Sashe 37
Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Na kudi ne..!*
Kika karanta baki biya ba Allah ya isa! idan kina bukatar ki biya ga yanda abin yake...Vip group #600 normal gruop#300 account... 0542382124...Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 sai kiyi min mgn ta whasap da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
69&70
Gabad'aya tsarguwa nayi da yanayin kallon da mutane suke min bina suke da kallon zargi da tuhuma sun had'a rukuni rukuni suna surutai a kaina kowa dai da abinda yake fad'a dangane da faruwar al'amarin, can gefe na hango iyayena cikin yanayi na tsantsar damuwa da tashin hankali Tambaya sai hawaye take sharewa babana ne mai karfin halin danne abinda ke zuciyarsa amma kallo guda za kayi masa ka gane cewar yana cikin tashin hankali......Zuciyata ce ta sake karyewa zafafan hawaye suka zubo min da sauri nasa hannu na goge nayi kasa da kaina gami da cigaba da bin bayan jakada zuciyata cike da wasiwahsin abinda zanje na tarar a fadar sarki, duk nasan ina da gaskiya amma zuciyata ta kasa tsayawa guri d'aya sai sa'ke-sa'ke takeyi min dangane da abinda ya faru.
Ganin Maimartaba a tsaye yana kai komo yasa naji gwiwata ta sage, a sanyaye na zube a kasan gurin murya na rawa nace"Ranka ya dad'e barka da wannan lokaci ina rokon Allah ya ja zamanin ka ya kara maka lafiya da nisan kwana." Zama yayi kan kujerarsa ya tsira min ido, sunkuyar da kaina nayi ina wasa da yatsun hannuna. Maimartaba kallon yarinyar yake yi yana mamakin abinda ta aikata masa a masarauta dole ne ya binkiceta domin sanin wanda ya sata zubawa d'ansa guba mai karfi a cikin abinci."
A nutse yace."Yarinya ya sunanki."? Kaina a kasa nace"Sunana Sumayya Lawi. kallona yake yana girgiza kansa, Yace."Yanzu na samu labarin abinda ya faru a bangaranku ina so ki fada min gaskiyar magana."
Hawaye ne suka zubo min da sauri nasa hannuna na goge wasu suka sake zubowa. gyaran mirya yayi yace."Ba kuka nace kiyi ba kiyi min bayani akan irin gubar da kika zubawa d'an uwanki musulmi."
Muryata na rawa nace"Ranka ya dade na rantse da wanda raina yake a hannunsa ban sawa kowa guba ba." Shuru yayi na minti biyu kafin yace."To kinyi rantsuwa da Allah Sumayya kin san Allah ba abun wasa bane idan baki sa musu guba a abinci ba ya akayi bayan sunci abincin da kika basu suka fita daga hayyacinsu."
A sanyaye nace"Naje sashen Yarima domin nayi ayyukan dana saba sai na tarar da Suwaiba tana soya doya da 'kwai Yarima ya shigo kicin din ya sallameta yace ba zai zauna ya ci komai ba saboda ya makara a gurin aiki, ganin kada ayi asarar doyar yasa na juye a cikin kula na kawowa su Haruna daga nan na wuce gurin karatu ina zaune a cikin 'yan uwana malam ya shigo ya fito dani yana tuhumata akan wannan dalilin daya faru Ranka ya dade wannan shine iyakacin abinda na sani."
Shuru fadar tayi Maimartaba yana nazari akan maganar da nayi, yace."Me ya hanaki cin doyar bayan kema kina bukata." Jin abinda yace ya sanya gabana faduwa, cikin mika lamura na ga Allah nace"Lokacin ina sauri na shiga karatu shiya banyi tunanin tsayawa naci ba." Girgiza kansa yayi kafin ya kalli Jakada dake tsaye a bakin kofa yace."Kaje da yarinyar can cikin gida ka rufeta a dakin duhu gabad'aya hujjojin da ta kawo basu gamsar dani ba ina ganin idan taji matsa zata fada min yanda al'amarun suka faru."
