Sashe 5
Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah)
11&12
Tun bayan fitar su Satima daga 'bangaransa yake zaune shi kadai a guri guda ya gaza ta'buka komai kallon kasan d'akin kawai yake yana mamakin abinda ke faruwa a masarautar a lokacin da ya tafi karatu yana da kuruciya shiyasa baya saurin gane wasu abubuwan amma yanzu shigarsa sauran 'bangarorin gidan domin gaisawa dasu ya fahimci cewar har yanzu bata sauya zani ba a tsakanin iyalan mutane uku da suke da muhimmacin a masarauta ba'a ga maciji kowanne da akwai mugun abu a zuciyarsa dangane da d'an uwansa, Lokacin da suka shiga bangaran mai babban daki gabad'aya sun hallara a falo ita da 'ya'yanta sun kewaye ta babu wanda yasan abinda suke qullawa sai Allah.......Ganin shigowarsu ne yasa suka daidata nutsuwarsu suna masa barka da zuwa dukkaninsu sai ya'ke sukeyi da kokarin nuna masa kulawa, shi ba yaro bane ballantana ya kasa gane yanayin fuskokinsu dan wasu daga cikinsu sai satar kallonsa suke ta'kasan ido, dalilin daya sa kenan ya kasa zama ya miqe da niyyar tafiya........Uwargida na fara'a kamar gaske tace"Magajin Sarki ka tsaya kaci abincin ma tun safe 'Yan uwanka suka baro gidajan mazajensu suka yini suna shirya maka abun tar'ba."
Ba tare da ya kalleta ba yace."Nagode Gwaggo ina ganin za'a iya kai min abincin sashena idan na samu nutsuwa sai na zauna naci." Ta washe bakinta cike da jin dadi tace"To shikkenan yanzu zansa a kai maka kamar yanda ka bukata."
A nutse ya juya domin yiwa 'yan uwan nasa godiya sai kawai yaga sunyi masa caaa! da ido da sauri ya sunkuyar da kansa yana mamakin kallon da suke masa tamkar basu taba ganinsa ba, babu cikakkiyar walwala a maganarsa yace." My Aunt's ina godiya da hidima." Da farin ciki a fuskokinsu suka shiga amsawa, rufaffun takalmasa yasa ya fita daga falon, a tsaye a samu su Shatima na jiransa ya fito, kai tsaye suka wuce side din Baba Waziri nan ya samu cikakkiyar karba da kulawa gurin matayensa kamar yanda yake tsammani cike da jin kaunarsu yay musu sallama, Bangaran Ciroma da Galadima kuwa bai samu wata cikakkiyar kulawa ba dan kafatanin su adawa suke dashi Shatima da Moddibo ne kawai suke d'an nuna masa kauna da kulawa suma d'in Allah ne kad'ai yasan abinda ke zuciyarsu.......Wannan dalilin ne yasa tunda ya zauna yake tunanin al'amarin a rayuwarsa ya tsani rabuwar kai da lalacewar zumunci! ya fahimci suna masa hassada sosai saboda mahaifinsa ne ke kan mulki dukkaninsu suna zargin kamar shine zai maye gurbin mahaifinsa bayan Allah ya dauki ransa wanda shi kuma basu san mulki da wani abinda ya shafeshi baya daga cikin tsarin rayuwarsa, a wannan zamanin jan ragamar al'umma na da wahala mutuka shiyasa gabadaya baya da ra'ayi maye gurbin mahaifinsa.
Ya jima zaune a gefen katafaran gadonsa daya sha shimfid'u na alfarma irin na saurata kafin ya miqe a nutse ya nufi toilet din wanda shi kansa abin kallo ne duk abinda mutum ke bukata a kwai a cikin toilet d'in, tsaf yayi wanka ya fito daure da towel a k'ugunsa, a bakin k'ofa ya samu wani bawa hannunsa ringume da kayan sawa irin na sarauta.
