiyasa basu gane komai ba..........Koda Haruna ya same ni da maganar kasa 'boye masa nayi saboda na riga nasan irin kaunar da yake min, Haruna ya dinga mamaki al'amarin yace."Sumayya a gaskiya nima ban goyi da bayan ki cigaba da zuwa ba, kiyi zamanki idan Fulani ta kira ki kan maganar sai ki san abinda zaki ce mata." nace"To shikkenan da wannan muka rufe maganar Yarima muka shiga hirar soyayyarmu.
Yarima Ali tun bayan damuwa da rashin zuwanta har abun ya soma damunsa kullum idan zaici abinci sai yayi takaici da bacin rai dan Suwaiba sam bata iya girki ba wani sa'in inda ta ajiye abincin haka take zuwa ta tarar da abunta beci ba, wani lokacin kuma idan yaci loma daya yaji babu dadi kiranta yake yayi tai mata masifa irin wacce yake min akanta yake huce fushinsa, Suwaiba ta dinga data sanin zuwanta sashen dan komai tayi masa bata gwaninta.
Umartar Gimbiya Lawisa yayi data dinga kawo masa abinci dan baya tsammanin zai iya tunkarar mahaifiyarsa da maganar daina zuwa yarinyar yasan dole ta binciki dalili shiyasa ya kasa tunkararta sai ya Umarci gimbiya Lawisa da ta dinga kawo masa daga sashen su, Lawisa abin nema ya samu kullum xata zauna ta tsara masa girke girke safe da rana da dare ta barbade da maganin mallaka ta kawo masa sashensa, ta zauna yana ci suna hira babban burinta maganinta yayi tasiri a kansa, aikuwa ha'kan ta ya cimma ruwa dan yanzu sun daina fad'a yana nuna mata kulawa farin ciki tamkar ya kasheta......
Bayan wata biyu al'amura suna ta tafiya cikin nutsuwa yanzu na manta na daina fargabar abinda zai biyo baya tunda naga har an dauki tsayin wannan lokaci fulani bata kirani da wata magana ba sai hankalina ya kwanta sosai na cigaba da karatuna maganar auranmu da Haruna kuwa an tsayar da lokaci wata shida mai zuwa Mahaifina da Mahaifin Haruna har gaban Sarki sukaje suka sheda masa abinda ke faruwa, Sarki ya nuna farin cikinsa kana kuma yasa mana albarka.......Tsakanina da Haruna soyayya mai karfi ta sake 'kulluwa Bangaran Lahira kuwa abun nata sai a hankali dan daukar gaba tayi dani ta daina yi min magana, na tambayeta dalili taki fada min sai nima kawai na tattarata na watsar da ita na cigaba da sabgogina hankalina a kwance..
Bangaran Magajin Sarki kuwa sai godiyar Allah Cikin nasara da yardar Ubangiji ya fara aiki a asibitinsa yayin da jama'ar gari ke zirga zirga cikin asibitin domin nemawa kansu da 'ya'yansu lafiya kamar yanda ya fada a ranar Walima haka Asibitin na dauke da 'kwarrarun ma'aikata wa'inda suka san aikinsu wannan dalilin ya sanya hatta da manyan mutane masu kudi suke zuwa a dubasu a asibitin, alhamdulillhi bukatarsa ta biya ta kowane b'angare sai abu guda dake damunsa shine yanda zai tunkari Hadimarsa ya fada mata cewar ya yanke hukuncin auranta kamar yanda ta bukata ya amince zai aureta ita da Lawisa a rana daya, kullum da tunanin yanda zai tunkare ta da maganar yake kwana yake tashi gabadaya kunyar hada ido yake da ita sabida abin da yayi mata, amma yana ganin tilas yaje ya samu mahaifiyarsa ya shirya mata wata maganar akan rashin zuwan yarinyar gurinsa.
Karfe takwas da rabi na dare ya samu mahaifiyar tasa a kishingide akan dadduma ta idar da sallah tana jan carbi, a nutse ya zauna a gabanta tare da mika gaisuwarsa, ta amsa da fuska a sake tace"Babana aiki ya 'boye ka bana ganin ka a kan lokaci."
