Sashe 10
Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tsayawa nayi ina jira yayi gaba nabi bayansa ya nuna min hanya da hannunsa ba tare da yace komai ba na fahimci abinda yake nufi da sauri nayi gaba ya rufa min baya.
Yanayin tafiya ta da tashi ba daya bane koda na waiwaya sai naga nayi masa nisa sosai d'an tsayawa nayi ina jiran zuwanshi.....Bangaran shi kuwa tafiya kawai yake amma hankalinsa tuntuni ya tashi sakamakon yanayin tafiyar da takeyi sassan jikinta na motsawa mazaunanta ba 'karamin tayar masa da hankali yayi ba hakan ya sake sanya masa rashin kuzari da karfin jiki ya dinga tafiya tamkar wanda 'kwai ya fashewa a ciki gabad'aya sha'awarshi ta tashi yana so ya samu yarinyar da zata d'ebe masa kewa.
Sai da ya kusa zuwa dab dani sannan na juya na cigaba da tafiya.....Yarima Ali ajiyar zuciya ya sauke ya tsirawa faffad'an qugunta ido wanda yake juyawa cikin zanin kamfalar dake jikinta........ajiyar zuciya ya dinga saukewa yana kokarin danne abinda ke taso masa.
Koda muka shiga gurin namu Tambaya dake bakin rijiya tana wanke kwanuka mikewa tayi da sauri ganina tare dashi yasa hankalinta ya tashi tana tsoro ko wani abu ne ya faru, ganin ta razana yasa nace"Ki kwantar da hankalinki babu abinda ya faru Yarima zai duba jikin babana ne."
Zubewa tayi gabansa tana gaisheshi gami dayi masa godiya. Cikin sanyin murya ya amsa tare da bata umarnin mi'kewa.
Na kalleshi a nutse nace"Ranka ya dade bisimillah ka shigo." Takalmansa ya cire a nutse ya rankwafa domin shiga dakin dake gajeriyar kofa ce shi kuma ya kasance mutum mai tsayi shine dalilin da yasa ya risina domun shiga dakin.
Guri na shiga karkad'ewa wai ko zai zauna, sai naga yaja ya tsaya yana kallon babana dake kwance yana bacci.....Cikin rawar baki nace"Ka ganshi ko wallahi yana jin ji......! hannu ya daga min alamanun baya bukatar maganata, nayi shuru ina kallonsa sai kallon babana yake kafin ya kalleni yace"Ina maganin da kuke bashi."?
Da sauri na dauko na mika masa, ya jima yana duba magungunan kafin ya miko min da fadin"Kada ku sake bashi maganin ku ajeshi zamuje yanzu nasa Haruna ya samo masa wasu insha Allah zasuyi masa."
Da sauri nace"To mungode shima na hausan da muke bashi mu daina."? Kallona yayi da sauri yace."Bayan wannan maganin akwai wanda kuke bashi."? nace."Eh akwai na hausa wanda na kar'bo gurin masu maganin gargajiya."
Tsaki! yaja da fad'in"Jeki dauko min maganin nagani." Na mike da sauri na fita tsakar gida na samu Tambaya ta gama wanke kwanuka tana tsaye jikin bango (garu)ta rungume hannuwanta a kirji.
"Tambaya ina maganin da ki'ka jiqawa babana." Da sauri ta shiga wani daki dake tsakar gidan ta dauko maganin cikin bokitin roba madaidaici karba nayi da sauri na shiga dakin, na mika masa .
"Ajiye ki bud'e nagani." Ajiyewa nayi a kasan guri nayi yanda yace. Ni dashi gabad'aya tsirawa maganin ido mukayi ganin yanda yake wata irin kumfa ga wari na tashi a cikinsa.