Gefan gado ya samu ya zauna ba tare da yace komai ba, bawan ya karaso tare da durkusawa a gabanshi yace."Ranka ya dade ni sunana Haruna ni zan dinga yi maka hidima da duk abinda kake bukata na shigo naji kana wanka sai na dau'ko maka tufafin da suka dace.''
A nutse ya d'ago kansa yana kallon kayan dake hannun bawan, manyan kaya ne irin na saurata har da nad'i da katuwar alkyabba sam ba zai iya sanya kayan nauyi a jikinsa ba.
Girgiza masa kansa yayi a nutse yace."Mayar da wa'innan kayan ka dauko min masu sauki." Da saurin ya miqe da kayan a hannunsa ya bud'e shirgegiyar wardorobe din dake kafe a bangon dakin ya ajiye kayan tare da nemo masa irin kayan da yake bukata......Farin yadi filtex mai taushin gaske ya dauko mashi ya jiye kusa dashi kana ya sake komawa wardorbe din ya dauko wani dan madaidaicin akwati shima yazo ya ajiye masa a kusa dashi........Wata iriyar hula naga ya dauko mai tafe da takalminta yazo ya tsuguna tare da cire ledar data lullube hular da takalmin ya d'ora kan kayan ya miqe tsaye da sauri tare da matsawa gefe guda kansa a kasa yace."Ranka ya dad'e na dauko maka dukkanin abin bukata ka duba ka gani idan da akwai wani abinda kake bukata.
Gefan da kayan suke a ajiye ya duba minti biyu yana kallon gurin kafin yace."Jeka nagode." Da sauri ya sunkuyar da kansa kasa gami da fadin"Godiya nake Magajin sarki." yana gama maganarsa ya bude kofar dakin ya fita da saurin gaske........A nutse ya miqe ya nufi gaban mirror din dake cike da kayan shafe shafe da turaruka na mussaman irin na masu sarauta, Cream kawai ya shafa a jikinsa ya shafawa jikinsa turare mai kamshi, kana ya bar gurin, tsaf ya shirya jikinsa cikin farin yadin wanda akayi masa d'inki mai yankakken hannu irin na zaman gida gaban rigar da bayanta anyi aiki da farin zare wanda yake nuni da tambarin masarautar, a nutse ya bude akwatin nan naga tarin agoguna da manya manyan zubonan azurfa kala kala sai sheqi sukeyi, agogo mai sarqa yasa a hannunshi na dama kana ya zura wasu zubonan azurfa a tsayunsa guda biyu na hagu da dama, zubonan suyi masa kyau sosai da sosai. ya mayar da a kwatin ya rufe ya dauki hular yana gyarata hula ce aka d'inkata da wani irin yadi mafi akasari ma masu saurata suke amfani da ita tsayin hular ne ya bashi dariya ya dinga duba hular yana tunanin ajiyeta ya bar kansa a haka sai dai yayi dubarar lankafe saman ta ya rage mata tsayi yasa a kansa kana ya zura takalman dake gabanshi masu kalar hular .....Gaban mirror ya tsaya yana sake duba kansa, murmushi ya dinga yi yana shafa siririn sajen fuskarsa lallai malam bahaushe yayi gaskiya da yake fad'in kowa ya bar gida to gida ya barshi, yaushe rabonsa da sanya manyan kaya a jikinsa, sai yaga shi kansa ya k'arayiwa kansa kyau da kwarjini wannan zungureriyar hular da yake wa dariya yaga tayi masa kyau sosai ta sake fito masa da kewayayyar fuskarsa mai dauke da k'ayataccen sajensa, ajiyar zuciya ya sauke a nutse ya bar gurin mirror kai tsaye hanyar fita daga dakin ya nufa...........Yana fitowa Haruna dake tsaye kamar gunki a kofar dakin yayi kasa da kansa tare da fadin"Barka da fitowa." Ba tare da yace masa komai ba ya wuce cikin falon.....Nan ya ganta a hakimce a kan kujera k'afarta d'aya kan 'daya tana sakar masa kyakkyawan murmushi...........Idonsa a tsaye a kanta ya samu guri ya zauna cikin d'aya daga cikin k'ayattatun kujerun dake kewaye da falon Wani irin zama yayi irin na masu mulki yasa mata idonsa yana kallo fuskarsa babu d'igon annuri.
