Sashe 36
Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tace"Kuma naga baki je sashen Yarima ba Allah yasa dai lafiya."Nace."Lafiya lau sai an dan jima zanje." Fita tayi daga dakin tana fadin"To ai sai kiyi maza kizo kiyi wankan kafin lokacin Walimar yayi kinje kin gama abinda zakiyi.
Mi'kewa nayi ina kokarin cire rigata gefe guda kuma ina mamakin yanda tambaya ta damu da dole sai nayi wanka na shirya nida zan samu yanda nake so wallahi ba zan fita ba balantana na ganshi gabad'aya ya fice min daga raina tausayinsa ma na daina ji sabida irin rashin kyautawar da yayi min jiya.
Daya daga cikin tamfofin da Fulani keyi min kyautarsu na dauko wata super mai ruwan ganye nasa a jikina, nayi mamaki sosai da dinkin ya zauna a jikina tamkar an auna ni.
Murmushi nayi a sanda na kalli mudubi naga yanda nayi kyau Atamfar ta haska ni
Zama nayi domin na gyara fuskata babana ne ya shigo fuskarsa cike da walwala da farin ciki yace."Yawwa Sumayya ki shirya sosai ga 'yan uwanki can kowacce tayi ado inaso ki zama tauraruwa a cikinsu.' cikin tsokana yake maganar
Dariya nasa nace"Baba kenan ashe kana so nayi kyau nafi kowa ko."? da mirmushi a fuskarsa yace."Eh mana ai kowa nasa ya sani." murmushi nayi nace"To kaima sai ka shirya mu fita tare." Yace."Ke dai ki fara fita nida mahaifiyarki zamu biyo bayanki."
Nace"To shikkenan baba yanda kace haka za'ayi......Kwalli na zirara a idona na shafa hoda sama-sama! sai nasa man le'be kadan a fuskata kana na hada kayan kwalliyar naje na ajiye.
Ina kokarin nade lifaya a jikina Tambaya ta shigo dakin....gani nayi ta tsaya tana murmushi, na saki fuskata ina dariya nace nayi kyau ne."? Kanta ta daga tace"Sosai kuwa idan zaki futa kiyi addua saboda bakin mutane." Dariyar maganar ta bani nace"To shikkenan zanyi insha Allah.
Tsakar gida na fito da mudubi a hannuna ina dubawa, gaskiya nayi kyau ni kaina nasan hakan, ajiye mudubin nayi kan taga nace"To Tambaya ni na fita sai kun fito." Tana daga daki tace"to shikkenan."
Koda na fito ban zarce gurin Walimar ba sai dana na biyawa Lahira na sameta a tsaye da mudubi a hannunta tana gyara daurin dankwalinta, wani irin kallo naga tabi ni dashi a take yanayin fuskarta ya sauya naso na fahimci wani abu...."Lallai Sumayya kece kikayi kyau haka."? abinda tafada kenan tana kallon sutturar jikina.
Yar dariya nayi ina duba jikina nace"Haba Lahira wane irin kyau banda zagi dai." Ta'be baki tayi ta cigaba da gyara daurin dankwalinta sosai abinda tayi ya bani mamaki na hango hassada da ganin kyashi a idonta.
Lami mahaifiyarta ce ta fito daga daki sai naga itama ta saki baki tana kallona, cikin sanyin jiki na tsuguna har kasa na gaisheta, bata amsa ba sai kumbura fuska takeyi tace"Ke Sumayya waye ya baki wannan kayan ni dai in banda ke banta'ba ganin wata baiwa tasa irin wannan sutturar ba.''
Wasa na shiga yi da hannuwana nace"Wallahi Mamma Fulani ce tayi min kyautarsu kin san ni nake kula da Yarima ta fanni abincinsa jin dadin yanda nake bashi kulawa yasa tayi min kyautar sutturu harda zoben gold."
Lahira da mahaifiyarta suka saki baki suna kallona kafin su mayar da hankalinsu kan zoben dake hannuna! Lami tsaki taja tayi gaba ba tare da tace komai ba, kallo na bita dashi ina mamakin abinda ya janyo haka.
Lahira kuwa gani nayi idonta yayi jawur kamar wacce tayi kuka duk sai naji banji dadin hakan ba, daurewa nayi nace."Lahira idan kin gama kizo muje mu samu gurun zama kada guri ya cika da jamaa mu tsaya a tsaye kinsan ni bana jurar tsayuwa.