Dauke kansa yay rai a b'ace yace."Rufe." Jiki a sanyaye na rufe ina kallonsa, Yace."Wannan maganin kwanansa nawa a jiqe."? a sanyaye nace"Zai kai sati biyu." Cike da taikaci yace." Waye ya fad'a miki ana had'a maganin hausa dana bature a tare? shuru nayi kaina a kasa.....Ya cigaba da cewa"Magani kun jiqa shi tsayin sati biyu yana kumfa wari na tashi a cikinsa amma kuna d'irka masa so kuke ku kasheshi."? Nayi saurin kallonsa ina girgiza kaina. Yace."To ko dan gaba ba'a hada maganin hausa dana bature a tare sannan kuma idan kun jiqa maganin hausa to kuyi amfani dashi a lokacin idan ya kwana daya biyu ku zubar dashi domin ya tashi a aiki amma magani tsayin sati biyu a jiqe kuna bashi dole ku kasa gane kansa.
Nace"Kayi hakuri zamu gyara insha Allah.'' Shiru yayi ya sunkuyar kansa 'kasa, na dinga satar kallonsa ina mamakin wannan d'abia tashi bini bini kallon 'kasa sai kace makaho........"Anjima bayan isha'i ki shigo ki kar'bar masa wasu maganin insha Allahu zai samu lafiya." Murya na rawa nace"To mungode ranka ya dade."
Ba tare da yace wani abuba ya rankwafa da niyyar fita daga dakin........Bayansa nabi naga suna sallama da tambaya, har soro na rakashi ina godiya uffan bece min ba har ya fita daga zauran namu.....na koma cikin gidan da sauri na shiga yiwa Tambaya bayani da yayi akan maganin gargajiyar da muka jiqa.
*BINTA UMAR ABBALE*
Kuyi sharingðŸ‘ðŸ»
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALEðŸ’_ *[email protected]*
*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊�*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_
*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
21&22
Sai bayan dana idar da sallar isha'i tukkuna na shedawa Tambaya maganar komawa ta 'bangaransa da aiki. shuru tayi tana nazarin al'amarin tace"Sumayya dole ne mubi umarnin masarauta bamu da za'bi sai abinda suka ce damu saboda haka na umarce ki kije ki kula da Yarima bisa amana ki kyautata masa kamar yanda zaki kyautatawa iyayenki." Nace"Tambaya babu wanda nake ji sai babana ki duba kiga halin da yake ciki gashi kema bakya zama sosai kullum kuna gurin girkin abinci bana so a barshi shi kadai a gidan shiyasa wallahi tunda naji maganar hankalina ya tashi."
"Sumayya duk abinda Allah yayi nufun zartarwa akan mahaifinki to ko muna nan ko bama nan bamu isa mu hana Allah ikonsa ba, saboda haka ki nutsu ki kwantar da hankalin ki cuta ba mutuwa bace insha Allah Allah zai tashi kafad'unsa."
Shuru nayi ina sa'ke-sa'ke a cikin raina.
Tace"Tunda kinyi sallah sai kici abinci ki tafi kada ki 'bata lokaci a samu matsala.
A sanyaye naje na 'Dauko kula ta abincin na had'o da plate na zauna inda na tashi abincin na zuba a plate nayi bisimillah a nutse na fara ci, Tambaya miqewa tayi ta nufi inda mijinta yake kwance, a hankali ta shiga kiran sunansa, bude idonsa yayi ya kalleta a hankali ya mayar da idon ya rufe, tace"Malam kaji maganar da muke tattaunawa ko.'' ? idanunsa ya bude ya kalli gefan da nake zaune ina cin abinci.
A sar'ke yace"Sumayya kibi umarnin masarauta ko bayan babu raina bance ki bijirewa masarauta ba domin baki da wani tushe sai ita iyayenmu da kakannimu duk a k'arkashin masarauta suka rayu a haka duk aka haife mu saboda haka nake umartar ki da cewar kiyi biyayya kamar yanda kika ga munayi a matsayin mu na iyayenki."
