Sashe 83
Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yace."To babu komai Mamma ai kamar yau zamu dawo tunda yanzu gashi har munyi sati guda." Tace."To masha Allah ina rokon Ubangiji Allah ya dawo daku lafiya.'' Ya amsa da ''ameen ya Allah." kashe wayar tayi ta juyo tana kallona da murmushi a fuskarta tace"Kinji yanda mukayi da mijinki ko." nace"Naji mamma nima zanfi so na dawo nan din." Tace"To shikkenan bayan sallar isha'i sai kuje tare da Jakadiya ki dauko abunda zaki bukata." nace"To godiya nake ranki ya dad'e."
Tana wani irin kuka take fad'in "Wallahi na daina yarda kana amfani dani da kwaroran roba(Condem) sai kace karuwa zaka dinga gudun haihuwa dani wato ita wacce kake so ka bari ta dauki ciki ni kuma ka yaudareni ka dibga min kwayoyi yanzu kuma ka dawo kana sa condem to na gane yanxu wallahi idan baka daina ba sai na tona maka asiri."! cikin kuka na fitar hayyaci take maganar."
A fusace! yace." Lawisa kada ki fasa tona min asiri a gida idan kin fad'awa iyayena abinda yake faruwa a tsakaninmu wallahi sai kinyi mamakin hukuncin da zanyi miki! kuma bazan cire condem ba duk abinda zakiyi sai dai kiyi."
Da sauri ta janye jikina tana kuka tace"Ni kuma wallahi na daina amincewa da kai kana cutar dani da mugun halinka sai Allah ya saka min."!! mari ya kwada mata yana huci! yace."ai baki fi karfina ba yanzu zan biya bukata ko kina so ko bakyaso." kafin tayi wani yunkuri ya turmushe ya shiga biyawa kansa bukata ba tare da ya cire condem din ba.........sai da yayi me isar sa sannan ya daga ta yaje yai wanka ya fito ya shirya jikinsa ya fita ya barta cikin yanayi na tsantsar damuwa da tashin hankali.
Tare mukaje gurina da Jakadiya ta zauna a falo ni kuma na nufi dakina domin harhad'a 'yan kayan da zan bukata, ina sanya 'kafata a cikin d'akin santsi ya kayar dani! wata irin fad'uwa nayi cikina ya daki! 'kasa da karfin gaske! rintse idona nayi tare da kiran sunan Allah da karfi! dakin ne yayi duhu! cikin karfin hali nayi yunkurin mikewa! naji saukar duka akaina! fad'uwa nayi ina kiran sunan Allah da karfin gaske nace"Jakadiya."!!!!!! a guje! ta shigo dakin tana amsawa tare da laluben mukunnin fitila, ji tayi an bangajeta an fita a guje! salati tasa da sauri ta kunna fitilar! dakin yayi haske! ganin ta a kwance tana murkususu yasa hankalinta ya tashi! zubewa tayi a gabanta tana kiran sunanta jikinta sai rawa yake.......Cikin karfin hali nace"Jakadiya mutuwa zanyi."!! hawaye ta share tace"Ba zaki mutu ba sumayya Allah zai toni asirin duk wanda yake kokarin cutar dake......da sauri ta mike ta fita nan ta samu masu tsaron gurin a tsaitsaye suna magana tace''Ina fata dai kun gane wanda ya fito yanzu." gabadayansu suka ce "Babu samu nasarar kama ta ma dan kayan dake jikinta irin na bayi ne shiyasa ba muyi tunanin wani abuba." Jakadiya da sauri ta bar gurin dan ba taga amfanin tsayuwarta ba.
Su Mariya ne suka rufu akanta suna mata firfita gabadayansu hankalinsu ya tashi da abinda ya faru da uwar dakin nasu, suna cikin dakinsu suka jiyo ihun ta dalilin da yasa kenan suka fito a gigice!
Ganin jini ya 'bata mata zanin jikinta yasa hankalinsu ya kara tashi shikkenan suma suna cikin gariri dole a tambayesu yanda akayi suka bari ta shigo gurin har ta samu nasara.
