← Book details Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 90

Sashe 7

Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

****
Cikin saurin na fito daga gurin mu domin zuwa duba dawakan da babana ke hidimarsu tun safe dana zuba musu abinci ban sake zuwa duba su ba saboda yini mukayi wankin kayanmu nida mahaifiyata wannan dalilin ne yasa ban je gurin da wuri ba............Ina daf da shiga kofar dawakan na hangeta ita da masu take mata baya, sanin halinta naso a girmamata yasa na sunkuyar da kaina qasa har suka karaso gurin nace" Barka da yamma ranki shi dad'e." banza tayi min bata amsa ba sai hararata take ni kam ban san me yasa ta tsaneni ba tsakanina da ita harara ne da kallon banza. Ganin taki amsawa yasa da sauri nayi nufin shiga kofar......Naji ta daka min tsawa da fad'in "Ke! mahaukaciya dawo ki tsaya a inda kike ko nace ki tafi ne."? Cike da mamaki nake kallonta kafin nace" Ranki ya dad'e na gaishe ki kin'ki amsawa me kike so nayi miki a yanzu ina da uziri zan zubawa dawakai abinci."
Kallona naga tanayi tana girgiza kanta, ni kaina sai da na gama maganar nazo ina nadama sabida nasan na tarowa kaina jaraba, ni haka nake bana barin magana a cikina idan mutum ya gaya min biyar sai na fada masa goma gashi bani da tsoro ko kad'an cikin dubbanin mutane aka ajiye ni zan iya kwatar kaina saboda ina da baki.

Inda nake tazo ta tsaya tana yi min wani irin kallon raini! kafin na ankara naji yawun bakinta a fuskata, da sauri na dago kaina ina kallonta........Tana wani irin huci! tace"Yanzu Sumayya a matsayinki na makaskanciyar baiwa a gidan nan har kina da damar tsallake umarnina nace miki ga abinda nake bukata kice kina da uziri."?

Hannu nasa na goge yawun data tofa min nace"Ranki ya dade ki gafarce iya bakin kokarina nayi miki na baki girmanki na risina na gaishe shin to dan Allah dan annabi me kike so nayi miki ."
Mari! ta kwad'a min a kumatuna kafin na dawo daidai ta sake waska min wani a d'aya gefan! Ido jawur nake kallonta ina jin tamkar nima na fitar da hannu na rama! marin......hannu ta daga kawai tana nuna ni tsabar b'acin ran dana kuntunka mata ya hanata magana, a rayuwar Gimbiya Lawisa tun tasowarta a gidan sarautar babu wanda ya ta'ba yi mata gardama akan umarninta sai Sumayya......Juyawa nayi zan shiga kofar dawakai ta janyo faffad'an wuyan rigata aikuwa a take rigar ta yage da yake rigar ta yadi ce mai dogon hannu zanin kuma na shadda kamfala shine uniform din mu a cikin gidan mata zani maza wando amma dai duk ranar jumaa muna sanya tufafi masu kyau domin girmama ranar haka ma ranar sallar 'karama da babba sarki nayi mana d'inkuna na atamfofi muyi ado domin murna da zuwan ranar.........Hannu nasa da sauri na dafe wuyan rigar ganin yana kokarin sab'ulewa. Tsira mata ido nayi rai a 'bace! nace tsirara zakiyi min ne? kada fa ki manta kema macace idan kinyi min tsirara a idanun jama'a kamar kin tonawa kanki asiri ne."
Wani marin ta sake bani tana huci! ni kuma mirmushin takaici nayi hannuna dafe da kuncina ina kallon ikon Allah........Jama'a ne suka taru a gurin sai bata hakuri suke harda masu durkusa mata, Buba ta kalla dake riqe da shar'be'biyar bulala tace"Bani bulalar nan." Da sauri ya mika mata yana fadin "Tuba take ranki ya d'ad'e."........Ganin ta d'aga bulalar zata shaud'a min yasa nayi saurin fizgewa na nannad'eta a hannuna sai kawai muka tsirawa juna ido nida ita jama'ar dake gurin da ita kanta mamakin karfin halina suke.........Ta girgiza kanta tana kallon Buba tace" Inaso ka samo igiya mai kauri ka daure mata hannuwa da kafafu yau nayi al'kawarin sai naga karshen taurin kanki."..............Kallonta kawai nake tsabar takaici da bakin ciki yasa nake jin kamar na zazzabga mata bulalar dake hannuna, ina kallon Buba ya tawo da murtukekiyar igiya gabana ya yanke ya fad'i ganin ya nufo inda nake....................yasa na juya baya ina neman mafaka babu dan duk ko ina mutane ne sun kewaye mu, tsugunawa nayi a kusurwa hawaye ya kwace min, Buba babu tausayi yazo ya shiga kici kicin daure min hannuwa da kafafuna sai tirje tirje nake ina haurinsa amma sai da ya samu nasarar daure ni tamau! gwiwowina a kasa kaina a sunkuye na soma jin saukar bulala a gadon bayana.......tsabar taurin kaina yasa na kasa motsi ina dai jin radad'in bulalar na ratsa min jiki amma saboda na nuna mata a banza takeyi yasa na daure.........Gimbiya Lawisa sai da jikinta yay sanyi ganin ko gezau na 'kiyi ballanatana na nuna mata ina jin zafin bulalar, tunani tayi ko itace ba ta iya bulalar ba rai a 'bace tace"Buba zo kayi mata ka tabbatar da cewa ta ratsa jikinta shegiya basamudiya yanda take da wannan gansameman jikin dama ai duka ba zai ratsa ta ba." Gefe ta koma tana haki! dan ba karamin galabaita tayi ba.'' Buba cike da bin umarni ya daga bulalar zai shaud'a mata, muryarsa ta katse masa hanzari.....Kafatanin jama'ar dake gurin suka juya suna kallonsa ganin ya nufo gurin ne yasa kowa yayi k'asa da kansa har ita Lawisan sunkuyar da kanta tayi......Cikin nutsuwa ya 'karaso gurin aka bud'a masa hanya ya shiga har inda nake durkushe! ta 'kasan idona nake kallonsa yana tsaye hannuwansa duk biyun a baya sai kalle kalle yake a gurin kafin naga ya kalleta babu fara'a a tare dashi yace."Yace."Meke faruwa ina zaune Haruna ke sheda min ga jama'a sun taru kuma kina gurin saboda haka inaso nasan abinda ke faruwa."
*BINTA UMAR ABBALE*