Muryata na rawa nace"Baba dan Allah ka daina maganar mutuwa insha Allahu zaka tashi ka cigaba da sabgogin ka cuta ba mutuwa bace." Murmushi yay yace."Sumayya kenan to ina rokon ubangiji Allah ya tashi kafad'una na cigaba da rayuwa a tare daku.'"
murya na rawa nace"ameen baba Allah ya baka lafiya." amsawa sukayi da "ameen" na mike na fita domin wanke hannuna.
Lokacin dana shiga dakin Tambaya na kokarin mikar dashi zaune domin ta d'aura masa alwala taimaka mata nayi mukayi masa alwalar ta gyara shi sosai yanda zaiji dadin sallah ya tayar da iqama a nutse! kallona tayi tace"Kiyi maza ka tafi mana." Sai Naji zuciyata ta karye tunda na taso ban ta'ba zuwa ko'ina na kwana ba kullum ina tare da iyayena
A sanyaye na juya ina goge hawaye da hannuna nace"Na tafi." Itama tambayan cikin alhini tace"Sai da safe." Jin kuka naso ya kufce min yasa nayi gaggawar fita daga dakin, takalmana dake bakin kofar dakin na zura na fita daga gidan.
Haruna da su Isa na samu a falon suna aikace aikace, gaisawa mukayi na nemi kan kujera na zauna ina rarraba idona a katafaran falon nashi daya gaji da had'uwa, ko wace kusurwa hotonshi ne a manne wani da manyan kaya na sarauta wani kuma da 'kananun kaya cikin hotonan nasa babu wanda yayi dariya a ciki fuska a murtuke tamkar wanda akayiwa dole gurin daukar hoton, muryar Haruna ce ta katse min tunanin da nake, na kalleshi inaso ya sake maimaita min abinda yake fad'a, Yace."Sumayya ba zama zakiyi ba zaki hau sama ne ki bubbuga idan ya bude sai ki sheda masa isowarki idan da akwai abinda yake bukata kiyi masa sai kiyi mu dai mun gama aikin mu zamuje mu huta sai ya b'ukace mu.'' Na kalleshi da fadin"Ina ne d'akin nasa."
Wata matattakalar bene ya nuna min da fadin''Kina kaiwa karshen benan za kiga wata kofa mai biyu nan ne d'akinsa sai ki danna wani abu a jikin kofar zai yi magana.
Nayi shuru ina sa'ke-sa'ke mi'kewa nayi na kama hanyar benan, da k'yar nake hawa benan sabida santsin ties d'in ina hawa ina ri'ke sandar benan gabana na fad'uwa! ajiyar zuciya na ajiye bayan na gani a kofar dakin
Sai da na daidaita nutsuwa ta tukkuna na danna abinda zai isar masa da isowata. shuru ba'ayi magana ba, nasa hannu akan abun na latsa da kar'fi! Naji muryarsa yana fad'in "Wanene." "Nice Sumayya.'' Murya a hard'e na fadi maganar. shuru har tsayin mintina goma bai bude ba jikina yayi sanyi kamar nayi tafiya ta sai dai na daure na cigaba da tsayuwa, motsin bude kofar naji nayi saurin ja gefe tare dayin kasa da kaina, koda ya bude kofar ban kalleshi ba nace" Barka da dare ranka ya dade."
"Barka dai shigo ciki." Yafada tare da juyawa cikin dakin. Dago kaina nayi da sauri na mayar dashi qasa sakamakon ganinsa da nayi d'aure da towel gabana ya dinga bugawa kasa shiga dakin nai nayi tsaye a bakin kofar ina tararrabi."
Zama yay gefan bed dinshi yana kallon bakin kofar, "Ke! ki shigo nace dake."! A tsawace ya fad'i maganar, shahada nayi na shiga yace." Kulle kofar." hannu nasa na tura kofar dakin ta rufe, tsayuwa nayi jikin kofar kaina a qasa nace"Ranka ya dade gani nazo." Shareni yayi ya cigaba da murza vasilin a jikinsa, duk da kaina a qasa yake sai da naga cinyoyinsa d'an towel din ya dinga turewa daga jikinsa yana shafa vasilin din, ganin kamar yana so yayi tsirara yasa na juya masa baya.
