Sashe 55
Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Juyawa yayi ya kalli jama'ar da sukayi dafifi a gurin, yace."Kowa ya tafi.' da sauri suka watse! ya kalli Tambaya jiki a mace yace."Zamuje da ita asibiti domin taimaka mata." Tana kuka tace"Allah ya saka maka da alkairi." Hannu yasa yana kokarin daukarta, Lawi yace."ranka ya dade da kanka." Kansa kawai ya girgiza masa shi yanzu meye ba zaiyi wa yarinyar nan ba watakila ma gurin bashi kariya ta had'u da tsautsayi koma dai menene idan ta farfad'o tilas tayi masa bayani.
Mikewa yayi da ita a hannunsa, Mika'il da security dinsa sukayi gaba da sauri, Tambaya da Lawi suka rufa musu baya.
Bayan mota ya kwantar da ita, ya dan gyara ta domin ya samu gurin zama ya kallesu sun bashi tausayi mutuka ciki kokarin kwantar musu da hankali yace."Insha Allah da kafafunta zata dawo ku daina damuwa kuyi mata addua." Lawi ya sauke ajiyar zuciya da fadin"Ubangiji Allah ya tashi kafad'arta." ameen yace tare da bawa Mika'il umarnin tafiya, sai da motar ta 'bace wa ganinsu sannan suka nufi sashen su cikin halin damuwa gami da rokon Allah sassauci!
Tun mota yake bata taimakon gaggawa dan bakinsa da nata ya had'a ya dinga hura mata iskar bakinsa gabadaya jikinsa ya baci da jinin dake fita ta goshinta, hannusa guda yasa ya danne inda jinin ke zuba ya cigaba da bata taimako irin nasu, cikin ikon Allah kuwa suna daf da shiga asibitin ta farfad'o Allah ya godewa ya rike hannunta tsam a cikin nasa.
Cikin kwarewa da sanin makamar aiki ya tsayar da jinin dake zuba daga goshinta, duk wani taimako da yasan tana bukata sai da yayi mata ya samu nutsuwar zuciyarsa, zama yayi gefanta tare da rike hannunta guda, fuskarta ya tsirawa ido tana ta bacci dan sai da yayi mata allura kafin ya fara aikinsa.
Ajiyar zuciya ya sauke ya tsirawa ties ido babban burinsa yarinyar ta samu nutsuwa ta sheda masa abinda ya faru da ita, tabbas yana zargin wasu daga cikin ma'kiyansa ne suka soma farautar ta, shi kam ya rasa yanda zaiyi da rayuwarsa da makiya.
Agogon hannunsa ya duba karfe daya da rabi na dare, ashe ya jima a zaune yana tunani, hannunsa dake cikin nata yayi nufin cirewa ta rik'e! sai yayi saurin kallo ta yana kiran sunanta
Jin muryarsa ta doki kunnena yasa nayi gaggawar bude idona! idanuwanmu ne suka had'u, kawai hawaye ya kwace min na rintse hannunsa dake cikin nawa ina kallonsa hawaye na ambaliya a fuskata,
Jikina ya matso sosai jikinsa har rawa yake yace."Sumayya sannu kinji ko ki fada min inda ke miki ciwo."
Hannuna na dora saman goshina naji shi a nannad'e! cikin sanyi jiki ya dauke hannuna dake gurin yace."Zai daina ciwo insha Allah! kiyi hakuri kinji ko." Kaina na daga ina kallonsa tausayinsa na ratsa zuciyata.
Yace."Ko zaki tashi zaune."? kaina na girgiza alamu A'a. Dakin yayi shuru na minti biyar kafin yace." Zaki iya yi min bayanin abinda ya same ki."?
Kai na d'aga alamun "E" ya sake matsowa kusa dani murya a kasa yace." Ina sauraranki.
Muryata na rawa nace"Muddibo ne." da sauri ya kalleni nasan mamaki yake jin na ambaci sunan Muddibo.