Mamma da Jakadiya suka shigo dakin hankalinsu a tashe! lokacin Sumayya ta galabaita mutuka, mamma ganinta cikin mugun yanayi yasa ta fashe da kuka rungumeta tayi jikinta duk ya 'baci da jini tace"Sumayya Allah ya saka miki." jin miryarta yasa na 'kan'kame! hannunta ina nishi! nace"Mamma Lauratu ta samu nasara akaina shikkenan nasan sun kashe min baby." wasu zafafan hawaye suka shigo zubo min........Rungumeni tayi tana tofa min adduoi...cikin wannan hali Shatima ya shigo hankalinsa a tashe yace."Mamma ku kamata muje asibiti a dubata." Mamma ta mike jikinta duk ya mutu ta riga ta futar da rai da cikin da ta kwallafa rai dashi.......
Jin cewar matar mai asibitin ce yasa likitoci suka rufu a kanta sai da suka tabbatar da cewa komai yayi daidai sannan hankalinsu ya kwanta.........Mamma ajiyar zuciya ta sauke mai sanyi lokacin da ta gama sauraran jawabin da Dr Sadiya take mata, tace"Alhamdullh dr dama ni fargabata kada ace cikin ya zube tunda dai Allah ya takaita to sai mugodewa masa kuma sannuku da kokari Allah ya saka muku da alkairi." Dr Sadiya tace"babu komai ranki ya dade an jima kadan zaku iya shiga ku dubata yanzu tana bacci." Mamma tace"To babu damuwa." Dr Sadiya ta bude musu wani daki suka zauna a ciki suna jajanta al'amarin..........A daran Maimartaba da Waziri tare da Mahaifinta Lawi sai da suka zo asibitin suka duba ta basu tafi ba sai da ta tashi suka tabbatar da lafiyarta sannan suka tafi ita kuwa Mamma kasa tafiya tayi tasa Shatima ya shedawa D'an uwan nasa abinda yake faruwa, lokacin yayi ta kiran wayarsa bata shiga tace ya bari da safe sai ya kirashi ya fada masa...............
Hannuwana ta rike tace"Sumayya ba kuka za kiyi ba Allah zaki godewa daya kare ki daga sharrin masu sharri Kiyi shuru ki kwantar da hankalinki ki fada min dukkanin abinda yake faruwa."
Hawaye na share a hankali na soma yi mata bayanin abubuwan da suka dinga faruwa a tsakanina dasu.
Hawaye ta share tana girgiza kanta tace" Wannan rashin imani da rashin tsoron Allah na hajiya karima yana bani mamaki! wato ashe bata hakura ba shine take so ta dauki fansa akanki ai bake kika sa aka rataye danta ba da zata dinga bibiyarki da sharri! ki daina kuka sumayya insha Allah sunyi na farko sunyi na karshe sai an dauki mataki mai tsauri akansu sai sunyi da sun sanin abinda suka aikata miki, dama ita wannan Lauratu shaidaniya ce dan ta kashe mutum ba sabon abu bane a gurinta to wannan karon sai tayi nadamar abinda ta aikata.
Da asubah bayan ta idar da sallah, kira ya shigo wayarta koda ta duba sai taga yaron nata ne a nutse ta daga tare dayin sallama............Murya a sha'ke Lawisa ta amsa tare da fad'in "Mamma ina fata kun tashi lafiya." a sanyaye tace"Lafiya lau Lawisa ina fatan kuna nan lafiya?" kuka ta fashe dashi! Mamma hankalinta ya tashi tace"Lawisa lafiya kike kuka ina babana yake."? Lawisa kasa magana tayi ta cigaba da gurshe'ken kukanta.
Mamma jikinta dik yayi sanyi tace"Lawisa ki daina kuka ki fada min abinda ke faruwa ko fada kukayi dashi ne."? murya a sar'ke tace"Mamma ki gafarce ni nasan idan kikaji abinda yake tafe dani hankalin ki zai tashi." Tace"Lawisa ai yanzu hakama a cikin tashin hankali nake dan jiya da daddare Kanwar mamakin Lauratu ta shiga har gurin Sumayya tayi yunkurin cutar da ita dan yanzu hakama muna asibiti."