Yanayin tafiya ta da tashi ba daya bane koda na waiwaya sai naga nayi masa nisa sosai d'an tsayawa nayi ina jiran zuwanshi.....Bangaran shi kuwa tafiya kawai yake amma hankalinsa tuntuni ya tashi sakamakon yanayin tafiyar da takeyi sassan jikinta na motsawa mazaunanta ba 'karamin tayar masa da hankali yayi ba hakan ya sake sanya masa rashin kuzari da karfin jiki ya dinga tafiya tamkar wanda 'kwai ya fashewa a ciki gabad'aya sha'awarshi ta tashi yana so ya samu yarinyar da zata d'ebe masa kewa.
Sai da ya kusa zuwa dab dani sannan na juya na cigaba da tafiya.....Yarima Ali ajiyar zuciya ya sauke ya tsirawa faffad'an qugunta ido wanda yake juyawa cikin zanin kamfalar dake jikinta........ajiyar zuciya ya dinga saukewa yana kokarin danne abinda ke taso masa.
Koda muka shiga gurin namu Tambaya dake bakin rijiya tana wanke kwanuka mikewa tayi da sauri ganina tare dashi yasa hankalinta ya tashi tana tsoro ko wani abu ne ya faru, ganin ta razana yasa nace"Ki kwantar da hankalinki babu abinda ya faru Yarima zai duba jikin babana ne."
Zubewa tayi gabansa tana gaisheshi gami dayi masa godiya. Cikin sanyin murya ya amsa tare da bata umarnin mi'kewa.
Na kalleshi a nutse nace"Ranka ya dade bisimillah ka shigo." Takalmansa ya cire a nutse ya rankwafa domin shiga dakin dake gajeriyar kofa ce shi kuma ya kasance mutum mai tsayi shine dalilin da yasa ya risina domun shiga dakin.
Guri na shiga karkad'ewa wai ko zai zauna, sai naga yaja ya tsaya yana kallon babana dake kwance yana bacci.....Cikin rawar baki nace"Ka ganshi ko wallahi yana jin ji......! hannu ya daga min alamanun baya bukatar maganata, nayi shuru ina kallonsa sai kallon babana yake kafin ya kalleni yace"Ina maganin da kuke bashi."?
Da sauri na dauko na mika masa, ya jima yana duba magungunan kafin ya miko min da fadin"Kada ku sake bashi maganin ku ajeshi zamuje yanzu nasa Haruna ya samo masa wasu insha Allah zasuyi masa."
Da sauri nace"To mungode shima na hausan da muke bashi mu daina."? Kallona yayi da sauri yace."Bayan wannan maganin akwai wanda kuke bashi."? nace."Eh akwai na hausa wanda na kar'bo gurin masu maganin gargajiya."
Tsaki! yaja da fad'in"Jeki dauko min maganin nagani." Na mike da sauri na fita tsakar gida na samu Tambaya ta gama wanke kwanuka tana tsaye jikin bango (garu)ta rungume hannuwanta a kirji.
"Tambaya ina maganin da ki'ka jiqawa babana." Da sauri ta shiga wani daki dake tsakar gidan ta dauko maganin cikin bokitin roba madaidaici karba nayi da sauri na shiga dakin, na mika masa .
"Ajiye ki bud'e nagani." Ajiyewa nayi a kasan guri nayi yanda yace. Ni dashi gabad'aya tsirawa maganin ido mukayi ganin yanda yake wata irin kumfa ga wari na tashi a cikinsa.