Gimbiya Lawisa cikin iyayi da iyawa ta ma'kale murya tare da fadin "Barka da fitowa magajin sarki inayi maka barka da dawowa masarauta lafiya."
falon shuru yayi bayan gama maganarta tana jiran amsarsa taji shuru bece komai ba, dago kai tayi tana kallonsa taga yana ta kallon jikinta.......Yarima Ali na da muguwar d'abi'ar san mata dan ko acan amurukan ma shagalinsa ya sha da matan turawa da bakaken fata amma duk kulafucinsa bai ta'ba zina ba sai dai romancing nan yake biyawa kansa bukata, yana da bala'in san mata masu kyau da k'irar jiki, Gimbiya Lawisa nada kyau da lafiyayyan jiki shiyasa ya gaza dauke idonsa daga kanta sha'awarta ce ta d'arsu a zuciyarsa. Ganin tana kallonsa tana murmushi yasa yayi gyaran murya da kyar yace."Daga wane 'bangare kike.''? 'Yar dariya tayi tana kallonsa tace"Yanzu dan Allah baka gane ni ba ? nice fa Lawisa ta gurin Baba Ciroma 'kanwar Moddibo."'
Sajensa ya shafa har yanzu babu fara'a a fuskarsa yace."Ya za'ayi na gane ki bayan rabona daku sama da shekara goma lokacin dana bar gida ina tsammanin baki kai shekaru bakwai a duniya ba."
Tace"Eh hakane kam shekaruna takwas a lokacin daka tafi karatu amma kuma ni kaga ban mance da kai ba."! Shuru yay yana kallonta, Ta cigaba da cewa"Wannan dalilin ne yasa ma na shirya gagarimar walima domin taya ka murnar dawowa gida lafiya.'' Murmushi yayi yana kallonta yace."Nagode 'Kanwata inaso naga ana nuna kulawa akaina nayi farin ciki sosai da wannan karamcin yaushe ne kika tsayar da taron.
Cikin farin ciki da jin dadi tace"Naji dadi sosai daka kar'bi magana ta da mahimanci nagode sosai sannan kuma ranar jumaa ne ranar dana tsayar domin taron walimar." Da ragowar murmushi a fuskarsa yace."To shikkenan Allah ya kaimu ranar lafiya."
Falon yayi shuru Lawisa sai sa'ke-sa'ke take a cikin ranta tana tunanin ko kawai ta fad'a masa tana sonsa tunda taga nan da nan ya kar'bi maganar da ta kawo masa da muhimanci.....tana kokarin tayi magana......Aunty Safiyya d'aya daga cikin yayyunsa ta shigo falon bayanta wasu bayi ne mata guda biyu suna dauke da tire din abinci kai tsaye can gurin daining suka..........Aunty Safiyya ganin Lawisa a zaune tana murmushi yasa tayi saurin kallonta ta kalli 'kanin nata sai kawai taji farin cikin ganinsu a tare lallai babu shakka Lawisa zata taimaka musu gurin ganin bukatarsu ta biya a kansa.....Cike da farin ciki gami da nuna jin dad'i tace"A'a k'anina soyayya akeyi ne.'' Kansa ya sunkuyar qasa bece uffan ba.
Ita kuwa Lawisa sai murmushi takeyi na jin dadi tana kallon aunty Saffiyan tana sunkuyar da kanta.
Kusa dashi taje ta zauna kamar gaske ta dafa kafad'arsa da fadin'' A gaskiya nayi farin cikin ganin ku a tare dama babban burinmu a yanzu kayi aure ka sake zama babban mutum to alhamdullilahi tunda ma 'yar gida za'ayi towo na mai na ne abun yayi dad'i nasan kuma iyayenmu zasuyi farin ciki mutuka, kuma inaso na tabbatar maka da cewar kayi sa'ar matar aure domin dai Lawisa babu abinda ta nema ta rasa na bangaran kyawun hali ga uwa uba kyawun sura."
