Sashe 26
Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wayar dake hannunsa ya ajiye kan drowar cikin kulawa ya amsa da fadin"Ameen suma ameen nagode kwarai ku sauka lafiya." Babana da Tambaya suka kama hanyar futa suna jin dadi a cikin zuciyarsu bayansu nabi nima raina tas naji dadi sosai da bai wulakanta min iyayena ba.
Har bakin mota na rakasu suka shiga direba yaja suka tafi cike da kauna da kewarsu na koma cikin asibitin... dakin na koma still yana zaune a inda yake ya d'auki wayar yana dubawa, agogo na duba naga biyar shaura, jikina na bani baiyi sallah ba cikin rawar baki nace"Ranka ya dade biyar saura lokacin sallah ya wuce."
Kallona yayi cikin mamaki yace."Waye yace miki banyi sallah ba? lallai yarinyar nan kin raina ni da yawa ni kike tunawa lokacin sallah."? Da sauri nace"Aa ba nufina na 'bata maka rai ba ranka ya dad'e nasan sharrin abar dake hannunka waya tana hana ibadah akan lokaci shiyasa nayi maka wannan maganar." Tsaki! mai karfi yaja ya d'auke kansa daga kaina, juyawa nayi zan fita daga dakin yace."Ke! zo ki d'auke tsiyarku bana bukata."
Da sauri na Juyo ina kallonsa dan ban fahimci maganarsa ba, ledar kayan dubiyar da babana ya kawo masa ya jefo min ta sauka daidai kafafuna. "D'auka ki fita dashi d'aga d'akin nan."! yafada yana min wani irin kallo.
A hankali na sunkuya ina kallon kayan dubiyar manya manyan mangwaro ne masu kyau da nuna duk wanda ya gansu sai yayi sha'awa saboda kyawunsu, cikin ledar na mayar da mangwaron k'walla na taruwa a idona na mi'ke tsaye da ledar a hannuna, cikin rawar murya nace" Me yasa lokacin da'aka baka ka kar'ba harda godiya wannan abin da kayi d'abiar munafukan mutane ne." Uffan bece min ba dan idan da sabo ya saba da tsayayyata bana jin tsoron fad'a masa gaskiya komai d'acinta sai dai ya gaji da marina ko dukuna........."Allah ya shiryeka shirin addinin musulnci." Abinda na fad'a kenan a k'untace na kama hanya zan fita daga dakin naji yace."Da yake Ubanki ne ya kawo min kayan dubiyar ai baki tsaya kin duba kin binkicika ba kai tsaye kika ajiye min sabida kina ganin shi ba zai iya cutar dani ba ko."?
Kallonsa nayi raina bak'ik'irin nace"Babana ba zai cutar da kai ba kuma baza'a hada baki dashi a cuceka ba, inaso na tabbatar maka da cewa akan gaskiya mahaifina na iya rasa rayuwarsa mutum ne shi mai tsoron Allah da gudun duniya idan ma kana zarginsa akan wani abu to ka daina domin kuwa kana daukar hakkinsa.
"Dallah malama fita ki bani guri kin tsaya kaina kina tsara magana ni bana shedar mahaifinki dan ban yarda dashi ba ke bari kiji ke kanki ban yarda dake ba ballanatana Ubanki duk wannan tsayayyar da kike a kaina kallon ki kawai nake."
Cikin sigar k'unsa ba'kin ciki nace"Na lura tunda na hanaka kaina kake zagina kana cin mutuncina to bari kaji wallahi mai kusantar wannan jikin nawa sai salihin namiji nagartacce mai addini maganar rashin yarda daka keyi ka yarda dani ko kada ka yarda dani bai dameni ba domin Allah nake kula da kai kuma nasan yafi kowa sanin zuciyata insha Allahu burinka ba zai cika a kaina ba."! ina kare maganar na bude kofar dakin a zafafe! na fita tare da buga masa kofar da karfin gaske.
Ya jima maganganun yarinyar na yi masa amsa kuwwa a kunne tunda yake ba'a ta'ba mayar masa da raddi masu zafi irin na yarinyar ba, tana samun dama a kansa sosai tana farfada masa ba'ka'ken maganganu iya son ranta yasan kuma ba komai ne ya janyo haka ba illah zulamarsa daya nuna a fili amma yana da kyau rana guda ya nuna mata cewa bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane.
