Sashe 29
Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin tsawa yace."Ke kada ki rainawa mutane hankali mana! wace irin fahimtar juna ce wannan? ace kullum yana binki a dik inda kike kada ku sake ku aikata min fasiqanci a guri wallahi tallahi kika sake na kama ku sai na d'auki babban mataki a kanku."
Na dinga kallonsa zuciya na tafarfasa tsabar bacin rai naji yawun bakina ya bushe guy nan bai ta'ba 'bata min rai irin yau ba amma bari nayi maganinsa.
Babu sukuni nace"Haruna kamaman namiji ne hakanan Sumayya kamammiyar macece, Haruna da Sumayya suna san junansu shiyasa suke nesa da junansu saboda suna so suyi aure mai tsabta, ranka ya d'ade shi fasiqi ya futa daban! ana gane fasiqi a fuska da ayyukansa ba duka mutane suka taru suka zama d'ay......Wawan! duka ya kaiwa bakina nayi saurin kaucewa ina kallonsa, idanunsa naga sunyi jawur! gabana ya dinga bugawa! "Me kike nufi da wannan maganar da kike."?
Cikin dauriya nace" Bana nufin komai ranka ya dad'e inaso na nuna maka cewar maganar da kayi a kan mu bata dace ba zargi haram....."Rufe min baki munufaka."!! katseni yay da wannan magana. shuru nayi ina kallonsa, ya jima yana kallon k'asan kilishin da yake zaune, ya dago ido jawur yace."Tashi ki fice min a guri bana bukatar kallon wannan bakar fuskar taki."
"Ranka ya dad'e kayi hak..! hannu ya daga min alamun baya so na karasa, shiru nayi na yunkura na mike.." Dauke tsiyarki banza 'kazama kawai."! banji ciwon zagin da yayi min ba saboda na riga na saba, tire din dake gabansa nake kallo a sanyaye nace"Kaine fa kace na had'a maka fruit sal.....Kafin na rufe bakina ya dago tire din ya watso min shi a jiki....gabadaya gaban rigarta da zanina ya 'baci 'kasan gurin da gefan kilishin ya lalace... wayoyinsa ya kwasa yana watsa min kallon banza ya bar gurin....ban dauke idona daga kansa ba har sai da na daina ganinshi....hawayen takaici ne suka shiga zubo min a fuska durkushewa nayi a gurin na dinga kukan da yake nema ya tarwatsa min zuciyata.
*Na kudi ne..*
Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina so ki biya kudin ki ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal #300...0542382124..binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number.
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*GAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
55&56
Samun sa nayi a tsaye a tsakiyar falon yana zagaye koda na shiga gefe guda na samu na tsuguna kaina na sunkuyar k'asa ina addua kada Allah yasa ya tozartani a gabanta dan na fahimci take takensa. bece min komai ba ya zauna kan kujera tare da d'ora kafa daya kan daya zaman yayi kama dana kasaita da nuna isa, ta kasan idona nake kallonsa yana ta girgiza kafa yana latsa waya, haka ta shigo ta same mu, kujera ta nema ta zauna, falon yayi shuru na tsayin minti goma a sace na kallesu shi yana can aikin latsa waya ita kuma alamun tsoro da fargaba na hango a cikin idonta.
kaina na mayar kasa ina jin faduwar gaba, ni da ita duk abu daya ne yake damun mu.
"Lawisa me Sumayya tayi miki da zaki sa Buba ya doke ta ."? A sanyaye tace" Laifi tayi min wanda ya fusata ni shine na yanke mata wannan hukuncin.''
"Ba kwana ki nayi miki magana akan hakan ba."? Yafada yana tsareta da ido, cikin dauriya tace" Naso nayi mata hukunci da kaina tayi min gardama shiyasa na kira buba ya koya mata hankali tunda dai ita bata da mutunci.
Saurin kallonta nayi muka hada ido ta watso min harara, kaina na sunkuyar ina jiran naji abinda zaice.
"Me tayi miki abinda nake son ji kenan."? yafada hankalinsa akan wayarsa.....ajiyar zuciya ta sauke tace" Yau tsayin wata kenan ina aikota ta kawo maka sa'ko ashe zuwa take ta zubar a wani guri daya daga cikin bayina suka sheda min koda na tambayeta ba tayi gardama ba ta tabbatar min da gaskiya ne al'amarin ya 'bata min rai sosai shiyasa na yanke mata wannan hukuncin."
