Sashe 42
Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haruna yace." Ba kuka zakiyi ba Sumayya addua ya kamata kiyi." Nasa hannu na goge fuskata "Haruna ya mukaji da hakurin rashin Isa."! Sunkuyar da kansa yayi murya na rawa yace." Hakuri da godiya Isa ya rasu yayi shahada muna rokon Allah ya gafarta masa." A sanyaye na amsa da "ameeen ya rabbi dan Allah kuyi hakuri da faruwar wannan al'amari Haruna kunsan ba zan ta'ba cutar daku ba, wallahi dana san akwai guba acikin doyar nan ba zan kawo ku muku ba kai kanka kasan yanda mutanan gidan nan ke dauki ba dadi akan Yarima burinsu suga bayansa Allah bai nufeshi da cin doyar ba sai ku gashi sunyi nasara sun kashe wanda beji ba be gani ba amma babu komai zasuje su tarar da Ubangijinsu."
Hamza yace.Hakane maganarki Sumayya mu bamu ga laifinki ba wallahi saboda tuntuni mun riga mun san halinki ba zaki cutar damu ba sabida haka ki kwantar da hankalinki duk wanda kikaga ya mutu to dama can kwanansa ya kare Allah yasa ta wannan sanadin Isa zai rasa rayuwarsa muna rokon Allah ya kar'bi shahadarsa.''
Jiki a sanyaye na amsa da ameen ya rabbi ni zan shiga gurin Yarima." Suka ce to sai kin fito."
Yana tsaka da saukowa daga benan shi na shiga, sai na tsaya har ya karasa saukowa, kauda 'bacin raina nayi na gaishe shi. a dakile ya amsa min. nace"Me zakace dangane da abinda ya faru jiya."? Harara ya watsa mun yace." 'Yar jarida ce ke da zaki titsiye ni da tambaya."?
A dake nace"Dole na titsiye ka da tambaya saboda duk abinda 'yan uwanka keyi maka baka ta'ba yarda gashi sanadiyar cin doyar da aka zuba maka guba a ciki wani yaci ya mutu ina fatan yanzu ka gazgata maganata."
"Kinga Sumayya ba wannan ne a gabana ba wanda ya mutu dama can kwanansa ya 'kare mai yasa su sauran da suka ci doyar basu mutu ba, bana son zargi akan abinda mutum baida tabbas a kai nayi binkice na gane ba guba ce ta janyo faruwar al'amarin ba man da yarinyar tayi suyar doyar dashi shine ya gur'bata saboda haka kada na sake jin kinyi wata magana akan wannan al'amarin idan na sake jin kin sako wani nawa a ciki sai ranki ya 'baci!
Kallon shashasha nayi masa nace"Ai dama ba zaka ta'ba yarda ba sai ranar da suka kai ka 'kasa sannan zaka yarda da abinda ake fada maka! kai me 'yan uwa kullum baka so ace ga abunda sukayi maka su kuma kullum cikin shirya maka mugun abu suke ka'ki ka gane ka dauki son duniya ka d'ora musu idan sun kashe ka iyayenka su sukayi asara su kuwa ranar zasuyi kwanan farin ciki bukatarsu ta biya a kanka."
Har na 'kare maganata idanunsa na tsaye a kaina, yace.''Idan sun kashe ni ina ruwanki."? shuru nayi ina kallonsa ya cigaba da cewa 'yan uwana ne ba naki ba ko Wu'ka suka dauko suna yankar namar jikina idone naki kullum ina fad'a miki cewa ki fitar da kanki akan abinda be shafeki ba kin'ki kije kiyi tayi yanda suke farautata kema ba zasu barki ba." Yana gama maganarsa yazo ya wuce ta gabana fita yayi daga falon, da sauri nabi bayansa na sameshi tsaye shida hadimansa suna magana nan na gane gurin jana'izar Isa zasu tafi! a sanyaye na nufi gurinmu ina share hawaye shikkenan Isa ya mutu mutumin kirki sarkin fara'a da barkwanci Isa bashi da abokin fada kullum zaka sameshi da carbi a hannunsa, duk wanda yasan Isa dole ne ya fad'i halinsa nagari.