Lawisa taji gwiwarta tayi sanyi jikinta na rawa tace"Mamma dan Allah kuyi hakuri Aunty Lauratu ba zata aikata haka ba." cike da mamaki tace"Lawisa kin san halin kanwar mamanki nima na san halinta na kuma nasan abinda za tayi da wanda ba zata aikata ba Lauratu shigarta prison nawa saboda aikata munana ayyuka shine Mahaifiyarki ta hada baki da ita suke bibiyar rayuwar Sumayya saboda su dauki fansa akan abinda ya faru."
Lawisa kuka kawai take gabadaya kanta ya kulle ta rasa wane irin tunani za tayi dama tasan dole sai asirinsu ya tonu shiyasa tun kafin su aikata ta hanasu saboda gudun abinda zai faru dasu.
Mamma tace"Ki daina kuka ki fada min abinda ya hadaki da mijinki." Hawaye ta share ta dan juya ta kalli toilet yana ciki yana wanka bayan ya gama sasakarta wallahi tai rantsuwa da Allah sai ta tona masa asiri tunda ya kasance azzalimi.
Cikin kuka da nadama ta shiga fada mata abubuwan da suke faruwa. Mamma ta shiga tsantsar tashin hankali dajin abinda Lawisa ke fada mata, babanta shike gudun haihuwa har yana saka kwaroron roba sabida kada ya samu zuria! wannan al'amari yayi masifar tashin hankalinta, waiwaya tayi bayanta tana kallon Sumayya dake bacci! cikin zuciyarta tace"Wannan yarinya babu abinda zance dake a duniyar nan kinyi min hallaci tabbas samun irin masu halinki zaiyi wahalar gaske........Ajiyar zuciya ta sauke tace"Lawisa daina kuka ki saurareni." hawaye ta share tace"Ina jinki Mamma." Tace"Kiyi hakuri kinji ko insha Allah haka ba zata sake faruwa ba, sannan duk ranar daya kuma zuwa zai sadu dake da kwaroro a jikinsa kada ki amince dashi! idan kun dawo gida zan dauki mataki akansa inaso kuma ki rufa asirin maganar nan dan idan kin fito kin fada kin tonawa kanki asiri sannan kuma kin tona asirin mijinki amma hakikanin gaskiya babana bai kyauta miki ba amma kada ki damu zan dauki mataki akansa." Zuciyarta tayi sanyi tace"To shikkenan Mamma nagode sosai Allah ya kara girma." Sallama sukayi ta kashe wayar tana jin sanyi a cikin ranta, tana juyowa suka hada ido ya fito tun dazu kuma komai kunnensa. hannu ya mika mata da fadin" Bani waya ta." jiki a sanyaye ta mika masa ya kar'ba yana kallonta yace."Sai da kika fada mata ko."? hawaye ta goge tace"Ya za'ayi ba zan fada mata ba kana cutata.'' Yace'' To kin janyowa kanki saki." kallonsa tai gabanta na mugun faduwa! yace." Na fada miki cewa duk ranar da kika kuskura kika fitar da sirrina wani yaji to zan miki hukunci da bakiyi tsammani ba munyi haka da Sumayya kuma ta kiyaye ke da yake baki da mutunci kika kira mahaifiyata ko? to kisa a ranki cewa daga yau ke ba matata bace."!! Ihu! ta kurma! ta zube a gurin tana kuka da rokonsa akan kada ya saketa ya tausaya mata, fizge kafarsa yayi yasa kayansa ya fita daga dakin ransa a mugun bace.
Tana wani irin kuka take fad'in "Wallahi na daina yarda kana amfani dani da kwaroran roba(Condem) sai kace karuwa zaka dinga gudun haihuwa dani wato ita wacce kake so ka bari ta dauki ciki ni kuma ka yaudareni ka dibga min kwayoyi yanzu kuma ka dawo kana sa condem to na gane yanxu wallahi idan baka daina ba sai na tona maka asiri."! cikin kuka na fitar hayyaci take maganar."
A fusace! yace." Lawisa kada ki fasa tona min asiri a gida idan kin fad'awa iyayena abinda yake faruwa a tsakaninmu wallahi sai kinyi mamakin hukuncin da zanyi miki! kuma bazan cire condem ba duk abinda zakiyi sai dai kiyi."