Yace."Muddibo ne sumayya me yayi miki." ? nasa hannu nagoge hawayen dake zuba, nace"Aiki ya sani nace ba zanyi ba shine ya kwada min mari hakan be isheshi ba ya dauki dutsen wuta ya buga min akaina kashe ni yayi niyyar yayi kamar yanda ya fada zuwan mutane gurin yasa ya gudu.
Gani nayi ya sunkuyar da kansa fuskarsa kamar ta nuna alamun rashin yarda
Nace"Dama nasan ba zaka yarda ba." ya kalleni babu walwala a fuskarsa yace."Sumayya dole nayi kokwanto akan hakan shin wane irin aiki ne ya sakiyi masa kikai masa gardama."'?
"Magani ya bani yace." Lallai na zuba maka a lemo." Kallona yayi yana mamakin maganata! nace"Ni kuma na kwance maganin na watsa masa a fuskarsa."
Cike da mamaki yake kallona kafin yace." Sumayya me yasa kike da tsaurin ido ne? saboda kawai Muddibo ya baki magani kisa min a lemo sai ki watsa masa a fuska sa'anki ne ko kuwa ? Muddibo zai iya daukar mummunan mataki akanki."
Raina a bace nace"Akan na kashe wani gwara ni a kasheni dama aini baiwa ce kowa yana iya amfani dani ta kowace hanya amma nayi rantsuwa ba zan taba bari amanar Allah ta cini ba."!
Girgiza kai yake yana kallona yace."Kwarai ina yaba miki! bisa namijin kokarin da kike gurin ganin kin kare raina da lafiyata, amma me yasa baki bi umarnin muddibo ba, me yasa baki kar'bi maganin ba idan yaso ke kuma sai ki san yanda kikayi kika zubar dashi a wani gurin, na tabbata tsaurin idon da kikayi masa ne yasa yayi miki wannan mumman dukan, Sumayya inaso ki san da cewa ni kad'ai ne zaki iya yiwa zafin kai! na rabu dake amma baki isa kiyiwa wanda yake sama dake tsaurin ido ya kyaleki ba."
Shuru nayi ina nazarin maganarsa, eh kamar yanda yace dana sani na yaudareshi na karbi maganin daga bisani sai na zubar kawai. wani lokacin ne idan zuciyata ta dauki zafi ni kaina bana iya tank'warata."
"Kin tabbata cewa Muddibo ne ya aikata miki wannan mummunan abun."? Kaina na daga ina goge hawaye, Yace." Lallai za'a ramawa kura aniyarta dan ba zan k'yale Muddibo ba sai naci mutuncinsa wallahi tallahi sai yayi daya sanin ta'ba lafiyarki, ni akan wannan zan dauki mataki a kansa daga baya kuma sai ya shedawa Police Maganin me ya baki kisa min a lemo."
Dad'i naji a cikin zuciyata jin cewa zai dauki mataki akansa, nace"Daka dauki mataki akan yunkurin kashe ka da yake ina ganin shi yafi amfani tunda ni ba'a bakin komai nake ba a cikin masarauta kamar yanda ka gama fada yanzu."
Girgiza kansa yayi ya rintse hannuna da nashi yace."Sumayya a cikin masarauta ba'a bakin komai kike ba kamar yanda na fada miki yanzu amma sanadiyar faruwar wannan al'amari masarauta zata san kina da muhimanci a tare da ita."
Lumshe idona nayi kawai na tsinci kaina da d'amke hannunsa dake cikin nawa, gabad'aya muka had'e yatsun hannunmu guri guda tamkar masu d'aukarwar junanmu al'kawari.
' Dakin ne yayi shuru na tsayin lokaci kafin naji ya kira sunana, idona na bude ina kallonsa, yace."Kiyi bacci kada kisa damuwar komai a cikin ranki kinji ko." Lumshe ido nayi a hankali nace"Dan Allah kayi hakuri kabar maganar kada kayiwa Muddibo wani abu ni dama babban burina ka gane gaskiya ka amince da dukkanin gaskiyata."