Koda na koma gurinmu shuru na same shi Tambaya bata nan shima babana baya nan jikina ya bani dukkaninsu sun nufi gurin jana'izar Isa, juyawa nayi nima da niyyar naje can inda ake jana'izar sai kuma nayi wani tunani gurin nasan akwai dandazon mutane ina iya zuwa wata hatsaniyar ta tashi, can kuryar daki na shiga na kwanta a shimfidata rufin dakin na tsirawa ido ina tunanin rayuwa hakika da ina da inda yafi nan da tuni na gudu dan masifar ta isa haka! tunani nake akan maganarmu dashi ta dazu na yarda da maganarsa da yake cewa nima ba zasu barni ba saboda yanda nake saka ido sosai akansa da dukkanin abinda suke aikatawa, ni kaina na rasa me yasa nake damuwa dashi da lafiyarsa sam! bana kaunar abinda zai cutar dashi ko ya ta'ba lafiyarsa inda shi kuma kullum yake nuna min na tsaya a matsayina babu ruwana da 'yan uwansa babu shakka da zan iya dauke idona daga kansa da abinda suke masa to dana zauna lafiya, amma ba zan iya ba saboda ina tsananin tausayawa mahaifiyarsa da mahaifinsa da suka qallafa ransu a kansa, hawaye masu dumi ne suka zubo a kumatuna nasa hannu na goge wasu na sake zubowa hakika ina cikin tsaka mai wuya ina rokon Allah ya kawo mana mafita dani dashi da dukkanin wanda yake da damuwa a cikin zuciyarsa.............Haka na yini a kwance lokacin sallah ne kawai yake tayar dani, Tambaya bata shigo gidan ba sai dab da magariba ta shigo kai tsaye kicin ta nufa ta ajiye kayan abincin hannunta, tsakar gidan na fito muka hadu tace"Ashe kina ciki dama."? kaina na daga nace "Tun dazu dana shigo na tarar bakwa nan bacci ya dauke ni." Tace."Ayya ai bayan futar ki can gurun Iyayen Isa naje akayi jana'iza dani la'asar nayi kuma na nufi gurin aikin abinci shiyasa ban shigo da wuri ba." Nace"Sannu da aiki nima nayi niyyar zuwa sai na fasa saboda gudun abinda ka iya zuwa ya dawo.''
Tace."Ai gwara da baki je ba dan ni kaina zaman hakuri nayi a gurin Lami da sauran mutane sun had'u sai gulma sukeyi suna zaginki dauke kaina kurrum nayi na rabu dasu sukayi su gama." Girgiza kaina nayi cikin 'kunar zuciya nace"Tambaya kada ki damu Allah yana tare da masu gaskiya kedai ki tsananta addua a gurin Allah ya bayyana gaskiyar lamari." Tace!"Addua kullum cikin yin ta nake Insha Allahu Allah sai ya kare ki daga sharrin masu shari.'' Ameen nace na dauki buta domin daura alwalar sallar magariba....
*Na kudi ne*
Kada ki karanta min littafi baki biya ba keda kika futar da book din keda Allah idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal gruop#300 account.. 0542382124...Binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
77
Sosai ya rike 'kuguna ya matseni a jikinsa yana sauke wani irin numfashi yun'kurin k'wace jikina nayi ya sake matseni a raunane yace."Ba zan sake ki ba sai kin yafe min." Hawaye suka sake xubo min nace"Me kayi min kake neman yafiya a gurina ni ai baiwa ce zan iya kwanciya kabi ta kaina kaga dan ka 'kona ni ai ba wani abu bane."
Saukar hannushi naji a kirjina yana shafawa, "am sorry my love." a hard'e ya fadi maganar, yanda yake shafa fatar gurin yasa tsigar jikina duk ta tashi, gabadaya naji gwiwata tayi sanyi, a raunane nace"Sake ni na yafe maka." K'in saki na yayi ya cigaba da shafar gurin 'kunar yana sauke min hucin numfashinsa a wuyana, jikina yay la'asar ikon Ubangiji Allah ya had'ani da nataccen mutum........"Ki bari na duba miki." Da sauri nace."Nifa ban 'kone ba ka sake ni na tafi na yafe maka."
