← Book details Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 90

Sashe 41

Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yana juyowa muka had'a ido dashi, sai naga yayi wani irin murmushi kai kana ganinsa kasan na saduda ne tabbas bahaushe yayi gaskiya da yace ( bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane) ina shi ina had'a neman aure da Magajin sarki mai jiran gado tilas yanaji yana gani ya hakura da Sumayya ya bar masa, girgiza kansa yayi yana kallona nan na hango yanda idanunsa ya tara ruwan hawaye da sauri ya bude kofa ya fita.

Nima hawayen dake kokarin zubo min na mayar ina danne wani k'aton abu a mak'ogwarona, kallonsa nayi yana hard'e a kan kujera nace."Wallahi idan ka raba wannan soyayyar da k'arfin mulkin ka idan ka raba wannan k'aunar da karfin ikon ka to na tabbata Allah ba zai barka ba, kuma mutukar ka samu nasarar raba tsakanina da masoyina na gaskiya ka rubuta ka ajiye ko ka aureni ba zaka samu biyan bukatarka ba, saboda haka ka zauna kayi tunani da kyau akan maganata." Hanya na kama zan fita, da sauri na ganshi ya tari gabana zuba masa ido nayi ina kallonsa, Yace." Ni kuma nayi al'kawarin auranki ko kina so ko bakya so auranki bani na nema ba ke kika nema bayan kin kwad'aita min kuma daga baya kizo min da wata maganar banza! to na d'aura d'amarar auranki domin na kawar da sha'awata a kanki."

Cikin 'kunar zuciya na kalleshi magana nake so nayi tsabar bacin rai da takaici ya hana ni cewa komai ratse shi nayi zan wuce ya sake tare min hanya yana min wani irin kallo. girgiza kaina nayi nace "Bani hanya na wuce." Sake babbake hanyar yayi ya dogare hannusa a jikin bango....karfi nasa na doke hannun na ture shi! taga-taga yayi zai fadi baki ya bude yana kallona! tsaki mai karfi naja na bude kofa na fita. Murmushi yay yana mamakin k'arfin yarinyar har ta iya tureshi yana tsaye bai dauki mataki ba, kan kujera ya zauna yana tunanin ta yanda al'amarin zai yuwu.....

*Na kudi ne*
Kada ki karanta min littafi sai kin biya ke kuma da kika futar da littafin keda Allah, idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip group #600 normal group #300 account.... 0542382124.....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min magana ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊�)
71&72
Cikin kasala da mutuwar jiki yake tafiya tsirarun mutanan da suka rage a gurin suka dinga mika gaisuwarsu zuwa gareshi baya iya amsawa hannu kawai yake daga musu ya wuce.....Ya kusa isa kofar shi ya tuna da maganarsu da Maimartaba idan yake cewa idan ya fita ya bada umarnin fito da yaran, kai tsaye can ya nufa ya tarar da masu tsaron kofar suna shawagi a gurin, suna ganinsa suka zube gwiwa a kasa suke gaishe shi tare da sunkuyar da kansu kasa, a kasalance yace."Ku bude yaran nan su fito." Yana kare maganar ya juya da niyar barin gurin........."Yallabai babu lafiya." Da sauri ya juyo yana kallon mai maganar cikin rawar murya yace." 'Daya daga cikin yaran ce ta suma."
Gabansa ne ya fadi jin abinda bawan ya fada, da sauri ya dawo da baya, bawan ya matsa masa hanya ya shiga dakin, wayarsa ya kunna yana haskawa, ganinta a shema tamkar matacciya gabansa ya tsananta fad'uwa! da sauri ya tsuguna kusa da ita tare da umartar daya daga cikinsu ya kawo masa ruwa.
Ido ya tsirawa fuskarta yana mamakin tsayin lokacin data dauka a sume, hannunsa ya d'ora a kirjinta shuru babu alamun numfashi, ya sauke ajiyar zuciya tare dayin zaman durshan a gurin, kanta ya tallafo ya dora a cinyarsa, yana danna kirjinta a hankali a hankali, Bawan ne ya shigo da ruwa a hannunsa, ya kar'ba tare da umartarsa ya futa, bayan futar bawan sai ya shiga shafa mata ruwan a fuskarta da wuyanta yanayi yana kallon fuskarta, ya kai minti goma sha biyar yana aikin shafa mata ruwa a fuska bata motsa ba, jikinsa ya dinga kyarma yana addua Allah yasa itama ba mutuwa tayi ba.......Ruwan ya ajiye a hankali ya gyarata a jikinsa rigarta ya cire yayi saurin kauda kansa yana sauke wani irin numfashi, ya kai minti biyar yana kallo gefe guda kafin ya dan juyo a hankali yasa hannunsa a ruwan ya d'ebo ya yayyafa mata a jikinta ya cigaba da shafawa a kirjinta, hannunsa na mutsika nonowanta yana ya'ki da zuciyarsa kada ta rinjayeshi, yafi bukatar ta farfad'o tayi rayuwa a duniya.
Ido jawur ya cigaba da shafa mata ruwa a sassan jikinta yana sakin wani irin nishi mai wahalar gaske.

