← Book details Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 47 OF 90

Sashe 47

Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Tun kafin ya k'arasa ya hangosu a tsaye koda ya karasa gurun samun fuskokinsu yayi cikin yanayi na alhini da damuwa Mussaman shi maimartaban ya hango tsantsar tashin hankali a cikin kwayoyin idanunsa.........Cikin yanayi na damuwa yace."Allah ya baka yawan rai al'amarin nan fa da yake ta faruwa wallahi ko shakka ba nayi dasa hannun masarauta a ciki wa'inda baka ta'ba tsammanin zasu aikata wannan mummunan aikin ba zakayi mamaki idan binkice ya nuna maka su......Ciroma da Galadima jikinsu yayi sanyi suka maida hankalinsu kansa da fadin"Kai a iya bunciken ka wa kake tunanin zai aikatawa Yarima wannan mummunan aikin kada fa ka manta dukkaninmu cibiyarmu d'aya ya za'ayi wasu daga cikinmu su zama bara gurbi."

Shatima yace."Ni dai na fad'i abinda nake hasashe nasan kuma tabbas idan an tsananta binkice akan al'amarin a samu wa'inda suke da hannu a cikin al'amarin."
Ciroma cikin dakiya da nuna shi mai gaskiya ne yace."Shatima kayi gaskiya da wannan maganar insha Allahu zamu tsananta binkice domin gano wa'inda suke kokarin su kawo mana rud'ani a cikin wannan masarautar mai albarka."

Waziri ya sauke ajiyar Zuciya cikin sanyi yace."Yana da kyau muje mu zauna mu jirayi dawowar Yariman amma a gaskiya wannan al'amarin yayi tsanani duk wanda yake shirya wannan abu to babu shakka rayuwar Aliyu yake nema saboda haka yana da kyau dukkaninmu mu zauna domin mu kawo karshen wannan matsala."

Maimartaba ya sauke zazzafar ajiyar zuciya a nutse yace."Ku muje fada mu zauna mu tattauna domin mu samu mafita." Gabad'aya suka nufi fada kowa na sa'ke-sa'ke a zuciyarsa.

"Wayyo Allah na shiga uku na lalace Wayyo! Allahna."!!! Muryar Laure mahaifiyar Haruna mukaji ta shigo tana kurma ihu! had'e da fad'in ta shiga uku ta lalace.!!! da sauri mukayo waje muna rarraba ido! Laure ta shigo a jigace! tayi kozai kozai da ita sai ihu! take tana fadin ta shiga uku! gabadaya rikicewa nayi na nufe ta ina kokarin rik'eta kawai naji saukar mari a kumatuna, kafin ta cukume ni tana fad'in " Sumayya kece kika kashe min d'ana ni dake zanyi kuka ba da kowa ba Haruna yaron arziki ya mutu ya barni a duniya na shiga uku na lalace."!!!!! tana gunjin kuka takarashe maganar, kallonta na dinga yi bakina na rawa nace" ki fad'a min abinda ke fa...ruwa." wuya na ta ri'ke tamau! ta matseni a bango (garu) tace" Ni zaki mayar shashasha ko ? kina nufin bakin san abinda ke faruwa."? Hawaye ne suka kwace min nace"Wallahi tallahi bansan abinda ke faruwa ba dan Allah kiyi min bayani amma kada kice min Masoyina ya mutu."

Wani gigitaccan marin ta dauke ni dashi jikinta na rawa tace"Haruna ba masoyinki bane makiyin ki ne tunda har kika iya bashi guba yaci ya mutu to Haruna bashi da babbar abin 'ki kamar ke."
Kallonta nakeyi inaso nayi magana bakina yayi nauyi jiri ne ya shiga d'iba na ina jin sautin muryarta a kunnena silalewa nayi na fad'i a gurin, sama-sama naji salatin Tambaya a kaina..............Idona na bude a hankali ina kalle kalle Tambaya na gani a gurfane a gabana tana kuka tare da shafa min ruwa a fuskata, a furgice na mike zaune ta rike ni "Sumayya kwanta ki huta kada ki tashi." Girgiza kaina nayi cikin nauyin baki nace."Ina Laure take."? Tace."Me zakiyi mata."? kai tsaye nace."Inaso ta tabbatar min da gaskiyar mafarkina." Hawaye ta share tace"Sumayya ki shiga hankalinki ki samu nutsuwa ki kad'aita Allah ki sani Allah shike rayawa kuma shi ke kashewa babu mahalukin da ya isa yayi wannan al'amarin idan ba Ubangiji ba kawai kiyi wa Haruna kyakkyawar addua da samun rahamar Allah."

Wasu zafafan hawaye ne suka 'kwace min nace"Da gaske ne ashe."? kanta ta daga min....Rungumeta nayi tare da fashe da kuka "Wayyo Allah na shiga ukun...bakina ta rufe min kafin karasa, naji tana nanata kalmar innalillahi da sauri nima na kar'ba na dinga yi da karfi ina wani irin kuka mai tsuma zuciya, Yarima bukatarsa ta biya ya kashe Haruna yaji dadi dama yace." yana da hanyoyin da zai iya ruguza mana farin cikin mu tabbas dana san da gaske yake zai kashe min masoyi to dana bashi abinda yake bukata! da karfi nace"Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un wannan masarauta akwai azzalimai a cikinta."!!! Da sauri ta rufe min baki ta dago ni tana kallona tace"Sumayya wace irin magana ce wannan? ashe kina so ki janyo mana masifa."? Ina kuka nace"Shine ya kashe shi wallahi shine dama yace sai yaga karshen soyayyarmu bukatarsa ta biya ya kashe shi ya huta."