Kuka na fashe dashi nace"Ranka ya dade wallahi tallahi iya gaskiyata na fada maka ban san komai ba akan faruwar wannan al'amari ranka ya dade ka yarda da rantsuwata."
Babu yabo babu fallasa yace."Kwantar da hankali binkice zanyi akan al'amarin idan na gano gaskiya zansa a fito dake." Gwiwa a sanyaye nace"Godiya nake ranka ya dade ina rokon Allah ya bayyana mai gaskiya akan faruwar wannan al'amari." Ameeen yace ya bawa Jakada umarnin tafiya dani dakin duhu.
"Ya sunanki."? Suwaiba dake gurfane tana shar" ba gumi tace"Sunana Suwaiba Munzali." Maimartaba yace."Ke kika soya doya a bangaran Yarima ko."? da sauri tace"Eh nice ranka ya dade." Yace."Waye ya baki guba kisawa Yarima a cikin abincinsa." Suwaiba hannu tasa ta sharce gumin goshinta cikin inda inda tace "Ranka ya dade babu kowa." Yace."Sumayya ta tabbatar min da cewa kece kika soya doyar ta shigo ta sameki kina aiki kafin Yarima ya sallame ki bana son kiyi min gardama akan abinda na tambayeki inaso ki fada min gaskiyar abinda ya faru.''
Suwaiba kuka ne ya 'kwace mata jiki na kyarma tace"Wallahi babu kowa ranka ya dade ni dai nasan na soya doya da kwai amma bansan abinda ya biyo baya ba."
Shuru yayi yana kallonta babu shakka yaran naso suyi masa wasa da hankali a cikinsu dole a samu mai gaskiya da mara gaskiya dan haka itama Suwaibar tunda ta'ki fada masa gaskiyar magana sai kawai ya umarci Jakada da ya kaita dakin duhu inda yasa aka kai Sumayya.
Mun jima muna kallon junanmu cikin yanayi na tashin hankali da damuwa nace"Suwaiba ashe baki ji maganata ba sai da kika janyo mana shiga masifa yanzu meye ribarki a duniya idan aka hada baki dake aka kashe rai me zaki ce da Ubangiji a ranar lahira."
"Ke kinga Sumayya kada ki d'ora min sharri dan sabida kinga ta kwa'be dake a ciki shine zaki ce naji tsoron Allah to idan banji tsoransa ba tsoranki zanji mtssw! dan Allah kada ki sakeyi min wannan maganar dan ni ban zubawa kowa guba a abinci ba kije ki tuhumi kanki."
Tsabar haushi da takaici kasa cewa komai nayi ina kallonta sai surutai take tana fuffukar karya nace"Shikkenan tunda kin k'aryata kanki akan abinda kika aikata insha Allahu a yau sai Allah ya tona muku a siri keda wa'inda suka saki."
"Sai dai Allah ya tona miki asiri banza kawai! kece baki da tabbas amma ni na tabbata ba zan kwana a gurin nan ba za'a fito dani banza kawai."
Shuru nayi mata ina jinta tana zagina gami da fadin na zuba ido na gani sai an fita da ita daga gurin an bar ni a ciki.
Gefe guda na samu na karkade kurar dake gurin na zauna ina bin dakin da kallo, tabbas ya amsa sunansa dakin duhu babban daki ne wanda yake da taga d'aya itama yar mitsitsiya kuma acan sama take, ta wannan tagar haske yake dan shigowa, idan mutun na dakin baya gane yanayin gari safiya ko dare sai dai kawai kaji kiran sallah yanzu ma hakane ya kasance ina zaune a gefe Suwaiba na zurga zurga a dakin mukaji kiran sallar magariba na mike tsaye na isa bakin kofar fita, kofar na dinga jijjigawa rufe take gam ko motsi takiyi, juyowa nayi cikin rauni da sarewa da al'amarin muka had'a ido da Ita gani nayi tana share hawaye nace"A'a ya kike kuka keda kikace baki da damuwa."