Kallona ya shigayi yana gyada kansa yace."Wato ke ba zaki daina saka kanki a cikin abinda be shafe ki ba ko? shuru nayi yace."Me kike nufi akan abinda kike aikatawa ke kowa baki yarda dashi ba 'yan uwana zarginsu kike yi ke yafi kamata nayi zargi tunda kece bare amma na amince nake tarayya dake ban nuna miki komai ba to ki tashi ki fita ki bani guri bana bukatar sake ganinki a gurina dan na gaji da abinda kike min." kallonsa nake inaso nayi magana ya daga min hannu fuska a murtuke yace "bana bukatar sake ganinki a sashena 'yan uwana nawa ne idan kashe ni sukayi babu abinda ya shafe ki saboda haka tashi fice min daga falo."!
Cikin tsawa da kyara ya kare maganar.
Ji nayi gwiwa ta tayi sanyi ruwan hawaye ya taru a kwarmin idona ni kam wannan wulakanci ina zan kai shi, a sanyaye na mike na nufi kofa zuciyata na wani irin zafi......ina fita hawaye ya wanke min fuska, haruna ya tare ni guri muka samu muka zauna sai da nacu kukana na koshi tukkuna na fada masa yanda mukayi.
Yace." Ki daina kuka kada ki janyowa kanki ciwon kai ni wallahi naji dadi ma da haka ta faru saboda haka yanzu abinda za'ayi shine kije can sashen Fulani ina nufin mahaifiyarsa sai ki sheda mata abinda ke faruwa kin san hausawa nacewa ta inda aka hau tanan ake sauka.
Hanci na shaqa na goge fuskata tare da mikewa tsaye nace" dama dole naje na sanar mata dan saboda kada wani abu ya faru daga baya ta zarge ni da wani abu.
Mikewa yay yace."Muje na raka ki ki fada mata." Tare muka tafi muna sake tattaunar maganar.
Ta jima kafin ta dago kanta ganin b'acin rai a fuskarta yasa na sunkuyar da kaina kasa, tace"Sumayya duk naji maganarki raina kuma ya 'baci da irin wulakancin da babana yake miki yanzu ina laifin mai kula da kai abinda babana yayi miki ya bata min rai sosai kiyi hakuri Sumayya kada kiyi fushi kinji ko zaki cigaba da hidima dashi wallahi da ke kadai naji na aminta, ita kanta yarinyar da zai aura bata kwanta min a rai ba dan dai babu yanda zanyi ne tunda iyaye sun shiga cikin lamarin, zan sameshi zanyi masa fada sosai dole ya mutun taki ko dabbah ai tasan mai kyautata mata bare mutum saboda haka kije yanzu zan kirashi a waya zan zauna dashi zamuyi magana kuma zan nuna masa kuransa.
Daurewa nayi ina kokarin danne damuwata nace"Insha Allahu zanbi umarninki zan cigaba da dawainiya da Yarima kamar yanda kike so." Albarka ta dinga sa min kafin ta bani umarnin tafiya sallama nayi mata na fito
Haruna na tsaye yana jira na ina fitowa na fada masa duk yanda mukayi jikinsa ne naga yayi sanyi yace."Shikkenan Sumayya sai ki sake kiyayewa sannan ki daina yawan saka idonki akan 'yan uwansa tunda baya so ki rabu dashi idan da rabon yasha wuya ne shikkenan."
Shuru nayi kawai ina sauraransa bana jin zan iya zuba ido wani ya cutar dashi amana na daukarwa mahaifiyarsa zanyi iyakacin bakin k'okarina sai dai idan abin yafi karfina
A waya ta kira shi ta rufeshi da fad'a ta inda ta shiga bata nan take fita ba sosai ta nuna masa bacin ranta akan abinda yake yi mamaki ne ya rufeshi ashe yarinyar nan zuwa tayi ta had'ashi da mahaifiyarsa ransa idan yay dubu ya 'baci! tunda yake da mahaifiyarsa wani abu na sa'bani bai ta'ba shiga tsakaninsu ba sai ta dalilin yarinyar.....Girgiza kansa yayi ya shiga bata hakuri tace"Haba babana ai dole raina ya 'baci akan abinda kakeyi yarinyar nan kullum na dawainiya da kai amma kullum cikin cizguna mata kakeyi su 'yan uwan naka da kake fifitasu a kanta ba kaunarka sukeyi ba har yanzu ka kasa ganewa cewar kullum farautarka suke to mutukar kana kaunar farin cikina ka mutunta Sumayya bana san cin zarafin da kake mata ka sanja hali."