Shearing👏🏻
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALE🍒_ *[email protected]*

*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊�*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_
*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊�)

17&18
Tana kishingid'e a killace a guri guda da cazbaha a hannunta tana lazimi yau ita kadai ce a zaune a falon babu hadimai a kusa da ita ta bukaci zama ita kad'ai ne domin ta kad'aita kanta da mahallicinta shine da dalilin da yasa ta sallami bayin dake kusa da ita.

Tunda ya shigo take sakin murmushi idanunta a kansa har ya k'asara kan kilishin da take kishingide zaman raquma yay a gabanta tare da sunkuyar da kansa cikin tsantsar ladabi yace."Mamma barka da yamma." hannunta guda ta dora a saman kanshi tana shafawa gyaran murya tayi tana nuna masa cewar akwai abunda takeyi....Kansa ya dago yana kallonta sai ta nuna masa carbin dake hannunta tana murmushi had'e dayi masa nuni dacewar ya jira ta kammala.

Murmushi yay a nutse yasa hannu kan tire din dake gabanta wanda ke cike da kayan marmari.. tufa(apple) ya d'auka yasa a bakinsa ya gutsira yana sake gyara zamansa a gurin.

Kallonsa take tana murmushi mai ma'ana wanda kai kana ganin yanayin fuskarta zaka gane cewar tana cikin farin ciki kuma akwai soyayya da shaquwa mai yawa a tsakaninta da yaron nata.

Magajin sarki sai da ya cinye tufa(apple) uku tukkuna ta kammala lazimin a nutse tace"Babana barka da yamma." Ya dago kansa da sauri yace."Mammah barka dai ina fatan kin wuni cikin koshin lafiya." Yafadi maganar a sanda yake kokarin riko hannuwanta.

Tace."Lafiya lau na wuni ina fatan baka da matsala dan tun safe nake jiran shigowarka yau ba kayi shigowar safe ba ina fatan lafiya."

Zamansa ya gyara har yanzu kuma hannuwansa na rike da nata yace."Wallahi Mammah yau bacci na yini ina yi sai gefin la'asar na tashi nayi wanka wannan shine dalilin da yasa ban shigo mun gaisa ba."

Ajiyar zuciya ta sauke tace"To alhamdulillahi tunda lafiyarka lau dama akwai muhimiyyar maganar da nake so mu tattauna da kai."

Ya sake gyara zamansa cikin kulawa yace."Ina sauraran maganar Mammah." Da farin ciki ta tare da ita tace"Ashe bayan dawowarka gida kun shirya tsakaninku kai da Lawisa 'yar gurin Kawun ka Ciroma d'azu da safe maimartaba yake sheda min yanda al'amura suka kasance hakika naji dadi sosai daka za'bi matar aure acikin dangi ina ganin hakan sai yafi mana kwanciyar hankali da kai baki daya."

Shiru yayi kansa a kasa ya rasa abinda zaice. ashe sai da aunt Safiyya taje ta fad'i maganar wallahi shi ya dauka da wasa takeyi! tunda yake bai ta'ba sha'awar auran zumunci ba saboda gudun lalacewarsa yafi so ya fita waje yaje can ya auro saboda baya so ya auri 'yar dangi zumunci ya sake lalacewa dama a lalace yake shiyasa kwata-kwata baiyi na'am da maganar ba ashe sai da taje ta fadi maganar.

Fulani ganin yayi shuru tace."Babana ko akwai matsala ne? naga kayi shuru kana tunani kayi min bayani dan ba naso ayi al'amarin nan rayuka su 'baci idan ba kai ke son al'amarin ba to tun kafin tafiya tayi nisa a warwareshi."

Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke ya kalleta yana kokarin 'boye damuwar dake fuskarsa yace."Mammah ba wani abu bane yasa kika nayi shuru ina tunanin abinda aunty Safiyya ta aikata bayan nayi mata bayani cewar babu wata alaqa ta soyayya a tsakanina da Lawisa kawai tazo ta ganta ne a ranar dana dawo tazo tana sheda min cewa ta shirya walima domin murnar dawowata gida lafiya to ita kuma aunt Safiyyan shine take tunanin soyayya ce a tsakanina da ita.

Fulani shuru tayi tana mamakin al'amarin ta kalleshi a nutse tace"To yanzu wace shawara ka yanke dan gaskiya al'amarin yayiwa Maimartaba dadi bashi kadai ba har sauran 'yan uwansa sunyi farin ciki nima kuma naji dadin hakan idan kace ka janye maganar baza suji dadi ba.

Murmushi yay wanda ya tsaya iya le'bansa yace."Mammah bana fatan ranar da zata zo na 'bata muku rai dake da maimartaba tunda dai maganar nan ta fita har iyaye sunji to ina ganin babu damuwa zan auri yarinyar amma a gaba dole na 'kara aure mutukar Allah ya had'ani da wacce nake so."
Chapter 7 · 0% Book details