Fitowa tayi daga dakinsu tana yafa mayafi ba tare data kalleni ba tace"Muje.'' bayanta nabi ina dana sanin biyo mata dan dana san zata nuna min hassada to da sai dai ta same ni a can..........."Sumayya da gaske ne auranku da Haruna."? Katsaham naji ta jefo min wannan tambayar....ajiyar zuciya na sauke nace"Eh mana ko haruna nada wata illar ne."
Ta'be baki tayi tace"Babu." dauke kaina nayi ina jin haushin abunda take yanzu na gano Lahira da zuciya biyu take zaune dani tunda gashi nan tana nuna min bakin ciki.
Koda muka isa gurin taron samunsa mukayi a ciki da kyar muka samu gurin zama muka zazzauna muka cigaba da jiran fitowar Sarki da tawagarsa shi kansa wanda ake gabatar da Walimar dominsa bai fito ba. amma kuma manya bakin sun fara zuwa an tanadar musu gurin zamansu na mussaman.
Mun kai kusan mintina arbain da zama kafin Maimartaba ya fito da tawagarsa, gurin ne ya hautsine da bushe bushe gami da hayaniyar jama'a kullum idan Sarki zai fito jama'a nunawa suke kamar basu ta'ba ganinshi ba, da kyar aka samu gurin yayi lafiya, Sarki ya zauna a mazauninsa 'yan uwansa suka zauna kusa dashi, can gefe guda kuma Yarima Ali ne dashi dasu Shatima sun sashi a tsakiya sunsha kwalliya da kayan sarauta amma nashi na mussaman ne dan ba karamin kyau yayi ba yana sanye da farar shadda sai ya dora bakar alkyabba a jikinsa, gaskiya wanda ya nad'a masa nad'in dake kanshi gwani ne dan ya fito dashi sosai kuma nad'in yayi masa kyau mutuka! kamar koda yaushe fuskarsa a had'e babu fara'a jefi jefi yake kallon jama'a gabadaya ya kasa sakewa a gurin sabida rashin san mutane
Malam Ahamad Sulaiman shine ya gabatar da karatun al'akurani mai girma gurin yayi tsit har malam ya gama karatun kana ya bude taron da addua. Maimartaba yayi jawabin godiya ga jama'ar da suka samu damar hallartar taron sannan yayi addua tare da fatan kowa ya koma gidansa lafiya.
Bayan ya koma gurin zamansa, Waziri ya fito yayi nasa jawabi Bayanshi Galadima Yayi Ciroma yazo yayi nasa dukkaninsu sun danne bakin cikin dake cikinsu suna ta fara'a gami da nuna farin cikinsu.
Koda Yarima Ali ya taso domin yin nasa jawabin gurin ne ya hargitse da hayaniya, sai da masu kula suka tsawatar tukkuna aka samu lafiya, dago kansa yay an samu ya dan saki fuskarsa ya daga hannuwansa sama alamun gaisuwa ga tarin jama'ar dake gurin, gurin ya sake rikicewa kowa na fadar albarkacin bakinsa, zuciyoyin Ma'kiya kamar su buga saboda ganin yanda Jama'a ke nuna kaunarsu akan Ma'kiyinsu.......Shima nasa 'bangaran yaji dadi sosai da yanda jama'a ke nuna masa kauna dalilin da yasa kenan ya sassauta fuskarsa ya dinga d'aga hannuwansa sama yana sakin murmushin farin ciki...Dauke kaina nayi daga kallon fuskarsa dan ni duk mubayar da jama'a ke masa ba burgeni suke ba, da sun san waye shi da duk basu yi masa ihu gami da fadin sai yayi ba, gabadaya ma ni ji nayi zaman gurin ya isheni kallonsa ko jin muryarsa na tayar min da bacin rai.
Tsaki naja lokacin dana ji miryarsa yana fadin"Alhamdullhi Allah kaine abin godiya daka nuna min wannan rana mai albarka wannan rana r ba zan ta'ba mancewa da itaba a cikin kundin tarihin rayuwata saboda rana ce mai muhimanci a gareni daku baki daya nagodewa Allah na kuma godewa mahaifina wanda ya zama silar samuwa ta a wannan duniya, mahaifina ya taka muhimiyyar rawa a tare dani ya tsaya min akan dukkanin al'amurana na yau da gobe tun ina yaro yake dawainiya dani har na kai wannan matakin dana ke kai a yanzu.....Naje america nayi karatu mai zurfi dan na taimaki kaina da al'ummar musulmi alhamdullhi yau wata na hudu da dawowa gida duk wani hutu dana ke bukatar nayi na samu insha Allahu ranar monday litinin kenan zan fara aiki a sabon asibitina mai musa *Zinariya Hospital* asibitina ya kasance kyauta ga duk masu wa'innan lalurorin da zan lissafo.".. ...........Jin wannan magana tasa yasa jama'a da yawa suka mayar da hankalinsu kansa suna sauraransa.