Tsaki taja ta koma jikin bango ta jingina, girgiza kaina nayi naje na zauna a inda na tashi, addua na cigaba dayi a cikin zuciyata
Motsin bude kofar mukaji da sauri na mike tsaye Suwaiba kuwa har ta kai bakin kofar tana zazzare ido.
Wani babban bawa ne ya bude kofar duk muka zuba masa ido muna kallonsa, gefe ya matsa yana me yin kasa da kansa, Muddibo ne ya shigo dakin, gabana ya yanke ya fadi ganin yana watsa min wani irin kallo, sunkuyar da kaina nayi, ya kalli Suwaiba da fadin"Biyo bayana." Da sauri na dago kaina naga Suwaiba da sauri tabi bayansa nima sai na rufa mata baya, tana fita nayi yunkurin bin bayanta mari ya kwada min ya tankad'ani ciki faduwa nayi kaina ya bugu da wani babban dutse dake girke a gurin, dishi dishi na dinga gani kafin na fadi a gurin, Muddibo umartar bawan yayi da yayi maza ya kulle dakin..........
Magajin sarki ya shiga tsananin rudani a lokacin da aka kai masa manya hadiman sa a sume a take ya shiga basu taimakon gaggawa da irin baiwar da Allah yayi masa, cikin ikon Allah Haruna da Hamza suka farfado Isa kuwa ta Allah ta kasance a kansa ya mutu, Haruna da Hamza suka dinga kuka suna kallon gawar dan uwansu, Magajin sarki duk dauriyarsa sai da ya zubar da hawaye hakika mutuwar Isa ta ta'ba shi, ma'aikata ya umarta dasu had'a gawar Isa su daureta.
Lokacin da Maimartaba ya samu labarin mutuwar daya daga cikin mutum ukun da tsautsayin ya ritsa dasu, hankalinsa ya tashi ainu! ya dinga mamakin al'amarin yana tunanin da tuni fa d'ansa ne zai mutu idan da Allah ya nufe shi dacin doyar, lallai babu shakka dole ya tsautsara binkice akan wa'inda keda hannu gurin faruwar wannan al'amari.
Magajin Sarki bai bari ya fito daga asibitin ba sai da ya tsananta binkicensa akan sanin wace irin guba akayi amafani da ita domin a cutar dashi, ragowar doyar dasu Haruna suka rage ita yasa aka dauko masa yayi ta binkice a kanta har sai da ya gano yanda al'amarin yake, anyi amfani da gubar ne a cikin man da'aka soya doyar ya dinga girgiza kansa tabbas wanda ya aikata wannan aikin bashi da imani kuma baya k'aunarsa da gasken gaske, dole ne shima ya tsananta binkicensa akan faruwar al'amarin......hannuwansa ya wanke tas ya dauki rigarsa ta likitoci yasa yasa farin gilashinsa, kana ya kwashi wayoyinsa da duk abinda yake bukata ya fita daga ofis din nasa,
Direban sa ne ya bude kasa kofar mota ya shiga ya zauna, da sauri ya zagaya gurin zamansa ya kunna motar suka fita daga asibitin........a rikice ya tarar da gidan sarautar mutane sunyi cirko cirko kowa yana alhini akan abinda ya faru, umartar direban yayi daya yatsar da motar, ya zuge glass wani bawa ya kira da sauri yaje ya runkufa yana gaisheshi ba tare daya amsa ba yace."Kowa ya koma gurinsa tsayuwar bata da amfani wanda ya mutu ya riga ya mutu addua zakuyi masa." Da sauri bawan yace."Ranka ya dade a gafarce mu bari nayi sauri na isar musu da sakon ka."
Gilashin motar ya rufe ya bawa direba umarin tafiya.