Murmushi yayi yace."Wallahi kuwa Mamma wannan dalilin yasa ma na yanke shawara cewa kullum kafin na fita zan dinga shigowa mu gaisa sabida wani lokacin bana shigowa gida da wuri sai can dare.
Tace"Aikuwa dai hakan shine daidai ina fatan komai yana tafiya cikin nutsuwa da kwanciyar hankali." Yace."Alhmdullhi mamma komai na tafiya daidai jama'a da yawa najin dadin alkairin da kukayi musu kullum cikin yi muku addua sukeyi." Murmushin jin dadi tayi tace"Alhamdullhi dama babban burinmu shine mu faranta ran mabukata kaima Allah ya saka maka da alkairi ya baka ladan abinda kake yi.".
"Ameeen Mamma na." Dakin ne yayi shuru na minti biyu kafin ya dago kansa a nutse yace."Mamma wannan yarinyar dake yi min hidima kwana biyu ta dauke kafarta ta daina zuwa ni ban san dalili ba rashin samun zama yasa ban shigo na sheda miki ba sai yanzu dana shigo gidan da wuri nace bari nazo na sheda miki halin da ake ciki ko zaki aika a kira ta gani gata gaki sai ta fad'i abinda akai mata ta daina zuwa tayi aikinta ."
Fulani mikewa tayi zaune tana kallonsa da mamaki a fuskarta tace"Babana har tsayin wane lokaci sumayya ta dauka bata tare da kai."?
*Na kudi ne*
Idan kika karanta baki biya ba Allah ya isa! idan kina so ki biya ga yanda abin yake...VIP gruop#600 normal group #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
63&64
'Bangaran Yarima Ali kuwa al'amarin ne ya dinga bashi mamaki! kamarshi yarinyar nan ta fitar da hannu ta tsinka masa mari! wannan al'amari ya girgiza mutuka kaf a tarihin rayuwarsa ba'a ta'ba cin mutuncinsa kamar na yau ba amma babu komai yasan duk abinda ya faru shine ya janyowa kansa kamar yanda yarinyar ta fada kafin ta fita, yana ganin dole ya hakura da ita komai k'ulafucinsa kuwa tunda raini da wulakanci ya soma shiga tsakaninsu, lallai dole ya kafa tarihi da yarinyar dan tunda yake babu 'ya macan da ta ta'ba yi masa abinda ta aikata masa, mari!! abin ya bashi mugun mamaki ta yanda har ya rasa wane irin hukunci zai yanke akanta
........Yana ganin ko kawai yabi shawarar ta ta farko wato ya aureta tunda taki bashi hadin kai idan ya biya bukatarsa sai ya saketa dan shi abin kunya ne a gurinsa ace itace matarsa sam bata kai matsayin da zaiyi zaman aure da ita ba, amma dole zai zauna yayi nazari da tunani akan al'amarin yanzu babban burinsa ya wulakantata kamar yanda ta wulakanta shi ta mare shi ba tare da taji tsoron abinda zai biyo baya ba, da kyar ya iya barin falon duk jikinsa yayi sanyi nadama da kunyar hada ido da yarinyar duk ya dameshi.
Washe gari da zazzabi na tashi na dinga daurewa domin bana so iyayena su fahimci abinda ke damuna.
Muna gama karyawa na nemi guri na kwanta ina lumshe idona babu abinda ke damuna sai al'amarin daya faru jiya har yanzu na kasa yanke hukunci.
"Sumayya ya kika koma kika kwanta kuma ki tashi kiyi wanka ki shirya jikin ki yau ai kaya zamu sa masu kyau tunda Walima za'a gudanar.
Tambaya ce take wannan maganar a lokacin da take tsaye a kaina.
bude idona nayi ina kallonta, tace" Ki tashi ga ruwa can na dora nasan yanzu yayi zafi sai kiyi wankan'' nace"Sai fa sha daya na rana za'a zauna zaman Walimar." Tace''To idan kinyi wankan ai kin huta."
Mikewa zaune nayi ina gyara daurin dankwalina.