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah)
11&12
Tun bayan fitar su Satima daga 'bangaransa yake zaune shi kadai a guri guda ya gaza ta'buka komai kallon kasan d'akin kawai yake yana mamakin abinda ke faruwa a masarautar a lokacin da ya tafi karatu yana da kuruciya shiyasa baya saurin gane wasu abubuwan amma yanzu shigarsa sauran 'bangarorin gidan domin gaisawa dasu ya fahimci cewar har yanzu bata sauya zani ba a tsakanin iyalan mutane uku da suke da muhimmacin a masarauta ba'a ga maciji kowanne da akwai mugun abu a zuciyarsa dangane da d'an uwansa, Lokacin da suka shiga bangaran mai babban daki gabad'aya sun hallara a falo ita da 'ya'yanta sun kewaye ta babu wanda yasan abinda suke qullawa sai Allah.......Ganin shigowarsu ne yasa suka daidata nutsuwarsu suna masa barka da zuwa dukkaninsu sai ya'ke sukeyi da kokarin nuna masa kulawa, shi ba yaro bane ballantana ya kasa gane yanayin fuskokinsu dan wasu daga cikinsu sai satar kallonsa suke ta'kasan ido, dalilin daya sa kenan ya kasa zama ya miqe da niyyar tafiya........Uwargida na fara'a kamar gaske tace"Magajin Sarki ka tsaya kaci abincin ma tun safe 'Yan uwanka suka baro gidajan mazajensu suka yini suna shirya maka abun tar'ba."
Ba tare da ya kalleta ba yace."Nagode Gwaggo ina ganin za'a iya kai min abincin sashena idan na samu nutsuwa sai na zauna naci." Ta washe bakinta cike da jin dadi tace"To shikkenan yanzu zansa a kai maka kamar yanda ka bukata."
A nutse ya juya domin yiwa 'yan uwan nasa godiya sai kawai yaga sunyi masa caaa! da ido da sauri ya sunkuyar da kansa yana mamakin kallon da suke masa tamkar basu taba ganinsa ba, babu cikakkiyar walwala a maganarsa yace." My Aunt's ina godiya da hidima." Da farin ciki a fuskokinsu suka shiga amsawa, rufaffun takalmasa yasa ya fita daga falon, a tsaye a samu su Shatima na jiransa ya fito, kai tsaye suka wuce side din Baba Waziri nan ya samu cikakkiyar karba da kulawa gurin matayensa kamar yanda yake tsammani cike da jin kaunarsu yay musu sallama, Bangaran Ciroma da Galadima kuwa bai samu wata cikakkiyar kulawa ba dan kafatanin su adawa suke dashi Shatima da Moddibo ne kawai suke d'an nuna masa kauna da kulawa suma d'in Allah ne kad'ai yasan abinda ke zuciyarsu.......Wannan dalilin ne yasa tunda ya zauna yake tunanin al'amarin a rayuwarsa ya tsani rabuwar kai da lalacewar zumunci! ya fahimci suna masa hassada sosai saboda mahaifinsa ne ke kan mulki dukkaninsu suna zargin kamar shine zai maye gurbin mahaifinsa bayan Allah ya dauki ransa wanda shi kuma basu san mulki da wani abinda ya shafeshi baya daga cikin tsarin rayuwarsa, a wannan zamanin jan ragamar al'umma na da wahala mutuka shiyasa gabadaya baya da ra'ayi maye gurbin mahaifinsa.
Ya jima zaune a gefen katafaran gadonsa daya sha shimfid'u na alfarma irin na saurata kafin ya miqe a nutse ya nufi toilet din wanda shi kansa abin kallo ne duk abinda mutum ke bukata a kwai a cikin toilet d'in, tsaf yayi wanka ya fito daure da towel a k'ugunsa, a bakin k'ofa ya samu wani bawa hannunsa ringume da kayan sawa irin na sarauta.
Gefan gado ya samu ya zauna ba tare da yace komai ba, bawan ya karaso tare da durkusawa a gabanshi yace."Ranka ya dade ni sunana Haruna ni zan dinga yi maka hidima da duk abinda kake bukata na shigo naji kana wanka sai na dau'ko maka tufafin da suka dace.''