Kika karanta baki biya ba Allah ya isa! idan kina bukatar ki biya ga yanda abin yake...Vip group #600 normal gruop#300 account... 0542382124...Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 sai kiyi min mgn ta whasap da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
69&70
Gabad'aya tsarguwa nayi da yanayin kallon da mutane suke min bina suke da kallon zargi da tuhuma sun had'a rukuni rukuni suna surutai a kaina kowa dai da abinda yake fad'a dangane da faruwar al'amarin, can gefe na hango iyayena cikin yanayi na tsantsar damuwa da tashin hankali Tambaya sai hawaye take sharewa babana ne mai karfin halin danne abinda ke zuciyarsa amma kallo guda za kayi masa ka gane cewar yana cikin tashin hankali......Zuciyata ce ta sake karyewa zafafan hawaye suka zubo min da sauri nasa hannu na goge nayi kasa da kaina gami da cigaba da bin bayan jakada zuciyata cike da wasiwahsin abinda zanje na tarar a fadar sarki, duk nasan ina da gaskiya amma zuciyata ta kasa tsayawa guri d'aya sai sa'ke-sa'ke takeyi min dangane da abinda ya faru.
Ganin Maimartaba a tsaye yana kai komo yasa naji gwiwata ta sage, a sanyaye na zube a kasan gurin murya na rawa nace"Ranka ya dad'e barka da wannan lokaci ina rokon Allah ya ja zamanin ka ya kara maka lafiya da nisan kwana." Zama yayi kan kujerarsa ya tsira min ido, sunkuyar da kaina nayi ina wasa da yatsun hannuna. Maimartaba kallon yarinyar yake yi yana mamakin abinda ta aikata masa a masarauta dole ne ya binkiceta domin sanin wanda ya sata zubawa d'ansa guba mai karfi a cikin abinci."
A nutse yace."Yarinya ya sunanki."? Kaina a kasa nace"Sunana Sumayya Lawi. kallona yake yana girgiza kansa, Yace."Yanzu na samu labarin abinda ya faru a bangaranku ina so ki fada min gaskiyar magana."
Hawaye ne suka zubo min da sauri nasa hannuna na goge wasu suka sake zubowa. gyaran mirya yayi yace."Ba kuka nace kiyi ba kiyi min bayani akan irin gubar da kika zubawa d'an uwanki musulmi."
Muryata na rawa nace"Ranka ya dade na rantse da wanda raina yake a hannunsa ban sawa kowa guba ba." Shuru yayi na minti biyu kafin yace."To kinyi rantsuwa da Allah Sumayya kin san Allah ba abun wasa bane idan baki sa musu guba a abinci ba ya akayi bayan sunci abincin da kika basu suka fita daga hayyacinsu."
A sanyaye nace"Naje sashen Yarima domin nayi ayyukan dana saba sai na tarar da Suwaiba tana soya doya da 'kwai Yarima ya shigo kicin din ya sallameta yace ba zai zauna ya ci komai ba saboda ya makara a gurin aiki, ganin kada ayi asarar doyar yasa na juye a cikin kula na kawowa su Haruna daga nan na wuce gurin karatu ina zaune a cikin 'yan uwana malam ya shigo ya fito dani yana tuhumata akan wannan dalilin daya faru Ranka ya dade wannan shine iyakacin abinda na sani."
Shuru fadar tayi Maimartaba yana nazari akan maganar da nayi, yace."Me ya hanaki cin doyar bayan kema kina bukata." Jin abinda yace ya sanya gabana faduwa, cikin mika lamura na ga Allah nace"Lokacin ina sauri na shiga karatu shiya banyi tunanin tsayawa naci ba." Girgiza kansa yayi kafin ya kalli Jakada dake tsaye a bakin kofa yace."Kaje da yarinyar can cikin gida ka rufeta a dakin duhu gabad'aya hujjojin da ta kawo basu gamsar dani ba ina ganin idan taji matsa zata fada min yanda al'amarun suka faru."