Tunda mukayi haka dashi naji gabadaya zaman asibitin ya fita daga raina addua na dinga yi akan Allah yasa a sallameshi domin mu koma gida na gaji da zama a asibitin na kuma gaji da irin wulakanci da iskancin da yake min, sati biyu da nayi a asibitin nayi asarar karatuna nasan an wuce ni sosai dole idan na koma na nemi wata ta koya min hakan ya sake sakani cikin damuwa kullum fuskata a had'e babu walwala, Dr Rabo shine yake nema ya shige min hanci kusan kullum da daddare sai yayi kirana ofis dinsa idan naje kawai nsai kura min ido yayi ta kallona idan na tambayi ba'asi sai yay murmushi yace."Kawai ya kirani ne domin mu gaisa ya kuma kalleni yaji dadi. cike da takaici nake tambayarsa meye amfanin kallon nawa, kai tsaye sai yace." Shi kadai yasan amfanin hakan, rai a 'bace nake fita daga ofis din.......Ana ya gobe za'a sallameshi dana shiga dakin na sameshi kan kujera daga shi sai gajeran wando farar fatar jikinsa sai daukar ido take kirjinsa cike yake da gashi hakanan saman kafafunsa gashine a kwance bakikirin, ban iya kallonsa a hakaba ba na kautar da kaina da fad'in "Ranka ya dad'e Haruna yace." Kana nema na."? Banza yay dani bai kalli inda nake tsaye ba ballantana ya amsa min. daure zuciyata nayi na sake yi masa magana, ya kalleni a watse yace."Meye tsakaninki da wannan likitan mai ciki kamar rumbu." Dr Rabo gajere ne mai tumbi shiyasa ya kirasa da wannan sunan.
Murmushi nayi dan na sake 'kuntata masa nace"Ranka ya dade kana yawan kushe hallitar Allah kaima fa kana da mukusa a jikinka kasan d'an adam tara yake be cika goma ba."
Rai a 'bace! yace."Ba wannan na tambayeki ba na tambayaki abinda yake tsakanin ki da Dr Rabo." Ajiyar zuciya na sauke nace"Sirri ne a tsakani na dashi bana bukatar kowa ya sanshi.
Naga ya zuba min da'kwa-da'kwan idanunsa yana hararata yace."Wane sirri zaki 'boye bayan abu gashinan a zahiri na sani jama'a sun sani duk daran duniya kina shiga ofis dinsa yana lalata dake shine zaki ce sirri."!!
Gabana ya dinga fad'uwa! wannan wane irin d'an sharri ne? 'kazafi zaiyi mana kenan, tsabar firgici da tashin hankali na gagara cewa komai....Yace."Ko nayi k'arya ne."! Hawaye ne suka zubo min na kalleshi muryata na rawa nace" Allah ya sakamin k'azafin da kayi min insha Allahu sai mun tsaya gaban ubangiji akan wannan magana da ka fad'a.'" Hanyar fita na nufa ina kuka wiwi!! jikinsa ne yay sanyi ganin irin uban kukan data fita tanayi! tsaki yaja ya mik'e ko banza ya samu sassauci a cikin zuciyarsa yarinyar ta jima tana 'kuntata masa yau ya rage kuncin dake damunsa, tuntuni ya gane Dr Rabo sonta yake shiyasa gabadaya ya gaza nutsuwa yana fargaba kada yaje wani abu ya shiga a tsakaninsu mugun kishin Dr yake ya'ki nunawa ne saboda wata manufa tashi, da yarinyar ta amince ta zama mai d'eba masa kewa to da tuni ya 'yanta ta ita da iyayenta su tashi daga sunan bayi su koma mutane masu 'yanci, yana jin tsoron Dr Rabo ya yaudareta ta bashi kanta shiyasa gabadaya shima yaji zaman asibitin ya isheshi.
'Daki na shiga na zauna na dinga rizgar kukan dana dade ina tarawa, a duniya ba'a ta'ba yi min abinda ya sani cikin kunci da bakin ciki ba irin k'azafin da guy nan yayi min wato tunda na'ki yarda dashi da bukatarsa shine ya yanke shawarar 'bullowa ta wannan hanyar na tsani zina da masu aikatata sai gashi yau banji ba ban gani ba anyi min 'kazafi da ita, kuka sosai nake ina rirrike kaina.
Muryar Haruna naji a kaina a firgice na dago ina kallonsa hannu nasa na goge hawayen fuskata nace"Haruna yaushe ka shigo ko motsin bude kofa banji ba.
A sanyaye yace."Ya za'ayi dama kiji motsin bude kofa kina irin wannan kukan." Cikin ya'ke nace"Haruna waye yace da kai kuka nake wani abu ne ya shige min ido shine ruwan hawaye yake futa.