Yarima Ali ya cigaba da cewa." Idan akwai masu fama da matsalar hawan jini Sugar ciwon qoda ciwon hanta cancer duk suna iya zuwa asibitina a sati mai zuwa domin su fara kar'bar magani, sannan akwai 'bangaran mata masu cika da masu haihuwa akwai bangaran yara masu fama cutar sikila asma nimonia da sauran cutukan dake dake addabar yara a kananu idan d'anka ko 'yarka na fama da daya daga cikin wa'innan cutukan dana lissafo to sai ka maxa ka garzaya dashi asibiti a sati mai zuwa insha Allahu za'a dora shi kan maganin daya dace, akwai likitoci na mussaman da muka tanada domin duba marasa lafiya amma duk da haka muna bukatar karin wasu kananun ma'akaita saboda haka dik wanda ke bukatar mu daukeshi aiki sai yazo mana da takardunsa a cikin satin da zamu shiga insha Allahu idan mun duba cancanta da nagartarsa zamu daukeshi aiki domin ya taimaki kansa kuma ya taimaki al'umma da ilimin da Allah yayi masa, wannan shine takaitaccan jawabin da zanyi!.'" Yarima Ali na gama jawabinsa guri ya hautsine jamaa suka dinga murna da farin ciki jin abin alkairin da suka samu. da kyar aka samu gurin yayi shuru, Maimartaba tsabar farin ciki kasa cewa komai yayi sai mirmushi yake yi, Waziri na taya shi, Bangaran su Ciroma kuwa tamkar zuciyarsu zata fito waje saboda haushi da takaici...Muddibo kuwa tashi yayi ya bar gurin can bangaran Uwargida Huwaila ya nufa, nan ya samesu sunyi jugum! abin duniya ya ishe su Aunt Safiyya da Aunty Bushira sai kuka sukeyi suna fad'in su basu yarda da wannan kyautar da Sarki yayi wa Yarima Ali ba kyautar Asibiti gari guda su suna zaune ko tsinke bai basu ba dan haka wallahi ba zasu tafi ba sai ya shigo gidan suma yayi musu kyautar filaye ko gidaje.,....
Mi'kewa nayi ina kokarin cire rigata gefe guda kuma ina mamakin yanda tambaya ta damu da dole sai nayi wanka na shirya nida zan samu yanda nake so wallahi ba zan fita ba balantana na ganshi gabad'aya ya fice min daga raina tausayinsa ma na daina ji sabida irin rashin kyautawar da yayi min jiya.
Daya daga cikin tamfofin da Fulani keyi min kyautarsu na dauko wata super mai ruwan ganye nasa a jikina, nayi mamaki sosai da dinkin ya zauna a jikina tamkar an auna ni.
Murmushi nayi a sanda na kalli mudubi naga yanda nayi kyau Atamfar ta haska ni
Zama nayi domin na gyara fuskata babana ne ya shigo fuskarsa cike da walwala da farin ciki yace."Yawwa Sumayya ki shirya sosai ga 'yan uwanki can kowacce tayi ado inaso ki zama tauraruwa a cikinsu.' cikin tsokana yake maganar
Dariya nasa nace"Baba kenan ashe kana so nayi kyau nafi kowa ko."? da mirmushi a fuskarsa yace."Eh mana ai kowa nasa ya sani." murmushi nayi nace"To kaima sai ka shirya mu fita tare." Yace."Ke dai ki fara fita nida mahaifiyarki zamu biyo bayanki."
Nace"To shikkenan baba yanda kace haka za'ayi......Kwalli na zirara a idona na shafa hoda sama-sama! sai nasa man le'be kadan a fuskata kana na hada kayan kwalliyar naje na ajiye.
Ina kokarin nade lifaya a jikina Tambaya ta shigo dakin....gani nayi ta tsaya tana murmushi, na saki fuskata ina dariya nace nayi kyau ne."? Kanta ta daga tace"Sosai kuwa idan zaki futa kiyi addua saboda bakin mutane." Dariyar maganar ta bani nace"To shikkenan zanyi insha Allah.
Tsakar gida na fito da mudubi a hannuna ina dubawa, gaskiya nayi kyau ni kaina nasan hakan, ajiye mudubin nayi kan taga nace"To Tambaya ni na fita sai kun fito." Tana daga daki tace"to shikkenan."