Ido ya zuba min kafin ya shiga girgiza kansa yace."Sumayya ba zan ta'ba yafewa kaina ba mutukar na bar jininki ya zuba a banza ni d'an halak ne kuma nasan abinda ya dace ."
Shuru nayi ina tunanin abinda zai faru a gaba bana so garin d'aukar fansa wata masifar ta faru a tsakaninsu nafiso kawai ya bar maganar kada yace zai dauki mataki kan abinda akayi min.
Hannuna ya saki ya mike kallo na bishi dashi, ya nufi toilet, ajiyar zuciya na sauke a hankali na rintse idona ina addua cikin zuciyata.
Motsin fitowarsa tasa na bude idona ina kallonsa naga ya shimfida dadduma, da alama sallah zaiyi idanuwa na mayar na rufe ina tunanin iyayena yanzu ko wane irin hali suke ciki? nasan dai duk inda suke suna cikin tashin hankali da damuwa mai tsanani! hawaye suka zubo min a kumatu hannu nasa da sauri na goge ina kokarin danne kukan dake kokarin kufce min.
b'angaran Magajin Sarki kuwa nafila yayi raka biyu ya daga hannu sama ya roki Allah sosai akan abubuwan dake faruwa da rayuwarsa da makusantan sa yanzu abun ya wuce kansa har yazo kan masu kula dashi, tunda an kasa samun galaba a kansa to bari a sabauta hadiman sa, gaskiya magana dole ya dauki mataki akan al'amarin dan yana ji yana gani jinin yarinyar dake tsaye a kan rayuwarsa ya tafi a banza ba dole ya nunawa Muddibo kuskuransa, ya jima hannu a sama yana rokon Allah kafin ya shafa adduar a fuskarsa ya mike a nutse ya nufo gadon da nake kwance.
Cikin bacci na jishi a jikina, nayi saurin bude idona ina kallonsa yana kokarin kwanciya kokarin mikewa nayi yayi saurin rike hannuna! Girgiza min kai yayi a hankali yace."Ki kwanta mana." Murya na rawa nace"To ka tashi daga kusa dani.'' a hankali yace."Dan gurin dana kwanta bai isa ya tsare miki gurinki ba kiyi hakuri ki kwanta babu abinda zai faru sai alkairi."
A sanyaye na dinga kallonsa ina mamakin karfin halinsa Tamkar wata matar auransa haka yake Mu'amula dani.
"Gaskiya ni bazan kwanta gado daya dakai ba saboda haka bari kawai na sauka kasa.'' Yunkurin sauka nake ya rike kafaduna! cikin kulawa yace." Saboda na kula da motsin ki yasa zan kwanta kusa dake amma tunda bakya so shikkenan bari na sauka." kallo na bishi dashi lokacin daya sauka daga gadon ya koma kan doguwar kujera ya kwanta, tausayi ya bani ganin yanda yayi sanyi yana min magana cikin kwantar da murya na amince da cewa abinda ya faru ya girgizashi mutuka yanzu kuma na gane cewa ina da muhimanci a rayuwarsa tunda gashinan a zahiri ya nuna tashin hankalinsa..........Na jima ina tunane tunane kafin bacci ya d'aukeni! bacci mai cike da munanan mafarkai marasa dadi da ma'ana.
Kiran sunana da ake yasa na bude idona da sauri ina kallonsa yana tsaye a kaina, hannu na dora saman kaina ina jin wani irin ciwo a gurin, a nutse yasa hannu ya cire hannuna, "Sannu." kaina na d'aga ya cigaba da cewa"Kinga gurin yayi fushi ko."!? kaina na girgiza a hankali na fara kokarin mikewa ya kama hannuna, kallonsa nayi ya girgiza min kai da fadin"Kada kice komai taimaka miki zanyi kiyi alwala ko." Shuru nai masa, ya fara kokarin dora hannuna a kafadarsa, yana so ya rike kuguna. da sauri nace"Dan Allah ka barni zan iya komai da kaina. Bai saurare ni ba, ya ratsa hannusa a k'uguna, ya sani a jikinsa sosai muka nufi toilet, kallona yayi yace."Babu inda ke miki ciwo ko."? ganin yanda ya damu yasa nace"Eh babu kaina ne ke ciwo." Cikin rarrashi yace."Bari kiyi sallah sai muje gida kiyi break kisha magani insha Allahu zaki samu sauki."