Da sauri ta janye jikina tana kuka tace"Ni kuma wallahi na daina amincewa da kai kana cutar dani da mugun halinka sai Allah ya saka min."!! mari ya kwada mata yana huci! yace."ai baki fi karfina ba yanzu zan biya bukata ko kina so ko bakyaso." kafin tayi wani yunkuri ya turmushe ya shiga biyawa kansa bukata ba tare da ya cire condem din ba.........sai da yayi me isar sa sannan ya daga ta yaje yai wanka ya fito ya shirya jikinsa ya fita ya barta cikin yanayi na tsantsar damuwa da tashin hankali.
Tare mukaje gurina da Jakadiya ta zauna a falo ni kuma na nufi dakina domin harhad'a 'yan kayan da zan bukata, ina sanya 'kafata a cikin d'akin santsi ya kayar dani! wata irin fad'uwa nayi cikina ya daki! 'kasa da karfin gaske! rintse idona nayi tare da kiran sunan Allah da karfi! dakin ne yayi duhu! cikin karfin hali nayi yunkurin mikewa! naji saukar duka akaina! fad'uwa nayi ina kiran sunan Allah da karfin gaske nace"Jakadiya."!!!!!! a guje! ta shigo dakin tana amsawa tare da laluben mukunnin fitila, ji tayi an bangajeta an fita a guje! salati tasa da sauri ta kunna fitilar! dakin yayi haske! ganin ta a kwance tana murkususu yasa hankalinta ya tashi! zubewa tayi a gabanta tana kiran sunanta jikinta sai rawa yake.......Cikin karfin hali nace"Jakadiya mutuwa zanyi."!! hawaye ta share tace"Ba zaki mutu ba sumayya Allah zai toni asirin duk wanda yake kokarin cutar dake......da sauri ta mike ta fita nan ta samu masu tsaron gurin a tsaitsaye suna magana tace''Ina fata dai kun gane wanda ya fito yanzu." gabadayansu suka ce "Babu samu nasarar kama ta ma dan kayan dake jikinta irin na bayi ne shiyasa ba muyi tunanin wani abuba." Jakadiya da sauri ta bar gurin dan ba taga amfanin tsayuwarta ba.
Su Mariya ne suka rufu akanta suna mata firfita gabadayansu hankalinsu ya tashi da abinda ya faru da uwar dakin nasu, suna cikin dakinsu suka jiyo ihun ta dalilin da yasa kenan suka fito a gigice!
Ganin jini ya 'bata mata zanin jikinta yasa hankalinsu ya kara tashi shikkenan suma suna cikin gariri dole a tambayesu yanda akayi suka bari ta shigo gurin har ta samu nasara.
Mamma da Jakadiya suka shigo dakin hankalinsu a tashe! lokacin Sumayya ta galabaita mutuka, mamma ganinta cikin mugun yanayi yasa ta fashe da kuka rungumeta tayi jikinta duk ya 'baci da jini tace"Sumayya Allah ya saka miki." jin miryarta yasa na 'kan'kame! hannunta ina nishi! nace"Mamma Lauratu ta samu nasara akaina shikkenan nasan sun kashe min baby." wasu zafafan hawaye suka shigo zubo min........Rungumeni tayi tana tofa min adduoi...cikin wannan hali Shatima ya shigo hankalinsa a tashe yace."Mamma ku kamata muje asibiti a dubata." Mamma ta mike jikinta duk ya mutu ta riga ta futar da rai da cikin da ta kwallafa rai dashi.......
Jin cewar matar mai asibitin ce yasa likitoci suka rufu a kanta sai da suka tabbatar da cewa komai yayi daidai sannan hankalinsu ya kwanta.........Mamma ajiyar zuciya ta sauke mai sanyi lokacin da ta gama sauraran jawabin da Dr Sadiya take mata, tace"Alhamdullh dr dama ni fargabata kada ace cikin ya zube tunda dai Allah ya takaita to sai mugodewa masa kuma sannuku da kokari Allah ya saka muku da alkairi." Dr Sadiya tace"babu komai ranki ya dade an jima kadan zaku iya shiga ku dubata yanzu tana bacci." Mamma tace"To babu damuwa." Dr Sadiya ta bude musu wani daki suka zauna a ciki suna jajanta al'amarin..........A daran Maimartaba da Waziri tare da Mahaifinta Lawi sai da suka zo asibitin suka duba ta basu tafi ba sai da ta tashi suka tabbatar da lafiyarta sannan suka tafi ita kuwa Mamma kasa tafiya tayi tasa Shatima ya shedawa D'an uwan nasa abinda yake faruwa, lokacin yayi ta kiran wayarsa bata shiga tace ya bari da safe sai ya kirashi ya fada masa...............