Ajiyar zuciya ya sauke yace."Mamma naji na d'auki laifina insha Allah zan gyara na daina bana san kina fushi da 'bacin rai akan abinda bai kai ya kawo ba."
"Babana idan ka naso na daina bacin rai sai ka daina abubuwan da kake na rashin kyautawa tukkuna." Hannuwanta ya ri'ke yace."Insha Allahu na daina yarinyar ta dawo ta cigaba da aikinta shikkenan ko."? Ajiyar zuciya ta sauke tace"Shikkenan magana ai ta wuce na bata hakuri sosai anjima da daddare zata shigo ta baka abinci kaima sai ka nemi afuwarta dan Allah yana san haka.
Da mamaki a fuskarsa yake kallonta har abadah baya tsammanin zai iya bawa yarinyar hakuri akan wani laifi da yayi mata kawai dai ya amsa mata ne domin ta kwantar da hankalinta ta kuma daina 'bacin rai akan al'amarin.
To koda na koma gurin mu ban yarda na fadawa iyayena abinda ya faru ba kawai nace musu nayi mata wani aiki ne...Tambaya tace"Muna nan muna tattaunawa akan maganarki da Haruna dan gidan Labaran bayan fitarki yazo gurin babanki suka tattauna ashe dama soyayya ce a tsakaninku mu bamu sani ba."
Kunyace ta rufe ni nayi yar dariya ina kokarin shiga daki nace "Tambaya kenan." Babana dake zaune kan darduma yana murmushin farin ciki yace."Sumayya a gaskiya nayi farin ciki da wannan al'amari sosai na yaba da tarbiyar Haruna yana da nutsuwa da kintsi nayi imanin zai rike min ke da mutunci wannan dalilin yasa na amince da maganar amma na cewa mahaifin nasa sai na zauna dake kin sake tabbatar min da bakin ki.
Shuru nayi ina wasa da hannuwana, yace."Sumayya babu kunya a tsakanina dake ni mahaifin ki ki fada min shin kina son Haruna ko aa."
Murmushi nayi nace"Eh baba ina sonsa ina rokon Allah yasa shi din alkairi ne a tare dani." cike da farin ciki ya amsa da ameeen Sumayya ubangiji Allah ya tabbatar mana da alkairi Allah yasa damu za'ayi."
Na dinga kallonsa zuciya na tafarfasa tsabar bacin rai naji yawun bakina ya bushe guy nan bai ta'ba 'bata min rai irin yau ba amma bari nayi maganinsa.
Babu sukuni nace"Haruna kamaman namiji ne hakanan Sumayya kamammiyar macece, Haruna da Sumayya suna san junansu shiyasa suke nesa da junansu saboda suna so suyi aure mai tsabta, ranka ya d'ade shi fasiqi ya futa daban! ana gane fasiqi a fuska da ayyukansa ba duka mutane suka taru suka zama d'ay......Wawan! duka ya kaiwa bakina nayi saurin kaucewa ina kallonsa, idanunsa naga sunyi jawur! gabana ya dinga bugawa! "Me kike nufi da wannan maganar da kike."?
Cikin dauriya nace" Bana nufin komai ranka ya dad'e inaso na nuna maka cewar maganar da kayi a kan mu bata dace ba zargi haram....."Rufe min baki munufaka."!! katseni yay da wannan magana. shuru nayi ina kallonsa, ya jima yana kallon k'asan kilishin da yake zaune, ya dago ido jawur yace."Tashi ki fice min a guri bana bukatar kallon wannan bakar fuskar taki."
"Ranka ya dad'e kayi hak..! hannu ya daga min alamun baya so na karasa, shiru nayi na yunkura na mike.." Dauke tsiyarki banza 'kazama kawai."! banji ciwon zagin da yayi min ba saboda na riga na saba, tire din dake gabansa nake kallo a sanyaye nace"Kaine fa kace na had'a maka fruit sal.....Kafin na rufe bakina ya dago tire din ya watso min shi a jiki....gabadaya gaban rigarta da zanina ya 'baci 'kasan gurin da gefan kilishin ya lalace... wayoyinsa ya kwasa yana watsa min kallon banza ya bar gurin....ban dauke idona daga kansa ba har sai da na daina ganinshi....hawayen takaici ne suka shiga zubo min a fuska durkushewa nayi a gurin na dinga kukan da yake nema ya tarwatsa min zuciyata.