Dauke kansa yay rai a b'ace yace."Rufe." Jiki a sanyaye na rufe ina kallonsa, Yace."Wannan maganin kwanansa nawa a jiqe."? a sanyaye nace"Zai kai sati biyu." Cike da taikaci yace." Waye ya fad'a miki ana had'a maganin hausa dana bature a tare? shuru nayi kaina a kasa.....Ya cigaba da cewa"Magani kun jiqa shi tsayin sati biyu yana kumfa wari na tashi a cikinsa amma kuna d'irka masa so kuke ku kasheshi."? Nayi saurin kallonsa ina girgiza kaina. Yace."To ko dan gaba ba'a hada maganin hausa dana bature a tare sannan kuma idan kun jiqa maganin hausa to kuyi amfani dashi a lokacin idan ya kwana daya biyu ku zubar dashi domin ya tashi a aiki amma magani tsayin sati biyu a jiqe kuna bashi dole ku kasa gane kansa.
Nace"Kayi hakuri zamu gyara insha Allah.'' Shiru yayi ya sunkuyar kansa 'kasa, na dinga satar kallonsa ina mamakin wannan d'abia tashi bini bini kallon 'kasa sai kace makaho........"Anjima bayan isha'i ki shigo ki kar'bar masa wasu maganin insha Allahu zai samu lafiya." Murya na rawa nace"To mungode ranka ya dade."
Ba tare da yace wani abuba ya rankwafa da niyyar fita daga dakin........Bayansa nabi naga suna sallama da tambaya, har soro na rakashi ina godiya uffan bece min ba har ya fita daga zauran namu.....na koma cikin gidan da sauri na shiga yiwa Tambaya bayani da yayi akan maganin gargajiyar da muka jiqa.
*BINTA UMAR ABBALE*
Kuyi sharingðŸ‘ðŸ»
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALEðŸ’_ *[email protected]*
*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊�*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_
*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
21&22
Sai bayan dana idar da sallar isha'i tukkuna na shedawa Tambaya maganar komawa ta 'bangaransa da aiki. shuru tayi tana nazarin al'amarin tace"Sumayya dole ne mubi umarnin masarauta bamu da za'bi sai abinda suka ce damu saboda haka na umarce ki kije ki kula da Yarima bisa amana ki kyautata masa kamar yanda zaki kyautatawa iyayenki." Nace"Tambaya babu wanda nake ji sai babana ki duba kiga halin da yake ciki gashi kema bakya zama sosai kullum kuna gurin girkin abinci bana so a barshi shi kadai a gidan shiyasa wallahi tunda naji maganar hankalina ya tashi."
"Sumayya duk abinda Allah yayi nufun zartarwa akan mahaifinki to ko muna nan ko bama nan bamu isa mu hana Allah ikonsa ba, saboda haka ki nutsu ki kwantar da hankalin ki cuta ba mutuwa bace insha Allah Allah zai tashi kafad'unsa."
Shuru nayi ina sa'ke-sa'ke a cikin raina.
Tace"Tunda kinyi sallah sai kici abinci ki tafi kada ki 'bata lokaci a samu matsala.
A sanyaye naje na 'Dauko kula ta abincin na had'o da plate na zauna inda na tashi abincin na zuba a plate nayi bisimillah a nutse na fara ci, Tambaya miqewa tayi ta nufi inda mijinta yake kwance, a hankali ta shiga kiran sunansa, bude idonsa yayi ya kalleta a hankali ya mayar da idon ya rufe, tace"Malam kaji maganar da muke tattaunawa ko.'' ? idanunsa ya bude ya kalli gefan da nake zaune ina cin abinci.
A sar'ke yace"Sumayya kibi umarnin masarauta ko bayan babu raina bance ki bijirewa masarauta ba domin baki da wani tushe sai ita iyayenmu da kakannimu duk a k'arkashin masarauta suka rayu a haka duk aka haife mu saboda haka nake umartar ki da cewar kiyi biyayya kamar yanda kika ga munayi a matsayin mu na iyayenki."
Muryata na rawa nace"Baba dan Allah ka daina maganar mutuwa insha Allahu zaka tashi ka cigaba da sabgogin ka cuta ba mutuwa bace." Murmushi yay yace."Sumayya kenan to ina rokon ubangiji Allah ya tashi kafad'una na cigaba da rayuwa a tare daku.'"
murya na rawa nace"ameen baba Allah ya baka lafiya." amsawa sukayi da "ameen" na mike na fita domin wanke hannuna.