Da sauri ya juyo dani kafad'una ya rike ya kurawa fuskata ido kafin naga ya sauke idonsa inda k'unun ya zubawa ido ." ina kallonsa yasa bakinsa yana hura gurin, nayi saurin ture kansa gabana na bugawa, a buge ya dago yana kallona da jajayen idanunsa, dauke kaina nayi daga kallon fuskarsa dan gabadaya ni yanzu al'amarin sa tsoro yake bani.
Hannu yasa ya juyo da fuskata yana wani marairaice fuska yasa harshe yana lashe bushashshen hawayen daya bushe a fuskata......mirya na rawa nace"Dan darajar Allah ka bari babu kyau fa abinda da kakeyi ka sakeni na tafi wallahi na yafe maka."
Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke naga ya daidaita nutsuwarsa hannuna ya rike ya fara tafiya.
Turjewa nayi cikin faduwar gaba nace"Ina zaka kaini." ?
"Zan duba miki 'kunar ne." Girgixa kaina nayi nace"Ka barta kawai in Allah ya yarda ba zata tashi ba.'' Ido ya tsira a gurin kafin ya sauke ajiyar zuciya ya kalleni, dauke kaina nayi saboda bana son kallon kwayoyin idanunsa, "Sumayya.'' kallonsa nayi saboda yanda naji ya ambaci sunan nawa ya cigaba da cewa" Maimartaba ya umarce ni akan lallai na janye maganar aurena dake."
Ajiyar zuciya na sauke lokaci guda naji wani irin farin ciki ya mamaye zuciyata.
Girgiza kansa yayi yace.''Nasan jin wannan maganar yasa ki farin ciki ko.''' shuru nayi ina kallonsa! girgiza kansa yayi yana wani murmushi yace."Ni yaro ne mai biyayya gami da bin umarnin iyayena saboda haka zanyi kokari ganin nabi umarnin mahaifina ammafa ki sani duk hanyar da nasan zanbi na hanaku rayuwar jin dadi dake da masoyin naki na sani mafita a nan shine ki mallaka min abinda nake 'kulafuci idan na samu ko sau daya ne to zan barki ki zauna lafiya da mijinki.''
Yanda yake maganar ya nuna min da cewa tabbas zai iya aikata komai akaina da Haruna, jikina ne yayi sanyi na dinga jin tsoron sharrinsa kasa magana kawai nayi na zuba masa jajayen idanuna.
"Baki ce komai ba." Yafada yana sake nani'kar Jikina.''
''Yallabai bani da abinda zance maka saboda na fahimci kayi nisa kuma baka tsoron Allah akan biyan bukatarka babu komai duk abinda zakayi mana kaje kayi Allah yana kallonka.''
"Okey! wannan maganar taki ta nuna min cewa ba zaki bani abinda nake bukata ba."
Hamza yace.Hakane maganarki Sumayya mu bamu ga laifinki ba wallahi saboda tuntuni mun riga mun san halinki ba zaki cutar damu ba sabida haka ki kwantar da hankalinki duk wanda kikaga ya mutu to dama can kwanansa ya kare Allah yasa ta wannan sanadin Isa zai rasa rayuwarsa muna rokon Allah ya kar'bi shahadarsa.''
Jiki a sanyaye na amsa da ameen ya rabbi ni zan shiga gurin Yarima." Suka ce to sai kin fito."
Yana tsaka da saukowa daga benan shi na shiga, sai na tsaya har ya karasa saukowa, kauda 'bacin raina nayi na gaishe shi. a dakile ya amsa min. nace"Me zakace dangane da abinda ya faru jiya."? Harara ya watsa mun yace." 'Yar jarida ce ke da zaki titsiye ni da tambaya."?
A dake nace"Dole na titsiye ka da tambaya saboda duk abinda 'yan uwanka keyi maka baka ta'ba yarda gashi sanadiyar cin doyar da aka zuba maka guba a ciki wani yaci ya mutu ina fatan yanzu ka gazgata maganata."
"Kinga Sumayya ba wannan ne a gabana ba wanda ya mutu dama can kwanansa ya 'kare mai yasa su sauran da suka ci doyar basu mutu ba, bana son zargi akan abinda mutum baida tabbas a kai nayi binkice na gane ba guba ce ta janyo faruwar al'amarin ba man da yarinyar tayi suyar doyar dashi shine ya gur'bata saboda haka kada na sake jin kinyi wata magana akan wannan al'amarin idan na sake jin kin sako wani nawa a ciki sai ranki ya 'baci!