*Na kudi ne...!*
Kada ki karanta min littafi idan baki biya ba ke kuma da kika futa da book din keda Allah! idan kina bukatar biyan kudin ga yanda abin yake...Vip gruop#600 normal gruop#300 account... 0542382124..Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA*
*SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊�)
79
Wani irin kallon mamaki Tambaya keyi min, ina gunjin kuka nace"Da gaske ne shine ya kashe shi dama yace yana da hanyoyi da yawa da zai iya raba tsakanina dashi domin ya samu nasarar aurena."!
Tambaya kafad'una ta ri'ke tana jijjigani tace."Sumayya ki shiga nutsuwarki dan Allah ki daina sambatu sai surutai kikeyi marasa kan gado da ma'ana shin waye wannan da kike magana akansa."?.

Hanci na sha'ka na kalleta har yanzu na kasa tsayar da ruwan hawayen dake zuba nace"Tambaya Yarima yayi al'kawarin sai ya aureni ko ta halin 'ka'ka bayan mahaifinsa ya gargadeshi akan ya janye maganar aurena sai ya 'kudiri mummunar aniya a kanmu nida Haruna ya tabbatar min da cewa duk rintsi sai ya san yanda yayi ya aureni domin biyan bukatarsa."

Kallona ta dinga yi tana girgiza kanta gabadaya yanayin ta ya nuna alamun tsoro da tashin hankali......Ganin kawai ta kura min ido tana kallo yasa nayi yun'kurin mikewa, tayi saurin rike hannuna na zauna jiki a sanyaye tace"Sumayya da gaske kike Yarima ne silar mutuwar Haruna." Murya a dashe nace."Tabbas ko shakka ba nayi shine ya kashe s......! saurin rufe min baki tayi kafin na karasa maganar dukkaninmu muka kalli bakin kofa saboda sawun tafiyar mutane da mukaji......Murya na rawa tace"Sumayya ki bar wannan maganar a cikin ki duk rintsi kada ki fito da i ta, idan kin fad'a Yarima yayi silar mutuwar Haruna babu shakka zamu shiga tashin hankali a masarautar n........Katse maganarta tayi dalilin shigowar babana da wasu 'yan sanda guda biyu mace da namiji. cikin tashin hankali muka
Mi'ke tsaye. "Malam wannan ce Sumayyan ko."? A sanyaye Lawi ya daga kansa. ya kalli 'yar uwarsa da fad'in ''Merry je kiyi aikin ki." Gani nayi ta nufo inda nake da ankwa a hannunta, bakina ya dinga motsi jikina ya dinga karkarwa a lokacin gabadaya kwakwalwata toshewa tayi na dinga tunanin adduar da zanyi, Tambaya kuwa kuka ta fashe ta durkushe a gurin tana rirrik'e kafar ma'aikaciyyar a lokacin da take kokarin daure min hannu.

Kallonta tayi cikin yanayin hausarta tace."Kiyi hakuri ba zamuyi mata komai ba mutukar bata wahalar damu ba." Tambaya ta kalli namijin tana kuka tace"Dan darajar Allah da annabi kada ku tafi da ita wallahi bata da laifi akan faruwar wannan al'amari." Yace."baba dole ne ayi binkice akan 'yarki domin itace ta girka abincin dake dauke da guba a ciki idan ba tayi mana gardama ba to zata samu sassauci idan kuwa ta tsaya gardama za tasha wuya a gurinmu." Tambaya kallona tayi tana marairaicewa! naji wani irin tausayinsu ya rufe ni, babana tsabar tashin hankali duk kammaninsa sun sauya ya kasa magana kawai ya jingina jikin bango (garu) sai kallonmu yake.

Cikin kokarin danne tashin hankalina nace"Tambaya ki daina kuka dan Allah kiyi min addua insha Allahu mai gaskiya baya ta'bewa Allah zai kub'tar dani daga dukkanin wata musiba."

Mi'kewa tsaye tayi tana kokarin magana suka tasa 'keya ta, Lawi da saurin gaske ya shiga daki yana share hawaye ita kuwa Tambaya bayanmu ta biyo tana kuka had'e da ri'ke min hannun riga sai hakuri take bawa jami'an tsaron.........Dandazon mutanan dake gurin yasa nayi saurin sunkuyar da kaina kasa na dinga tafiya kaina a sunkuye ina kiran sunan Allah a zuciyata, motarsu suka saka ni, na dukufar da kaina k'asa band'ago kaina ba har sai dana muka fita daga gidan.

Suna zaune suna tattanawa dangane da faruwar al'amarin sa'kon mai girma governor ya iso, mai girma governor yayi umarni da cewa lallai a rufe asibitin *ZINARIYA HOSPITAL* sai gwamnati ta gama binkice akan mutuwar da mutane keyi a cikin asibitin." Maimartaba beji ciwo akan umarnin governor ba koda bai bada umarin rufe asibitin ba dama ya yanke shawarar rufe shi..........Galadima da Ciroma cike da tsantsar farin ciki suka bar fada, suka had'u a gurin guda suna ta 'bab'baka dariya bukatarsu ta fara biya gwamnati ta shigo cikin al'amarin zasu san yanda zasuyi su had'a kai da gwamnatin domin su ruguza asibitin.
Chapter 47 · 0% Book details