Lokacin dana shiga dakin Tambaya na kokarin mikar dashi zaune domin ta d'aura masa alwala taimaka mata nayi mukayi masa alwalar ta gyara shi sosai yanda zaiji dadin sallah ya tayar da iqama a nutse! kallona tayi tace"Kiyi maza ka tafi mana." Sai Naji zuciyata ta karye tunda na taso ban ta'ba zuwa ko'ina na kwana ba kullum ina tare da iyayena
A sanyaye na juya ina goge hawaye da hannuna nace"Na tafi." Itama tambayan cikin alhini tace"Sai da safe." Jin kuka naso ya kufce min yasa nayi gaggawar fita daga dakin, takalmana dake bakin kofar dakin na zura na fita daga gidan.
Haruna da su Isa na samu a falon suna aikace aikace, gaisawa mukayi na nemi kan kujera na zauna ina rarraba idona a katafaran falon nashi daya gaji da had'uwa, ko wace kusurwa hotonshi ne a manne wani da manyan kaya na sarauta wani kuma da 'kananun kaya cikin hotonan nasa babu wanda yayi dariya a ciki fuska a murtuke tamkar wanda akayiwa dole gurin daukar hoton, muryar Haruna ce ta katse min tunanin da nake, na kalleshi inaso ya sake maimaita min abinda yake fad'a, Yace."Sumayya ba zama zakiyi ba zaki hau sama ne ki bubbuga idan ya bude sai ki sheda masa isowarki idan da akwai abinda yake bukata kiyi masa sai kiyi mu dai mun gama aikin mu zamuje mu huta sai ya b'ukace mu.'' Na kalleshi da fadin"Ina ne d'akin nasa."
Wata matattakalar bene ya nuna min da fadin''Kina kaiwa karshen benan za kiga wata kofa mai biyu nan ne d'akinsa sai ki danna wani abu a jikin kofar zai yi magana.
Nayi shuru ina sa'ke-sa'ke mi'kewa nayi na kama hanyar benan, da k'yar nake hawa benan sabida santsin ties d'in ina hawa ina ri'ke sandar benan gabana na fad'uwa! ajiyar zuciya na ajiye bayan na gani a kofar dakin
Sai da na daidaita nutsuwa ta tukkuna na danna abinda zai isar masa da isowata. shuru ba'ayi magana ba, nasa hannu akan abun na latsa da kar'fi! Naji muryarsa yana fad'in "Wanene." "Nice Sumayya.'' Murya a hard'e na fadi maganar. shuru har tsayin mintina goma bai bude ba jikina yayi sanyi kamar nayi tafiya ta sai dai na daure na cigaba da tsayuwa, motsin bude kofar naji nayi saurin ja gefe tare dayin kasa da kaina, koda ya bude kofar ban kalleshi ba nace" Barka da dare ranka ya dade."
"Barka dai shigo ciki." Yafada tare da juyawa cikin dakin. Dago kaina nayi da sauri na mayar dashi qasa sakamakon ganinsa da nayi d'aure da towel gabana ya dinga bugawa kasa shiga dakin nai nayi tsaye a bakin kofar ina tararrabi."
Zama yay gefan bed dinshi yana kallon bakin kofar, "Ke! ki shigo nace dake."! A tsawace ya fad'i maganar, shahada nayi na shiga yace." Kulle kofar." hannu nasa na tura kofar dakin ta rufe, tsayuwa nayi jikin kofar kaina a qasa nace"Ranka ya dade gani nazo." Shareni yayi ya cigaba da murza vasilin a jikinsa, duk da kaina a qasa yake sai da naga cinyoyinsa d'an towel din ya dinga turewa daga jikinsa yana shafa vasilin din, ganin kamar yana so yayi tsirara yasa na juya masa baya.