Kuka na fashe dashi nace"Ranka ya dade wallahi tallahi iya gaskiyata na fada maka ban san komai ba akan faruwar wannan al'amari ranka ya dade ka yarda da rantsuwata."
Babu yabo babu fallasa yace."Kwantar da hankali binkice zanyi akan al'amarin idan na gano gaskiya zansa a fito dake." Gwiwa a sanyaye nace"Godiya nake ranka ya dade ina rokon Allah ya bayyana mai gaskiya akan faruwar wannan al'amari." Ameeen yace ya bawa Jakada umarnin tafiya dani dakin duhu.
"Ya sunanki."? Suwaiba dake gurfane tana shar" ba gumi tace"Sunana Suwaiba Munzali." Maimartaba yace."Ke kika soya doya a bangaran Yarima ko."? da sauri tace"Eh nice ranka ya dade." Yace."Waye ya baki guba kisawa Yarima a cikin abincinsa." Suwaiba hannu tasa ta sharce gumin goshinta cikin inda inda tace "Ranka ya dade babu kowa." Yace."Sumayya ta tabbatar min da cewa kece kika soya doyar ta shigo ta sameki kina aiki kafin Yarima ya sallame ki bana son kiyi min gardama akan abinda na tambayeki inaso ki fada min gaskiyar abinda ya faru.''
Suwaiba kuka ne ya 'kwace mata jiki na kyarma tace"Wallahi babu kowa ranka ya dade ni dai nasan na soya doya da kwai amma bansan abinda ya biyo baya ba."
Shuru yayi yana kallonta babu shakka yaran naso suyi masa wasa da hankali a cikinsu dole a samu mai gaskiya da mara gaskiya dan haka itama Suwaibar tunda ta'ki fada masa gaskiyar magana sai kawai ya umarci Jakada da ya kaita dakin duhu inda yasa aka kai Sumayya.
Mun jima muna kallon junanmu cikin yanayi na tashin hankali da damuwa nace"Suwaiba ashe baki ji maganata ba sai da kika janyo mana shiga masifa yanzu meye ribarki a duniya idan aka hada baki dake aka kashe rai me zaki ce da Ubangiji a ranar lahira."
"Ke kinga Sumayya kada ki d'ora min sharri dan sabida kinga ta kwa'be dake a ciki shine zaki ce naji tsoron Allah to idan banji tsoransa ba tsoranki zanji mtssw! dan Allah kada ki sakeyi min wannan maganar dan ni ban zubawa kowa guba a abinci ba kije ki tuhumi kanki."
Tsabar haushi da takaici kasa cewa komai nayi ina kallonta sai surutai take tana fuffukar karya nace"Shikkenan tunda kin k'aryata kanki akan abinda kika aikata insha Allahu a yau sai Allah ya tona muku a siri keda wa'inda suka saki."
"Sai dai Allah ya tona miki asiri banza kawai! kece baki da tabbas amma ni na tabbata ba zan kwana a gurin nan ba za'a fito dani banza kawai."
Shuru nayi mata ina jinta tana zagina gami da fadin na zuba ido na gani sai an fita da ita daga gurin an bar ni a ciki.
Gefe guda na samu na karkade kurar dake gurin na zauna ina bin dakin da kallo, tabbas ya amsa sunansa dakin duhu babban daki ne wanda yake da taga d'aya itama yar mitsitsiya kuma acan sama take, ta wannan tagar haske yake dan shigowa, idan mutun na dakin baya gane yanayin gari safiya ko dare sai dai kawai kaji kiran sallah yanzu ma hakane ya kasance ina zaune a gefe Suwaiba na zurga zurga a dakin mukaji kiran sallar magariba na mike tsaye na isa bakin kofar fita, kofar na dinga jijjigawa rufe take gam ko motsi takiyi, juyowa nayi cikin rauni da sarewa da al'amarin muka had'a ido da Ita gani nayi tana share hawaye nace"A'a ya kike kuka keda kikace baki da damuwa."