Mikewa yayi da ita a hannunsa, Mika'il da security dinsa sukayi gaba da sauri, Tambaya da Lawi suka rufa musu baya.
Bayan mota ya kwantar da ita, ya dan gyara ta domin ya samu gurin zama ya kallesu sun bashi tausayi mutuka ciki kokarin kwantar musu da hankali yace."Insha Allah da kafafunta zata dawo ku daina damuwa kuyi mata addua." Lawi ya sauke ajiyar zuciya da fadin"Ubangiji Allah ya tashi kafad'arta." ameen yace tare da bawa Mika'il umarnin tafiya, sai da motar ta 'bace wa ganinsu sannan suka nufi sashen su cikin halin damuwa gami da rokon Allah sassauci!
Tun mota yake bata taimakon gaggawa dan bakinsa da nata ya had'a ya dinga hura mata iskar bakinsa gabadaya jikinsa ya baci da jinin dake fita ta goshinta, hannusa guda yasa ya danne inda jinin ke zuba ya cigaba da bata taimako irin nasu, cikin ikon Allah kuwa suna daf da shiga asibitin ta farfad'o Allah ya godewa ya rike hannunta tsam a cikin nasa.
Cikin kwarewa da sanin makamar aiki ya tsayar da jinin dake zuba daga goshinta, duk wani taimako da yasan tana bukata sai da yayi mata ya samu nutsuwar zuciyarsa, zama yayi gefanta tare da rike hannunta guda, fuskarta ya tsirawa ido tana ta bacci dan sai da yayi mata allura kafin ya fara aikinsa.
Ajiyar zuciya ya sauke ya tsirawa ties ido babban burinsa yarinyar ta samu nutsuwa ta sheda masa abinda ya faru da ita, tabbas yana zargin wasu daga cikin ma'kiyansa ne suka soma farautar ta, shi kam ya rasa yanda zaiyi da rayuwarsa da makiya.
Agogon hannunsa ya duba karfe daya da rabi na dare, ashe ya jima a zaune yana tunani, hannunsa dake cikin nata yayi nufin cirewa ta rik'e! sai yayi saurin kallo ta yana kiran sunanta
Jin muryarsa ta doki kunnena yasa nayi gaggawar bude idona! idanuwanmu ne suka had'u, kawai hawaye ya kwace min na rintse hannunsa dake cikin nawa ina kallonsa hawaye na ambaliya a fuskata,
Jikina ya matso sosai jikinsa har rawa yake yace."Sumayya sannu kinji ko ki fada min inda ke miki ciwo."
Hannuna na dora saman goshina naji shi a nannad'e! cikin sanyi jiki ya dauke hannuna dake gurin yace."Zai daina ciwo insha Allah! kiyi hakuri kinji ko." Kaina na daga ina kallonsa tausayinsa na ratsa zuciyata.
Yace."Ko zaki tashi zaune."? kaina na girgiza alamu A'a. Dakin yayi shuru na minti biyar kafin yace." Zaki iya yi min bayanin abinda ya same ki."?
Kai na d'aga alamun "E" ya sake matsowa kusa dani murya a kasa yace." Ina sauraranki.
Muryata na rawa nace"Muddibo ne." da sauri ya kalleni nasan mamaki yake jin na ambaci sunan Muddibo.
Yace."Muddibo ne sumayya me yayi miki." ? nasa hannu nagoge hawayen dake zuba, nace"Aiki ya sani nace ba zanyi ba shine ya kwada min mari hakan be isheshi ba ya dauki dutsen wuta ya buga min akaina kashe ni yayi niyyar yayi kamar yanda ya fada zuwan mutane gurin yasa ya gudu.