A nutse ya d'ago kansa yana kallon kayan dake hannun bawan, manyan kaya ne irin na saurata har da nad'i da katuwar alkyabba sam ba zai iya sanya kayan nauyi a jikinsa ba.
Girgiza masa kansa yayi a nutse yace."Mayar da wa'innan kayan ka dauko min masu sauki." Da saurin ya miqe da kayan a hannunsa ya bud'e shirgegiyar wardorobe din dake kafe a bangon dakin ya ajiye kayan tare da nemo masa irin kayan da yake bukata......Farin yadi filtex mai taushin gaske ya dauko mashi ya jiye kusa dashi kana ya sake komawa wardorbe din ya dauko wani dan madaidaicin akwati shima yazo ya ajiye masa a kusa dashi........Wata iriyar hula naga ya dauko mai tafe da takalminta yazo ya tsuguna tare da cire ledar data lullube hular da takalmin ya d'ora kan kayan ya miqe tsaye da sauri tare da matsawa gefe guda kansa a kasa yace."Ranka ya dad'e na dauko maka dukkanin abin bukata ka duba ka gani idan da akwai wani abinda kake bukata.
Gefan da kayan suke a ajiye ya duba minti biyu yana kallon gurin kafin yace."Jeka nagode." Da sauri ya sunkuyar da kansa kasa gami da fadin"Godiya nake Magajin sarki." yana gama maganarsa ya bude kofar dakin ya fita da saurin gaske........A nutse ya miqe ya nufi gaban mirror din dake cike da kayan shafe shafe da turaruka na mussaman irin na masu sarauta, Cream kawai ya shafa a jikinsa ya shafawa jikinsa turare mai kamshi, kana ya bar gurin, tsaf ya shirya jikinsa cikin farin yadin wanda akayi masa d'inki mai yankakken hannu irin na zaman gida gaban rigar da bayanta anyi aiki da farin zare wanda yake nuni da tambarin masarautar, a nutse ya bude akwatin nan naga tarin agoguna da manya manyan zubonan azurfa kala kala sai sheqi sukeyi, agogo mai sarqa yasa a hannunshi na dama kana ya zura wasu zubonan azurfa a tsayunsa guda biyu na hagu da dama, zubonan suyi masa kyau sosai da sosai. ya mayar da a kwatin ya rufe ya dauki hular yana gyarata hula ce aka d'inkata da wani irin yadi mafi akasari ma masu saurata suke amfani da ita tsayin hular ne ya bashi dariya ya dinga duba hular yana tunanin ajiyeta ya bar kansa a haka sai dai yayi dubarar lankafe saman ta ya rage mata tsayi yasa a kansa kana ya zura takalman dake gabanshi masu kalar hular .....Gaban mirror ya tsaya yana sake duba kansa, murmushi ya dinga yi yana shafa siririn sajen fuskarsa lallai malam bahaushe yayi gaskiya da yake fad'in kowa ya bar gida to gida ya barshi, yaushe rabonsa da sanya manyan kaya a jikinsa, sai yaga shi kansa ya k'arayiwa kansa kyau da kwarjini wannan zungureriyar hular da yake wa dariya yaga tayi masa kyau sosai ta sake fito masa da kewayayyar fuskarsa mai dauke da k'ayataccen sajensa, ajiyar zuciya ya sauke a nutse ya bar gurin mirror kai tsaye hanyar fita daga dakin ya nufa...........Yana fitowa Haruna dake tsaye kamar gunki a kofar dakin yayi kasa da kansa tare da fadin"Barka da fitowa." Ba tare da yace masa komai ba ya wuce cikin falon.....Nan ya ganta a hakimce a kan kujera k'afarta d'aya kan 'daya tana sakar masa kyakkyawan murmushi...........Idonsa a tsaye a kanta ya samu guri ya zauna cikin d'aya daga cikin k'ayattatun kujerun dake kewaye da falon Wani irin zama yayi irin na masu mulki yasa mata idonsa yana kallo fuskarsa babu d'igon annuri.