Murmushi yay yace."Ni ba yaro bane ballantana ki yaudareni da wannan maganar akan idona kika fito daga dakin da Yarima Ali yake kina kuka dan Allah yau dai kiyi min bayanin abinda ke tsakaninki dashi dan sau tari ina yawan ganinki kina fitowa daga dakin cikin bacin rai."
Kasa cewa komai nayi ina mamaki maganarsa ashe Haruna yana hankalce da abinda ke faruwa tsakanina da Yarima! a gaskiya nayi mamaki, dan kada ya zargi wani abu mai muni a tsakanina dashi yasa na yanke shawarar fad'a masa haka." Wallahi Haruna na gaji da zaman asibitin nan na gaji da wulakancin da muke fuskanta daga gurinsa nifa sai nake ganin kamar ni kadai ya tsana kullum cikin zagin iyayena yake yana buga min tsawa duk abinda zanyi masa bana gwaninta, wannan dalilin yasa kullum kake ganina ina fitowa daga dakin raina a bace."
Haruna yace."Hakuri zakiyi da yanda kika tsinci rayuwarki a ciki sumayya ki cigaba dayin aikin ki koda kuwa zai ce ki kwanta a kasa ya bi ta kanki baki da za'bi dole kibi umarninsa kasancewarki baiwar dake karkashinsa dole ki d'auki hakurin dukkanin abinda zaki gani, shawarar da zan baki shine ki tsananta addua akan Allah ya baki miji a kurkusa idan kinyi aure shikkenan kin huta da wannan aikin. amma mutukar ba kiyi aure ba to babu shakka zaki cigaba dayi masa hidima har karshen rayuwarki."
Maganganun Haruna sun kashe min jiki sosai na soma hango 'kamshin gaskiya a cikin maganarsa babu shakka idan nayi aure na huta da fargaba da tashin hankali ko banza nasan zan samu sassauci a wani 'bangare.
A sanyaye nace"Haruna nagode sosai na kuma ji dadi da wannan shawarar taka insha Allahu zan duba wanda ya dace dani na aura." Murmushi yayi yace."To babu damuwa Sumayya nima ina cikin layin masu so dan a gaskiya kina burgeni mutuka Sumayya kina da nutsuwa da kamun kai babu namijin da ba zaiyi sha'awar ki zama uwar 'ya'yansa ba."
Kallonsa nake ina mamakin furucinsa, yay murmushi yana shafa sumarsa yace."Ni zan tafi domin na barki kiyi tunani sai anjima." hanyar fita ya kama nabi shi da kallon mamaki har ya fita daga dakin......
*BINTA UMAR ABBALE*
Har bakin mota na rakasu suka shiga direba yaja suka tafi cike da kauna da kewarsu na koma cikin asibitin... dakin na koma still yana zaune a inda yake ya d'auki wayar yana dubawa, agogo na duba naga biyar shaura, jikina na bani baiyi sallah ba cikin rawar baki nace"Ranka ya dade biyar saura lokacin sallah ya wuce."
Kallona yayi cikin mamaki yace."Waye yace miki banyi sallah ba? lallai yarinyar nan kin raina ni da yawa ni kike tunawa lokacin sallah."? Da sauri nace"Aa ba nufina na 'bata maka rai ba ranka ya dad'e nasan sharrin abar dake hannunka waya tana hana ibadah akan lokaci shiyasa nayi maka wannan maganar." Tsaki! mai karfi yaja ya d'auke kansa daga kaina, juyawa nayi zan fita daga dakin yace."Ke! zo ki d'auke tsiyarku bana bukata."
Da sauri na Juyo ina kallonsa dan ban fahimci maganarsa ba, ledar kayan dubiyar da babana ya kawo masa ya jefo min ta sauka daidai kafafuna. "D'auka ki fita dashi d'aga d'akin nan."! yafada yana min wani irin kallo.
A hankali na sunkuya ina kallon kayan dubiyar manya manyan mangwaro ne masu kyau da nuna duk wanda ya gansu sai yayi sha'awa saboda kyawunsu, cikin ledar na mayar da mangwaron k'walla na taruwa a idona na mi'ke tsaye da ledar a hannuna, cikin rawar murya nace" Me yasa lokacin da'aka baka ka kar'ba harda godiya wannan abin da kayi d'abiar munafukan mutane ne." Uffan bece min ba dan idan da sabo ya saba da tsayayyata bana jin tsoron fad'a masa gaskiya komai d'acinta sai dai ya gaji da marina ko dukuna........."Allah ya shiryeka shirin addinin musulnci." Abinda na fad'a kenan a k'untace na kama hanya zan fita daga dakin naji yace."Da yake Ubanki ne ya kawo min kayan dubiyar ai baki tsaya kin duba kin binkicika ba kai tsaye kika ajiye min sabida kina ganin shi ba zai iya cutar dani ba ko."?