Gani nayi ya sunkuyar da kansa fuskarsa kamar ta nuna alamun rashin yarda
Nace"Dama nasan ba zaka yarda ba." ya kalleni babu walwala a fuskarsa yace."Sumayya dole nayi kokwanto akan hakan shin wane irin aiki ne ya sakiyi masa kikai masa gardama."'?
"Magani ya bani yace." Lallai na zuba maka a lemo." Kallona yayi yana mamakin maganata! nace"Ni kuma na kwance maganin na watsa masa a fuskarsa."
Cike da mamaki yake kallona kafin yace." Sumayya me yasa kike da tsaurin ido ne? saboda kawai Muddibo ya baki magani kisa min a lemo sai ki watsa masa a fuska sa'anki ne ko kuwa ? Muddibo zai iya daukar mummunan mataki akanki."
Raina a bace nace"Akan na kashe wani gwara ni a kasheni dama aini baiwa ce kowa yana iya amfani dani ta kowace hanya amma nayi rantsuwa ba zan taba bari amanar Allah ta cini ba."!
Girgiza kai yake yana kallona yace."Kwarai ina yaba miki! bisa namijin kokarin da kike gurin ganin kin kare raina da lafiyata, amma me yasa baki bi umarnin muddibo ba, me yasa baki kar'bi maganin ba idan yaso ke kuma sai ki san yanda kikayi kika zubar dashi a wani gurin, na tabbata tsaurin idon da kikayi masa ne yasa yayi miki wannan mumman dukan, Sumayya inaso ki san da cewa ni kad'ai ne zaki iya yiwa zafin kai! na rabu dake amma baki isa kiyiwa wanda yake sama dake tsaurin ido ya kyaleki ba."
Shuru nayi ina nazarin maganarsa, eh kamar yanda yace dana sani na yaudareshi na karbi maganin daga bisani sai na zubar kawai. wani lokacin ne idan zuciyata ta dauki zafi ni kaina bana iya tank'warata."
"Kin tabbata cewa Muddibo ne ya aikata miki wannan mummunan abun."? Kaina na daga ina goge hawaye, Yace." Lallai za'a ramawa kura aniyarta dan ba zan k'yale Muddibo ba sai naci mutuncinsa wallahi tallahi sai yayi daya sanin ta'ba lafiyarki, ni akan wannan zan dauki mataki a kansa daga baya kuma sai ya shedawa Police Maganin me ya baki kisa min a lemo."
Dad'i naji a cikin zuciyata jin cewa zai dauki mataki akansa, nace"Daka dauki mataki akan yunkurin kashe ka da yake ina ganin shi yafi amfani tunda ni ba'a bakin komai nake ba a cikin masarauta kamar yanda ka gama fada yanzu."
Girgiza kansa yayi ya rintse hannuna da nashi yace."Sumayya a cikin masarauta ba'a bakin komai kike ba kamar yanda na fada miki yanzu amma sanadiyar faruwar wannan al'amari masarauta zata san kina da muhimanci a tare da ita."
Lumshe idona nayi kawai na tsinci kaina da d'amke hannunsa dake cikin nawa, gabad'aya muka had'e yatsun hannunmu guri guda tamkar masu d'aukarwar junanmu al'kawari.
' Dakin ne yayi shuru na tsayin lokaci kafin naji ya kira sunana, idona na bude ina kallonsa, yace."Kiyi bacci kada kisa damuwar komai a cikin ranki kinji ko." Lumshe ido nayi a hankali nace"Dan Allah kayi hakuri kabar maganar kada kayiwa Muddibo wani abu ni dama babban burina ka gane gaskiya ka amince da dukkanin gaskiyata."
Ido ya zuba min kafin ya shiga girgiza kansa yace."Sumayya ba zan ta'ba yafewa kaina ba mutukar na bar jininki ya zuba a banza ni d'an halak ne kuma nasan abinda ya dace ."
Shuru nayi ina tunanin abinda zai faru a gaba bana so garin d'aukar fansa wata masifar ta faru a tsakaninsu nafiso kawai ya bar maganar kada yace zai dauki mataki kan abinda akayi min.