*Na kudi ne..*
Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina so ki biya kudin ki ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal #300...0542382124..binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number.
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*GAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
55&56
Samun sa nayi a tsaye a tsakiyar falon yana zagaye koda na shiga gefe guda na samu na tsuguna kaina na sunkuyar k'asa ina addua kada Allah yasa ya tozartani a gabanta dan na fahimci take takensa. bece min komai ba ya zauna kan kujera tare da d'ora kafa daya kan daya zaman yayi kama dana kasaita da nuna isa, ta kasan idona nake kallonsa yana ta girgiza kafa yana latsa waya, haka ta shigo ta same mu, kujera ta nema ta zauna, falon yayi shuru na tsayin minti goma a sace na kallesu shi yana can aikin latsa waya ita kuma alamun tsoro da fargaba na hango a cikin idonta.
kaina na mayar kasa ina jin faduwar gaba, ni da ita duk abu daya ne yake damun mu.
"Lawisa me Sumayya tayi miki da zaki sa Buba ya doke ta ."? A sanyaye tace" Laifi tayi min wanda ya fusata ni shine na yanke mata wannan hukuncin.''
"Ba kwana ki nayi miki magana akan hakan ba."? Yafada yana tsareta da ido, cikin dauriya tace" Naso nayi mata hukunci da kaina tayi min gardama shiyasa na kira buba ya koya mata hankali tunda dai ita bata da mutunci.
Saurin kallonta nayi muka hada ido ta watso min harara, kaina na sunkuyar ina jiran naji abinda zaice.
"Me tayi miki abinda nake son ji kenan."? yafada hankalinsa akan wayarsa.....ajiyar zuciya ta sauke tace" Yau tsayin wata kenan ina aikota ta kawo maka sa'ko ashe zuwa take ta zubar a wani guri daya daga cikin bayina suka sheda min koda na tambayeta ba tayi gardama ba ta tabbatar min da gaskiya ne al'amarin ya 'bata min rai sosai shiyasa na yanke mata wannan hukuncin."
Kallona ya shigayi yana gyada kansa yace."Wato ke ba zaki daina saka kanki a cikin abinda be shafe ki ba ko? shuru nayi yace."Me kike nufi akan abinda kike aikatawa ke kowa baki yarda dashi ba 'yan uwana zarginsu kike yi ke yafi kamata nayi zargi tunda kece bare amma na amince nake tarayya dake ban nuna miki komai ba to ki tashi ki fita ki bani guri bana bukatar sake ganinki a gurina dan na gaji da abinda kike min." kallonsa nake inaso nayi magana ya daga min hannu fuska a murtuke yace "bana bukatar sake ganinki a sashena 'yan uwana nawa ne idan kashe ni sukayi babu abinda ya shafe ki saboda haka tashi fice min daga falo."!
Cikin tsawa da kyara ya kare maganar.
Ji nayi gwiwa ta tayi sanyi ruwan hawaye ya taru a kwarmin idona ni kam wannan wulakanci ina zan kai shi, a sanyaye na mike na nufi kofa zuciyata na wani irin zafi......ina fita hawaye ya wanke min fuska, haruna ya tare ni guri muka samu muka zauna sai da nacu kukana na koshi tukkuna na fada masa yanda mukayi.
Yace." Ki daina kuka kada ki janyowa kanki ciwon kai ni wallahi naji dadi ma da haka ta faru saboda haka yanzu abinda za'ayi shine kije can sashen Fulani ina nufin mahaifiyarsa sai ki sheda mata abinda ke faruwa kin san hausawa nacewa ta inda aka hau tanan ake sauka.
Hanci na shaqa na goge fuskata tare da mikewa tsaye nace" dama dole naje na sanar mata dan saboda kada wani abu ya faru daga baya ta zarge ni da wani abu.
Mikewa yay yace."Muje na raka ki ki fada mata." Tare muka tafi muna sake tattaunar maganar.
Ta jima kafin ta dago kanta ganin b'acin rai a fuskarta yasa na sunkuyar da kaina kasa, tace"Sumayya duk naji maganarki raina kuma ya 'baci da irin wulakancin da babana yake miki yanzu ina laifin mai kula da kai abinda babana yayi miki ya bata min rai sosai kiyi hakuri Sumayya kada kiyi fushi kinji ko zaki cigaba da hidima dashi wallahi da ke kadai naji na aminta, ita kanta yarinyar da zai aura bata kwanta min a rai ba dan dai babu yanda zanyi ne tunda iyaye sun shiga cikin lamarin, zan sameshi zanyi masa fada sosai dole ya mutun taki ko dabbah ai tasan mai kyautata mata bare mutum saboda haka kije yanzu zan kirashi a waya zan zauna dashi zamuyi magana kuma zan nuna masa kuransa.