Gimbiya Lawisa cikin iyayi da iyawa ta ma'kale murya tare da fadin "Barka da fitowa magajin sarki inayi maka barka da dawowa masarauta lafiya."
falon shuru yayi bayan gama maganarta tana jiran amsarsa taji shuru bece komai ba, dago kai tayi tana kallonsa taga yana ta kallon jikinta.......Yarima Ali na da muguwar d'abi'ar san mata dan ko acan amurukan ma shagalinsa ya sha da matan turawa da bakaken fata amma duk kulafucinsa bai ta'ba zina ba sai dai romancing nan yake biyawa kansa bukata, yana da bala'in san mata masu kyau da k'irar jiki, Gimbiya Lawisa nada kyau da lafiyayyan jiki shiyasa ya gaza dauke idonsa daga kanta sha'awarta ce ta d'arsu a zuciyarsa. Ganin tana kallonsa tana murmushi yasa yayi gyaran murya da kyar yace."Daga wane 'bangare kike.''? 'Yar dariya tayi tana kallonsa tace"Yanzu dan Allah baka gane ni ba ? nice fa Lawisa ta gurin Baba Ciroma 'kanwar Moddibo."'
Sajensa ya shafa har yanzu babu fara'a a fuskarsa yace."Ya za'ayi na gane ki bayan rabona daku sama da shekara goma lokacin dana bar gida ina tsammanin baki kai shekaru bakwai a duniya ba."
Tace"Eh hakane kam shekaruna takwas a lokacin daka tafi karatu amma kuma ni kaga ban mance da kai ba."! Shuru yay yana kallonta, Ta cigaba da cewa"Wannan dalilin ne yasa ma na shirya gagarimar walima domin taya ka murnar dawowa gida lafiya.'' Murmushi yayi yana kallonta yace."Nagode 'Kanwata inaso naga ana nuna kulawa akaina nayi farin ciki sosai da wannan karamcin yaushe ne kika tsayar da taron.
Cikin farin ciki da jin dadi tace"Naji dadi sosai daka kar'bi magana ta da mahimanci nagode sosai sannan kuma ranar jumaa ne ranar dana tsayar domin taron walimar." Da ragowar murmushi a fuskarsa yace."To shikkenan Allah ya kaimu ranar lafiya."
Falon yayi shuru Lawisa sai sa'ke-sa'ke take a cikin ranta tana tunanin ko kawai ta fad'a masa tana sonsa tunda taga nan da nan ya kar'bi maganar da ta kawo masa da muhimanci.....tana kokarin tayi magana......Aunty Safiyya d'aya daga cikin yayyunsa ta shigo falon bayanta wasu bayi ne mata guda biyu suna dauke da tire din abinci kai tsaye can gurin daining suka..........Aunty Safiyya ganin Lawisa a zaune tana murmushi yasa tayi saurin kallonta ta kalli 'kanin nata sai kawai taji farin cikin ganinsu a tare lallai babu shakka Lawisa zata taimaka musu gurin ganin bukatarsu ta biya a kansa.....Cike da farin ciki gami da nuna jin dad'i tace"A'a k'anina soyayya akeyi ne.'' Kansa ya sunkuyar qasa bece uffan ba.
Ita kuwa Lawisa sai murmushi takeyi na jin dadi tana kallon aunty Saffiyan tana sunkuyar da kanta.
Kusa dashi taje ta zauna kamar gaske ta dafa kafad'arsa da fadin'' A gaskiya nayi farin cikin ganin ku a tare dama babban burinmu a yanzu kayi aure ka sake zama babban mutum to alhamdullilahi tunda ma 'yar gida za'ayi towo na mai na ne abun yayi dad'i nasan kuma iyayenmu zasuyi farin ciki mutuka, kuma inaso na tabbatar maka da cewar kayi sa'ar matar aure domin dai Lawisa babu abinda ta nema ta rasa na bangaran kyawun hali ga uwa uba kyawun sura."