Tsaki taja ta koma jikin bango ta jingina, girgiza kaina nayi naje na zauna a inda na tashi, addua na cigaba dayi a cikin zuciyata
Motsin bude kofar mukaji da sauri na mike tsaye Suwaiba kuwa har ta kai bakin kofar tana zazzare ido.
Wani babban bawa ne ya bude kofar duk muka zuba masa ido muna kallonsa, gefe ya matsa yana me yin kasa da kansa, Muddibo ne ya shigo dakin, gabana ya yanke ya fadi ganin yana watsa min wani irin kallo, sunkuyar da kaina nayi, ya kalli Suwaiba da fadin"Biyo bayana." Da sauri na dago kaina naga Suwaiba da sauri tabi bayansa nima sai na rufa mata baya, tana fita nayi yunkurin bin bayanta mari ya kwada min ya tankad'ani ciki faduwa nayi kaina ya bugu da wani babban dutse dake girke a gurin, dishi dishi na dinga gani kafin na fadi a gurin, Muddibo umartar bawan yayi da yayi maza ya kulle dakin..........
Magajin sarki ya shiga tsananin rudani a lokacin da aka kai masa manya hadiman sa a sume a take ya shiga basu taimakon gaggawa da irin baiwar da Allah yayi masa, cikin ikon Allah Haruna da Hamza suka farfado Isa kuwa ta Allah ta kasance a kansa ya mutu, Haruna da Hamza suka dinga kuka suna kallon gawar dan uwansu, Magajin sarki duk dauriyarsa sai da ya zubar da hawaye hakika mutuwar Isa ta ta'ba shi, ma'aikata ya umarta dasu had'a gawar Isa su daureta.
Lokacin da Maimartaba ya samu labarin mutuwar daya daga cikin mutum ukun da tsautsayin ya ritsa dasu, hankalinsa ya tashi ainu! ya dinga mamakin al'amarin yana tunanin da tuni fa d'ansa ne zai mutu idan da Allah ya nufe shi dacin doyar, lallai babu shakka dole ya tsautsara binkice akan wa'inda keda hannu gurin faruwar wannan al'amari.
Magajin Sarki bai bari ya fito daga asibitin ba sai da ya tsananta binkicensa akan sanin wace irin guba akayi amafani da ita domin a cutar dashi, ragowar doyar dasu Haruna suka rage ita yasa aka dauko masa yayi ta binkice a kanta har sai da ya gano yanda al'amarin yake, anyi amfani da gubar ne a cikin man da'aka soya doyar ya dinga girgiza kansa tabbas wanda ya aikata wannan aikin bashi da imani kuma baya k'aunarsa da gasken gaske, dole ne shima ya tsananta binkicensa akan faruwar al'amarin......hannuwansa ya wanke tas ya dauki rigarsa ta likitoci yasa yasa farin gilashinsa, kana ya kwashi wayoyinsa da duk abinda yake bukata ya fita daga ofis din nasa,
Direban sa ne ya bude kasa kofar mota ya shiga ya zauna, da sauri ya zagaya gurin zamansa ya kunna motar suka fita daga asibitin........a rikice ya tarar da gidan sarautar mutane sunyi cirko cirko kowa yana alhini akan abinda ya faru, umartar direban yayi daya yatsar da motar, ya zuge glass wani bawa ya kira da sauri yaje ya runkufa yana gaisheshi ba tare daya amsa ba yace."Kowa ya koma gurinsa tsayuwar bata da amfani wanda ya mutu ya riga ya mutu addua zakuyi masa." Da sauri bawan yace."Ranka ya dade a gafarce mu bari nayi sauri na isar musu da sakon ka."
Gilashin motar ya rufe ya bawa direba umarin tafiya.