Daurewa nayi ina kokarin danne damuwata nace"Insha Allahu zanbi umarninki zan cigaba da dawainiya da Yarima kamar yanda kike so." Albarka ta dinga sa min kafin ta bani umarnin tafiya sallama nayi mata na fito
Haruna na tsaye yana jira na ina fitowa na fada masa duk yanda mukayi jikinsa ne naga yayi sanyi yace."Shikkenan Sumayya sai ki sake kiyayewa sannan ki daina yawan saka idonki akan 'yan uwansa tunda baya so ki rabu dashi idan da rabon yasha wuya ne shikkenan."
Shuru nayi kawai ina sauraransa bana jin zan iya zuba ido wani ya cutar dashi amana na daukarwa mahaifiyarsa zanyi iyakacin bakin k'okarina sai dai idan abin yafi karfina
A waya ta kira shi ta rufeshi da fad'a ta inda ta shiga bata nan take fita ba sosai ta nuna masa bacin ranta akan abinda yake yi mamaki ne ya rufeshi ashe yarinyar nan zuwa tayi ta had'ashi da mahaifiyarsa ransa idan yay dubu ya 'baci! tunda yake da mahaifiyarsa wani abu na sa'bani bai ta'ba shiga tsakaninsu ba sai ta dalilin yarinyar.....Girgiza kansa yayi ya shiga bata hakuri tace"Haba babana ai dole raina ya 'baci akan abinda kakeyi yarinyar nan kullum na dawainiya da kai amma kullum cikin cizguna mata kakeyi su 'yan uwan naka da kake fifitasu a kanta ba kaunarka sukeyi ba har yanzu ka kasa ganewa cewar kullum farautarka suke to mutukar kana kaunar farin cikina ka mutunta Sumayya bana san cin zarafin da kake mata ka sanja hali."
Ajiyar zuciya ya sauke yace."Mamma naji na d'auki laifina insha Allah zan gyara na daina bana san kina fushi da 'bacin rai akan abinda bai kai ya kawo ba."
"Babana idan ka naso na daina bacin rai sai ka daina abubuwan da kake na rashin kyautawa tukkuna." Hannuwanta ya ri'ke yace."Insha Allahu na daina yarinyar ta dawo ta cigaba da aikinta shikkenan ko."? Ajiyar zuciya ta sauke tace"Shikkenan magana ai ta wuce na bata hakuri sosai anjima da daddare zata shigo ta baka abinci kaima sai ka nemi afuwarta dan Allah yana san haka.
Da mamaki a fuskarsa yake kallonta har abadah baya tsammanin zai iya bawa yarinyar hakuri akan wani laifi da yayi mata kawai dai ya amsa mata ne domin ta kwantar da hankalinta ta kuma daina 'bacin rai akan al'amarin.
To koda na koma gurin mu ban yarda na fadawa iyayena abinda ya faru ba kawai nace musu nayi mata wani aiki ne...Tambaya tace"Muna nan muna tattaunawa akan maganarki da Haruna dan gidan Labaran bayan fitarki yazo gurin babanki suka tattauna ashe dama soyayya ce a tsakaninku mu bamu sani ba."
Kunyace ta rufe ni nayi yar dariya ina kokarin shiga daki nace "Tambaya kenan." Babana dake zaune kan darduma yana murmushin farin ciki yace."Sumayya a gaskiya nayi farin ciki da wannan al'amari sosai na yaba da tarbiyar Haruna yana da nutsuwa da kintsi nayi imanin zai rike min ke da mutunci wannan dalilin yasa na amince da maganar amma na cewa mahaifin nasa sai na zauna dake kin sake tabbatar min da bakin ki.
Shuru nayi ina wasa da hannuwana, yace."Sumayya babu kunya a tsakanina dake ni mahaifin ki ki fada min shin kina son Haruna ko aa."
Murmushi nayi nace"Eh baba ina sonsa ina rokon Allah yasa shi din alkairi ne a tare dani." cike da farin ciki ya amsa da ameeen Sumayya ubangiji Allah ya tabbatar mana da alkairi Allah yasa damu za'ayi."