Kallon shashasha nayi masa nace"Ai dama ba zaka ta'ba yarda ba sai ranar da suka kai ka 'kasa sannan zaka yarda da abinda ake fada maka! kai me 'yan uwa kullum baka so ace ga abunda sukayi maka su kuma kullum cikin shirya maka mugun abu suke ka'ki ka gane ka dauki son duniya ka d'ora musu idan sun kashe ka iyayenka su sukayi asara su kuwa ranar zasuyi kwanan farin ciki bukatarsu ta biya a kanka."
Har na 'kare maganata idanunsa na tsaye a kaina, yace.''Idan sun kashe ni ina ruwanki."? shuru nayi ina kallonsa ya cigaba da cewa 'yan uwana ne ba naki ba ko Wu'ka suka dauko suna yankar namar jikina idone naki kullum ina fad'a miki cewa ki fitar da kanki akan abinda be shafeki ba kin'ki kije kiyi tayi yanda suke farautata kema ba zasu barki ba." Yana gama maganarsa yazo ya wuce ta gabana fita yayi daga falon, da sauri nabi bayansa na sameshi tsaye shida hadimansa suna magana nan na gane gurin jana'izar Isa zasu tafi! a sanyaye na nufi gurinmu ina share hawaye shikkenan Isa ya mutu mutumin kirki sarkin fara'a da barkwanci Isa bashi da abokin fada kullum zaka sameshi da carbi a hannunsa, duk wanda yasan Isa dole ne ya fad'i halinsa nagari.
Koda na koma gurinmu shuru na same shi Tambaya bata nan shima babana baya nan jikina ya bani dukkaninsu sun nufi gurin jana'izar Isa, juyawa nayi nima da niyyar naje can inda ake jana'izar sai kuma nayi wani tunani gurin nasan akwai dandazon mutane ina iya zuwa wata hatsaniyar ta tashi, can kuryar daki na shiga na kwanta a shimfidata rufin dakin na tsirawa ido ina tunanin rayuwa hakika da ina da inda yafi nan da tuni na gudu dan masifar ta isa haka! tunani nake akan maganarmu dashi ta dazu na yarda da maganarsa da yake cewa nima ba zasu barni ba saboda yanda nake saka ido sosai akansa da dukkanin abinda suke aikatawa, ni kaina na rasa me yasa nake damuwa dashi da lafiyarsa sam! bana kaunar abinda zai cutar dashi ko ya ta'ba lafiyarsa inda shi kuma kullum yake nuna min na tsaya a matsayina babu ruwana da 'yan uwansa babu shakka da zan iya dauke idona daga kansa da abinda suke masa to dana zauna lafiya, amma ba zan iya ba saboda ina tsananin tausayawa mahaifiyarsa da mahaifinsa da suka qallafa ransu a kansa, hawaye masu dumi ne suka zubo a kumatuna nasa hannu na goge wasu na sake zubowa hakika ina cikin tsaka mai wuya ina rokon Allah ya kawo mana mafita dani dashi da dukkanin wanda yake da damuwa a cikin zuciyarsa.............Haka na yini a kwance lokacin sallah ne kawai yake tayar dani, Tambaya bata shigo gidan ba sai dab da magariba ta shigo kai tsaye kicin ta nufa ta ajiye kayan abincin hannunta, tsakar gidan na fito muka hadu tace"Ashe kina ciki dama."? kaina na daga nace "Tun dazu dana shigo na tarar bakwa nan bacci ya dauke ni." Tace."Ayya ai bayan futar ki can gurun Iyayen Isa naje akayi jana'iza dani la'asar nayi kuma na nufi gurin aikin abinci shiyasa ban shigo da wuri ba." Nace"Sannu da aiki nima nayi niyyar zuwa sai na fasa saboda gudun abinda ka iya zuwa ya dawo.''
Tace."Ai gwara da baki je ba dan ni kaina zaman hakuri nayi a gurin Lami da sauran mutane sun had'u sai gulma sukeyi suna zaginki dauke kaina kurrum nayi na rabu dasu sukayi su gama." Girgiza kaina nayi cikin 'kunar zuciya nace"Tambaya kada ki damu Allah yana tare da masu gaskiya kedai ki tsananta addua a gurin Allah ya bayyana gaskiyar lamari." Tace!"Addua kullum cikin yin ta nake Insha Allahu Allah sai ya kare ki daga sharrin masu shari.'' Ameen nace na dauki buta domin daura alwalar sallar magariba....