Kallonsa nayi raina bak'ik'irin nace"Babana ba zai cutar da kai ba kuma baza'a hada baki dashi a cuceka ba, inaso na tabbatar maka da cewa akan gaskiya mahaifina na iya rasa rayuwarsa mutum ne shi mai tsoron Allah da gudun duniya idan ma kana zarginsa akan wani abu to ka daina domin kuwa kana daukar hakkinsa.
"Dallah malama fita ki bani guri kin tsaya kaina kina tsara magana ni bana shedar mahaifinki dan ban yarda dashi ba ke bari kiji ke kanki ban yarda dake ba ballanatana Ubanki duk wannan tsayayyar da kike a kaina kallon ki kawai nake."
Cikin sigar k'unsa ba'kin ciki nace"Na lura tunda na hanaka kaina kake zagina kana cin mutuncina to bari kaji wallahi mai kusantar wannan jikin nawa sai salihin namiji nagartacce mai addini maganar rashin yarda daka keyi ka yarda dani ko kada ka yarda dani bai dameni ba domin Allah nake kula da kai kuma nasan yafi kowa sanin zuciyata insha Allahu burinka ba zai cika a kaina ba."! ina kare maganar na bude kofar dakin a zafafe! na fita tare da buga masa kofar da karfin gaske.
Ya jima maganganun yarinyar na yi masa amsa kuwwa a kunne tunda yake ba'a ta'ba mayar masa da raddi masu zafi irin na yarinyar ba, tana samun dama a kansa sosai tana farfada masa ba'ka'ken maganganu iya son ranta yasan kuma ba komai ne ya janyo haka ba illah zulamarsa daya nuna a fili amma yana da kyau rana guda ya nuna mata cewa bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane.
Tunda mukayi haka dashi naji gabadaya zaman asibitin ya fita daga raina addua na dinga yi akan Allah yasa a sallameshi domin mu koma gida na gaji da zama a asibitin na kuma gaji da irin wulakanci da iskancin da yake min, sati biyu da nayi a asibitin nayi asarar karatuna nasan an wuce ni sosai dole idan na koma na nemi wata ta koya min hakan ya sake sakani cikin damuwa kullum fuskata a had'e babu walwala, Dr Rabo shine yake nema ya shige min hanci kusan kullum da daddare sai yayi kirana ofis dinsa idan naje kawai nsai kura min ido yayi ta kallona idan na tambayi ba'asi sai yay murmushi yace."Kawai ya kirani ne domin mu gaisa ya kuma kalleni yaji dadi. cike da takaici nake tambayarsa meye amfanin kallon nawa, kai tsaye sai yace." Shi kadai yasan amfanin hakan, rai a 'bace nake fita daga ofis din.......Ana ya gobe za'a sallameshi dana shiga dakin na sameshi kan kujera daga shi sai gajeran wando farar fatar jikinsa sai daukar ido take kirjinsa cike yake da gashi hakanan saman kafafunsa gashine a kwance bakikirin, ban iya kallonsa a hakaba ba na kautar da kaina da fad'in "Ranka ya dad'e Haruna yace." Kana nema na."? Banza yay dani bai kalli inda nake tsaye ba ballantana ya amsa min. daure zuciyata nayi na sake yi masa magana, ya kalleni a watse yace."Meye tsakaninki da wannan likitan mai ciki kamar rumbu." Dr Rabo gajere ne mai tumbi shiyasa ya kirasa da wannan sunan.
Murmushi nayi dan na sake 'kuntata masa nace"Ranka ya dade kana yawan kushe hallitar Allah kaima fa kana da mukusa a jikinka kasan d'an adam tara yake be cika goma ba."
Rai a 'bace! yace."Ba wannan na tambayeki ba na tambayaki abinda yake tsakanin ki da Dr Rabo." Ajiyar zuciya na sauke nace"Sirri ne a tsakani na dashi bana bukatar kowa ya sanshi.
Naga ya zuba min da'kwa-da'kwan idanunsa yana hararata yace."Wane sirri zaki 'boye bayan abu gashinan a zahiri na sani jama'a sun sani duk daran duniya kina shiga ofis dinsa yana lalata dake shine zaki ce sirri."!!