Ganin gashin idanunta na motsi yasa ya sauke ajiyar zuciya, alhmdullhi ya fad'a sai ya saurin de'bo ruwan da yawa ya yayyafa a fuskarta, a firgice ta bude idonta tana kalle-kalle a dakin, wayarsa ya dauka yana haskata, ta dinga kallonsa shima yana kallonta, jikinta tabi da kallo taga babu riga ballanatana breziya duk ya cire mata ga sanyin ruwa tana ji da tashin tsigar jiki, hannuwanta tasa ta rufe kirjinta zafafan hawaye suka shiga zubowa a fuskarta bakinta na rawa take so tayi magana amma ta kasa fargaba da tashin hankali sun dabaibayeta

A kasalance yace."Kina iya saka kayan ki ko na sanya miki.'' Kallon banza na watsa masa ina masa kallon macuci azzalami wato duk guje-guje na sai da yasan yanda yayi yazo ya cutar dani

Hannu nasa na goge hawayen fuskarta, Yace."Kisa kayanki mu fita daga cikin duhu da sauro." Banzar harara na watsa matsa tare da dauke kaina

"Kada ki 'kara hararata ballantana kiyi min tsaki sai ranki ya 'baci.''' A zafafe nace" Sai me idan raina ya 'baci! ashe da sauran 'bacin rai bayan wannan da nake ciki, wato ka samu labarin a inda nake shine ka biyo dare kazo ka biya bukatarka a kaina ko."!?

Kallona yay da yanayi na 'bacin rai a tare dashi yace."Idan ina so nayi wani abu dake ba sai na biyo dare na fakaici idanun mutane ba, ko can baya ni ne banga dama ba banyi ra'ayin yin abinda nake so dake ba dan haka ki daina wannan maganar sam ba wannan dalilin ne ya shigo dani ba''

A fusace! nace"To ai sai ka fada min dalilin daya shigo da kai! gashi nan ka tu'be min riga kaima ka cire botiran rigarka wane irin iskanci ne yasa zaka tu'be min rigata bayan bana cikin hayyacina."

"Sumayya bana neman wata magana mai tsayi na fada miki ba wannan dalilin ne ya shigo dani dakin nan ba ki yarda ko kada ki yarda be dame ni ba ki tashi kisa kayanki mu fita daga cikin duhu."

Tsaki! mai karfi naja nace"Babu abinda zan......Bakina ya murd'e min ya tsira min jajayen idanunsa, nan na hango tsantsar damuwa da tashin hankali a cikinsu.

Mutsika min le'buna yake cike da muguna hawaye suka dinga karakaina a kuncina, sai da ya gaji dan kansa ya sakar min baki.
Kaina na sunkuyar kasa hawayen azaba na zubo min .

Rigata ya dauko zai saka min da sauri na daga hannu zan mareshi! ri'ke min hannu yayi ya murd'e da kyau! yace." Marina zakiyi irin na kwanakin baya." Shuru nayi ina kallonsa, yace."Ki kiyaye aikata hakan idan kuma kin'ki watarana kina ji kina gani zan 'balla miki hannu babu abinda ya dameni." Yana gama maganarsa ya jefa min rigata a jiki da fadin "Dallah dauka kisa ki tashi."
Babu yanda na iya haka na dauki rigar nasa hannuna daya murde sai zafi yake min.

Mikewa tsaye yayi yana mayar da botiran rigarsa, yace."Ina d'aya yarinyar take?" Shuru nayi masa, ya buga min wata irin tsawa da fadin"Ba magana nake ba." Nace"Muddubo yazo ya fita da ita."
Shuru yay yana kallona na dauke kaina tare da nufar kofar fita, sawun tafiyarsa naji a bayana da sauri na 'kara gabana ina addua a cikin zuciyata

Jugum-jugum! na samu iyayenta Tambaya taci kuka ta koshi kanta sai ciwo yake mata, ina shigowa suka mike tsaye suna godewa Allah! Tambaya rungumeni tayi tana kuka hade da dudduba jikina, nace"Tambaya dan Allah ki daina kuka wuya bata kisa kuma Allah zai bayyana gaskiya dukkaninku ku kwantar da hankalinku

Babana ya rike hannuna a sanyaye yace.''Sumayya dole hankalinmu ya tashi ana tuhumarki da aikata mummunan abu ba zamu ta'ba samun nutsuwa ba sai gaskiya ta bayyana babu shakka duk wanda ya aikata wannan abu bashi da imani tunda gashi yayi nasarar kashe mai rai."

Cikin faduwar gaba nace"Waye ya mutu a cikinsu.'' A sanyaye yace."Isa ya rigamu gidan gaskiya yanzu haka gawarsa na ajiye sai da safe za'ayi jana'izarsa." Zubewa nayi a gurin ina fadin "Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un!! Tambaya tasa hannu ta rungumo ni ina kuka muka shiga daki tana rarrashina.

Yanda naga dare haka naga rana, tsabar fargaba da tashin hankali ya hanani rintsawa, 'bangaran Magajin Sarki ma hakan take a zaune ya kwana yana tunanin yanda zai 'bullowa al'amarin babu shakka akwai saka hannun Muddibo a cikin faruwar wannan al'amarin ya rufewa iyayensa maganar ne saboda gudun tashin hankali dan mutukar Maimartaba ya tabbatar da cewa Muddibo ne ya aikata wannan mugun abun to zai dauki mataki akansa kamar yanda yake yankewa duk mai laifi hukunci, 'Bangaran Ciroma da iyalansa kuwa zasu sake 'kullatarsa dashi da iyalansa gaba gami da 'kiyayyar juna zata sake nunkuwa akan tada shiyasa kawai yace matsalar ta faru ne daga man da'akayi suyar doyar dashi, amma dole ya zauna da yarinyar da tayi aikin ya tsorarta da ita domin ya tabbatar da zarginsa.

Kasa tsayawa nayi na karya kummalo na nufi sashensa, nan na samu Haruna da Hamza a harabar gurin sunyi jugum-jugum! ganinsu ya sanya hawaye suka 'kwace min koda na karasa inda suke kasa magana nayi kallonsu kawai nake ina share hawaye.
Chapter 41 · 0% Book details