Hannuna ya saki ya mike kallo na bishi dashi, ya nufi toilet, ajiyar zuciya na sauke a hankali na rintse idona ina addua cikin zuciyata.
Motsin fitowarsa tasa na bude idona ina kallonsa naga ya shimfida dadduma, da alama sallah zaiyi idanuwa na mayar na rufe ina tunanin iyayena yanzu ko wane irin hali suke ciki? nasan dai duk inda suke suna cikin tashin hankali da damuwa mai tsanani! hawaye suka zubo min a kumatu hannu nasa da sauri na goge ina kokarin danne kukan dake kokarin kufce min.
b'angaran Magajin Sarki kuwa nafila yayi raka biyu ya daga hannu sama ya roki Allah sosai akan abubuwan dake faruwa da rayuwarsa da makusantan sa yanzu abun ya wuce kansa har yazo kan masu kula dashi, tunda an kasa samun galaba a kansa to bari a sabauta hadiman sa, gaskiya magana dole ya dauki mataki akan al'amarin dan yana ji yana gani jinin yarinyar dake tsaye a kan rayuwarsa ya tafi a banza ba dole ya nunawa Muddibo kuskuransa, ya jima hannu a sama yana rokon Allah kafin ya shafa adduar a fuskarsa ya mike a nutse ya nufo gadon da nake kwance.
Cikin bacci na jishi a jikina, nayi saurin bude idona ina kallonsa yana kokarin kwanciya kokarin mikewa nayi yayi saurin rike hannuna! Girgiza min kai yayi a hankali yace."Ki kwanta mana." Murya na rawa nace"To ka tashi daga kusa dani.'' a hankali yace."Dan gurin dana kwanta bai isa ya tsare miki gurinki ba kiyi hakuri ki kwanta babu abinda zai faru sai alkairi."
A sanyaye na dinga kallonsa ina mamakin karfin halinsa Tamkar wata matar auransa haka yake Mu'amula dani.
"Gaskiya ni bazan kwanta gado daya dakai ba saboda haka bari kawai na sauka kasa.'' Yunkurin sauka nake ya rike kafaduna! cikin kulawa yace." Saboda na kula da motsin ki yasa zan kwanta kusa dake amma tunda bakya so shikkenan bari na sauka." kallo na bishi dashi lokacin daya sauka daga gadon ya koma kan doguwar kujera ya kwanta, tausayi ya bani ganin yanda yayi sanyi yana min magana cikin kwantar da murya na amince da cewa abinda ya faru ya girgizashi mutuka yanzu kuma na gane cewa ina da muhimanci a rayuwarsa tunda gashinan a zahiri ya nuna tashin hankalinsa..........Na jima ina tunane tunane kafin bacci ya d'aukeni! bacci mai cike da munanan mafarkai marasa dadi da ma'ana.
Kiran sunana da ake yasa na bude idona da sauri ina kallonsa yana tsaye a kaina, hannu na dora saman kaina ina jin wani irin ciwo a gurin, a nutse yasa hannu ya cire hannuna, "Sannu." kaina na d'aga ya cigaba da cewa"Kinga gurin yayi fushi ko."!? kaina na girgiza a hankali na fara kokarin mikewa ya kama hannuna, kallonsa nayi ya girgiza min kai da fadin"Kada kice komai taimaka miki zanyi kiyi alwala ko." Shuru nai masa, ya fara kokarin dora hannuna a kafadarsa, yana so ya rike kuguna. da sauri nace"Dan Allah ka barni zan iya komai da kaina. Bai saurare ni ba, ya ratsa hannusa a k'uguna, ya sani a jikinsa sosai muka nufi toilet, kallona yayi yace."Babu inda ke miki ciwo ko."? ganin yanda ya damu yasa nace"Eh babu kaina ne ke ciwo." Cikin rarrashi yace."Bari kiyi sallah sai muje gida kiyi break kisha magani insha Allahu zaki samu sauki."