Koda na fito ban zarce gurin Walimar ba sai dana na biyawa Lahira na sameta a tsaye da mudubi a hannunta tana gyara daurin dankwalinta, wani irin kallo naga tabi ni dashi a take yanayin fuskarta ya sauya naso na fahimci wani abu...."Lallai Sumayya kece kikayi kyau haka."? abinda tafada kenan tana kallon sutturar jikina.
Yar dariya nayi ina duba jikina nace"Haba Lahira wane irin kyau banda zagi dai." Ta'be baki tayi ta cigaba da gyara daurin dankwalinta sosai abinda tayi ya bani mamaki na hango hassada da ganin kyashi a idonta.
Lami mahaifiyarta ce ta fito daga daki sai naga itama ta saki baki tana kallona, cikin sanyin jiki na tsuguna har kasa na gaisheta, bata amsa ba sai kumbura fuska takeyi tace"Ke Sumayya waye ya baki wannan kayan ni dai in banda ke banta'ba ganin wata baiwa tasa irin wannan sutturar ba.''
Wasa na shiga yi da hannuwana nace"Wallahi Mamma Fulani ce tayi min kyautarsu kin san ni nake kula da Yarima ta fanni abincinsa jin dadin yanda nake bashi kulawa yasa tayi min kyautar sutturu harda zoben gold."
Lahira da mahaifiyarta suka saki baki suna kallona kafin su mayar da hankalinsu kan zoben dake hannuna! Lami tsaki taja tayi gaba ba tare da tace komai ba, kallo na bita dashi ina mamakin abinda ya janyo haka.
Lahira kuwa gani nayi idonta yayi jawur kamar wacce tayi kuka duk sai naji banji dadin hakan ba, daurewa nayi nace."Lahira idan kin gama kizo muje mu samu gurun zama kada guri ya cika da jamaa mu tsaya a tsaye kinsan ni bana jurar tsayuwa.
Fitowa tayi daga dakinsu tana yafa mayafi ba tare data kalleni ba tace"Muje.'' bayanta nabi ina dana sanin biyo mata dan dana san zata nuna min hassada to da sai dai ta same ni a can..........."Sumayya da gaske ne auranku da Haruna."? Katsaham naji ta jefo min wannan tambayar....ajiyar zuciya na sauke nace"Eh mana ko haruna nada wata illar ne."
Ta'be baki tayi tace"Babu." dauke kaina nayi ina jin haushin abunda take yanzu na gano Lahira da zuciya biyu take zaune dani tunda gashi nan tana nuna min bakin ciki.
Koda muka isa gurin taron samunsa mukayi a ciki da kyar muka samu gurin zama muka zazzauna muka cigaba da jiran fitowar Sarki da tawagarsa shi kansa wanda ake gabatar da Walimar dominsa bai fito ba. amma kuma manya bakin sun fara zuwa an tanadar musu gurin zamansu na mussaman.
Mun kai kusan mintina arbain da zama kafin Maimartaba ya fito da tawagarsa, gurin ne ya hautsine da bushe bushe gami da hayaniyar jama'a kullum idan Sarki zai fito jama'a nunawa suke kamar basu ta'ba ganinshi ba, da kyar aka samu gurin yayi lafiya, Sarki ya zauna a mazauninsa 'yan uwansa suka zauna kusa dashi, can gefe guda kuma Yarima Ali ne dashi dasu Shatima sun sashi a tsakiya sunsha kwalliya da kayan sarauta amma nashi na mussaman ne dan ba karamin kyau yayi ba yana sanye da farar shadda sai ya dora bakar alkyabba a jikinsa, gaskiya wanda ya nad'a masa nad'in dake kanshi gwani ne dan ya fito dashi sosai kuma nad'in yayi masa kyau mutuka! kamar koda yaushe fuskarsa a had'e babu fara'a jefi jefi yake kallon jama'a gabadaya ya kasa sakewa a gurin sabida rashin san mutane
Malam Ahamad Sulaiman shine ya gabatar da karatun al'akurani mai girma gurin yayi tsit har malam ya gama karatun kana ya bude taron da addua. Maimartaba yayi jawabin godiya ga jama'ar da suka samu damar hallartar taron sannan yayi addua tare da fatan kowa ya koma gidansa lafiya.
Bayan ya koma gurin zamansa, Waziri ya fito yayi nasa jawabi Bayanshi Galadima Yayi Ciroma yazo yayi nasa dukkaninsu sun danne bakin cikin dake cikinsu suna ta fara'a gami da nuna farin cikinsu.