*Na kudi ne*
Kada ki karanta min littafi baki biya ba keda kika futar da book din keda Allah idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal gruop#300 account.. 0542382124...Binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
77
Sosai ya rike 'kuguna ya matseni a jikinsa yana sauke wani irin numfashi yun'kurin k'wace jikina nayi ya sake matseni a raunane yace."Ba zan sake ki ba sai kin yafe min." Hawaye suka sake xubo min nace"Me kayi min kake neman yafiya a gurina ni ai baiwa ce zan iya kwanciya kabi ta kaina kaga dan ka 'kona ni ai ba wani abu bane."
Saukar hannushi naji a kirjina yana shafawa, "am sorry my love." a hard'e ya fadi maganar, yanda yake shafa fatar gurin yasa tsigar jikina duk ta tashi, gabadaya naji gwiwata tayi sanyi, a raunane nace"Sake ni na yafe maka." K'in saki na yayi ya cigaba da shafar gurin 'kunar yana sauke min hucin numfashinsa a wuyana, jikina yay la'asar ikon Ubangiji Allah ya had'ani da nataccen mutum........"Ki bari na duba miki." Da sauri nace."Nifa ban 'kone ba ka sake ni na tafi na yafe maka."
Da sauri ya juyo dani kafad'una ya rike ya kurawa fuskata ido kafin naga ya sauke idonsa inda k'unun ya zubawa ido ." ina kallonsa yasa bakinsa yana hura gurin, nayi saurin ture kansa gabana na bugawa, a buge ya dago yana kallona da jajayen idanunsa, dauke kaina nayi daga kallon fuskarsa dan gabadaya ni yanzu al'amarin sa tsoro yake bani.
Hannu yasa ya juyo da fuskata yana wani marairaice fuska yasa harshe yana lashe bushashshen hawayen daya bushe a fuskata......mirya na rawa nace"Dan darajar Allah ka bari babu kyau fa abinda da kakeyi ka sakeni na tafi wallahi na yafe maka."
Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke naga ya daidaita nutsuwarsa hannuna ya rike ya fara tafiya.
Turjewa nayi cikin faduwar gaba nace"Ina zaka kaini." ?
"Zan duba miki 'kunar ne." Girgixa kaina nayi nace"Ka barta kawai in Allah ya yarda ba zata tashi ba.'' Ido ya tsira a gurin kafin ya sauke ajiyar zuciya ya kalleni, dauke kaina nayi saboda bana son kallon kwayoyin idanunsa, "Sumayya.'' kallonsa nayi saboda yanda naji ya ambaci sunan nawa ya cigaba da cewa" Maimartaba ya umarce ni akan lallai na janye maganar aurena dake."
Ajiyar zuciya na sauke lokaci guda naji wani irin farin ciki ya mamaye zuciyata.
Girgiza kansa yayi yace.''Nasan jin wannan maganar yasa ki farin ciki ko.''' shuru nayi ina kallonsa! girgiza kansa yayi yana wani murmushi yace."Ni yaro ne mai biyayya gami da bin umarnin iyayena saboda haka zanyi kokari ganin nabi umarnin mahaifina ammafa ki sani duk hanyar da nasan zanbi na hanaku rayuwar jin dadi dake da masoyin naki na sani mafita a nan shine ki mallaka min abinda nake 'kulafuci idan na samu ko sau daya ne to zan barki ki zauna lafiya da mijinki.''
Yanda yake maganar ya nuna min da cewa tabbas zai iya aikata komai akaina da Haruna, jikina ne yayi sanyi na dinga jin tsoron sharrinsa kasa magana kawai nayi na zuba masa jajayen idanuna.
"Baki ce komai ba." Yafada yana sake nani'kar Jikina.''
''Yallabai bani da abinda zance maka saboda na fahimci kayi nisa kuma baka tsoron Allah akan biyan bukatarka babu komai duk abinda zakayi mana kaje kayi Allah yana kallonka.''
"Okey! wannan maganar taki ta nuna min cewa ba zaki bani abinda nake bukata ba."