Gabana ya dinga fad'uwa! wannan wane irin d'an sharri ne? 'kazafi zaiyi mana kenan, tsabar firgici da tashin hankali na gagara cewa komai....Yace."Ko nayi k'arya ne."! Hawaye ne suka zubo min na kalleshi muryata na rawa nace" Allah ya sakamin k'azafin da kayi min insha Allahu sai mun tsaya gaban ubangiji akan wannan magana da ka fad'a.'" Hanyar fita na nufa ina kuka wiwi!! jikinsa ne yay sanyi ganin irin uban kukan data fita tanayi! tsaki yaja ya mik'e ko banza ya samu sassauci a cikin zuciyarsa yarinyar ta jima tana 'kuntata masa yau ya rage kuncin dake damunsa, tuntuni ya gane Dr Rabo sonta yake shiyasa gabadaya ya gaza nutsuwa yana fargaba kada yaje wani abu ya shiga a tsakaninsu mugun kishin Dr yake ya'ki nunawa ne saboda wata manufa tashi, da yarinyar ta amince ta zama mai d'eba masa kewa to da tuni ya 'yanta ta ita da iyayenta su tashi daga sunan bayi su koma mutane masu 'yanci, yana jin tsoron Dr Rabo ya yaudareta ta bashi kanta shiyasa gabadaya shima yaji zaman asibitin ya isheshi.
'Daki na shiga na zauna na dinga rizgar kukan dana dade ina tarawa, a duniya ba'a ta'ba yi min abinda ya sani cikin kunci da bakin ciki ba irin k'azafin da guy nan yayi min wato tunda na'ki yarda dashi da bukatarsa shine ya yanke shawarar 'bullowa ta wannan hanyar na tsani zina da masu aikatata sai gashi yau banji ba ban gani ba anyi min 'kazafi da ita, kuka sosai nake ina rirrike kaina.
Muryar Haruna naji a kaina a firgice na dago ina kallonsa hannu nasa na goge hawayen fuskata nace"Haruna yaushe ka shigo ko motsin bude kofa banji ba.
A sanyaye yace."Ya za'ayi dama kiji motsin bude kofa kina irin wannan kukan." Cikin ya'ke nace"Haruna waye yace da kai kuka nake wani abu ne ya shige min ido shine ruwan hawaye yake futa.
Murmushi yay yace."Ni ba yaro bane ballantana ki yaudareni da wannan maganar akan idona kika fito daga dakin da Yarima Ali yake kina kuka dan Allah yau dai kiyi min bayanin abinda ke tsakaninki dashi dan sau tari ina yawan ganinki kina fitowa daga dakin cikin bacin rai."
Kasa cewa komai nayi ina mamaki maganarsa ashe Haruna yana hankalce da abinda ke faruwa tsakanina da Yarima! a gaskiya nayi mamaki, dan kada ya zargi wani abu mai muni a tsakanina dashi yasa na yanke shawarar fad'a masa haka." Wallahi Haruna na gaji da zaman asibitin nan na gaji da wulakancin da muke fuskanta daga gurinsa nifa sai nake ganin kamar ni kadai ya tsana kullum cikin zagin iyayena yake yana buga min tsawa duk abinda zanyi masa bana gwaninta, wannan dalilin yasa kullum kake ganina ina fitowa daga dakin raina a bace."
Haruna yace."Hakuri zakiyi da yanda kika tsinci rayuwarki a ciki sumayya ki cigaba dayin aikin ki koda kuwa zai ce ki kwanta a kasa ya bi ta kanki baki da za'bi dole kibi umarninsa kasancewarki baiwar dake karkashinsa dole ki d'auki hakurin dukkanin abinda zaki gani, shawarar da zan baki shine ki tsananta addua akan Allah ya baki miji a kurkusa idan kinyi aure shikkenan kin huta da wannan aikin. amma mutukar ba kiyi aure ba to babu shakka zaki cigaba dayi masa hidima har karshen rayuwarki."
Maganganun Haruna sun kashe min jiki sosai na soma hango 'kamshin gaskiya a cikin maganarsa babu shakka idan nayi aure na huta da fargaba da tashin hankali ko banza nasan zan samu sassauci a wani 'bangare.
A sanyaye nace"Haruna nagode sosai na kuma ji dadi da wannan shawarar taka insha Allahu zan duba wanda ya dace dani na aura." Murmushi yayi yace."To babu damuwa Sumayya nima ina cikin layin masu so dan a gaskiya kina burgeni mutuka Sumayya kina da nutsuwa da kamun kai babu namijin da ba zaiyi sha'awar ki zama uwar 'ya'yansa ba."
Kallonsa nake ina mamakin furucinsa, yay murmushi yana shafa sumarsa yace."Ni zan tafi domin na barki kiyi tunani sai anjima." hanyar fita ya kama nabi shi da kallon mamaki har ya fita daga dakin......
*BINTA UMAR ABBALE*