Koda Yarima Ali ya taso domin yin nasa jawabin gurin ne ya hargitse da hayaniya, sai da masu kula suka tsawatar tukkuna aka samu lafiya, dago kansa yay an samu ya dan saki fuskarsa ya daga hannuwansa sama alamun gaisuwa ga tarin jama'ar dake gurin, gurin ya sake rikicewa kowa na fadar albarkacin bakinsa, zuciyoyin Ma'kiya kamar su buga saboda ganin yanda Jama'a ke nuna kaunarsu akan Ma'kiyinsu.......Shima nasa 'bangaran yaji dadi sosai da yanda jama'a ke nuna masa kauna dalilin da yasa kenan ya sassauta fuskarsa ya dinga d'aga hannuwansa sama yana sakin murmushin farin ciki...Dauke kaina nayi daga kallon fuskarsa dan ni duk mubayar da jama'a ke masa ba burgeni suke ba, da sun san waye shi da duk basu yi masa ihu gami da fadin sai yayi ba, gabadaya ma ni ji nayi zaman gurin ya isheni kallonsa ko jin muryarsa na tayar min da bacin rai.
Tsaki naja lokacin dana ji miryarsa yana fadin"Alhamdullhi Allah kaine abin godiya daka nuna min wannan rana mai albarka wannan rana r ba zan ta'ba mancewa da itaba a cikin kundin tarihin rayuwata saboda rana ce mai muhimanci a gareni daku baki daya nagodewa Allah na kuma godewa mahaifina wanda ya zama silar samuwa ta a wannan duniya, mahaifina ya taka muhimiyyar rawa a tare dani ya tsaya min akan dukkanin al'amurana na yau da gobe tun ina yaro yake dawainiya dani har na kai wannan matakin dana ke kai a yanzu.....Naje america nayi karatu mai zurfi dan na taimaki kaina da al'ummar musulmi alhamdullhi yau wata na hudu da dawowa gida duk wani hutu dana ke bukatar nayi na samu insha Allahu ranar monday litinin kenan zan fara aiki a sabon asibitina mai musa *Zinariya Hospital* asibitina ya kasance kyauta ga duk masu wa'innan lalurorin da zan lissafo.".. ...........Jin wannan magana tasa yasa jama'a da yawa suka mayar da hankalinsu kansa suna sauraransa.
Yarima Ali ya cigaba da cewa." Idan akwai masu fama da matsalar hawan jini Sugar ciwon qoda ciwon hanta cancer duk suna iya zuwa asibitina a sati mai zuwa domin su fara kar'bar magani, sannan akwai 'bangaran mata masu cika da masu haihuwa akwai bangaran yara masu fama cutar sikila asma nimonia da sauran cutukan dake dake addabar yara a kananu idan d'anka ko 'yarka na fama da daya daga cikin wa'innan cutukan dana lissafo to sai ka maxa ka garzaya dashi asibiti a sati mai zuwa insha Allahu za'a dora shi kan maganin daya dace, akwai likitoci na mussaman da muka tanada domin duba marasa lafiya amma duk da haka muna bukatar karin wasu kananun ma'akaita saboda haka dik wanda ke bukatar mu daukeshi aiki sai yazo mana da takardunsa a cikin satin da zamu shiga insha Allahu idan mun duba cancanta da nagartarsa zamu daukeshi aiki domin ya taimaki kansa kuma ya taimaki al'umma da ilimin da Allah yayi masa, wannan shine takaitaccan jawabin da zanyi!.'" Yarima Ali na gama jawabinsa guri ya hautsine jamaa suka dinga murna da farin ciki jin abin alkairin da suka samu. da kyar aka samu gurin yayi shuru, Maimartaba tsabar farin ciki kasa cewa komai yayi sai mirmushi yake yi, Waziri na taya shi, Bangaran su Ciroma kuwa tamkar zuciyarsu zata fito waje saboda haushi da takaici...Muddibo kuwa tashi yayi ya bar gurin can bangaran Uwargida Huwaila ya nufa, nan ya samesu sunyi jugum! abin duniya ya ishe su Aunt Safiyya da Aunty Bushira sai kuka sukeyi suna fad'in su basu yarda da wannan kyautar da Sarki yayi wa Yarima Ali ba kyautar Asibiti gari guda su suna zaune ko tsinke bai basu ba dan haka wallahi ba zasu tafi ba sai ya shigo gidan suma yayi musu kyautar filaye ko gidaje.,....