Hannuwana ta rike tace"Sumayya ba kuka za kiyi ba Allah zaki godewa daya kare ki daga sharrin masu sharri Kiyi shuru ki kwantar da hankalinki ki fada min dukkanin abinda yake faruwa."
Hawaye na share a hankali na soma yi mata bayanin abubuwan da suka dinga faruwa a tsakanina dasu.
Hawaye ta share tana girgiza kanta tace" Wannan rashin imani da rashin tsoron Allah na hajiya karima yana bani mamaki! wato ashe bata hakura ba shine take so ta dauki fansa akanki ai bake kika sa aka rataye danta ba da zata dinga bibiyarki da sharri! ki daina kuka sumayya insha Allah sunyi na farko sunyi na karshe sai an dauki mataki mai tsauri akansu sai sunyi da sun sanin abinda suka aikata miki, dama ita wannan Lauratu shaidaniya ce dan ta kashe mutum ba sabon abu bane a gurinta to wannan karon sai tayi nadamar abinda ta aikata.
Da asubah bayan ta idar da sallah, kira ya shigo wayarta koda ta duba sai taga yaron nata ne a nutse ta daga tare dayin sallama............Murya a sha'ke Lawisa ta amsa tare da fad'in "Mamma ina fata kun tashi lafiya." a sanyaye tace"Lafiya lau Lawisa ina fatan kuna nan lafiya?" kuka ta fashe dashi! Mamma hankalinta ya tashi tace"Lawisa lafiya kike kuka ina babana yake."? Lawisa kasa magana tayi ta cigaba da gurshe'ken kukanta.
Mamma jikinta dik yayi sanyi tace"Lawisa ki daina kuka ki fada min abinda ke faruwa ko fada kukayi dashi ne."? murya a sar'ke tace"Mamma ki gafarce ni nasan idan kikaji abinda yake tafe dani hankalin ki zai tashi." Tace"Lawisa ai yanzu hakama a cikin tashin hankali nake dan jiya da daddare Kanwar mamakin Lauratu ta shiga har gurin Sumayya tayi yunkurin cutar da ita dan yanzu hakama muna asibiti."
Lawisa taji gwiwarta tayi sanyi jikinta na rawa tace"Mamma dan Allah kuyi hakuri Aunty Lauratu ba zata aikata haka ba." cike da mamaki tace"Lawisa kin san halin kanwar mamanki nima na san halinta na kuma nasan abinda za tayi da wanda ba zata aikata ba Lauratu shigarta prison nawa saboda aikata munana ayyuka shine Mahaifiyarki ta hada baki da ita suke bibiyar rayuwar Sumayya saboda su dauki fansa akan abinda ya faru."
Lawisa kuka kawai take gabadaya kanta ya kulle ta rasa wane irin tunani za tayi dama tasan dole sai asirinsu ya tonu shiyasa tun kafin su aikata ta hanasu saboda gudun abinda zai faru dasu.
Mamma tace"Ki daina kuka ki fada min abinda ya hadaki da mijinki." Hawaye ta share ta dan juya ta kalli toilet yana ciki yana wanka bayan ya gama sasakarta wallahi tai rantsuwa da Allah sai ta tona masa asiri tunda ya kasance azzalimi.
Cikin kuka da nadama ta shiga fada mata abubuwan da suke faruwa. Mamma ta shiga tsantsar tashin hankali dajin abinda Lawisa ke fada mata, babanta shike gudun haihuwa har yana saka kwaroron roba sabida kada ya samu zuria! wannan al'amari yayi masifar tashin hankalinta, waiwaya tayi bayanta tana kallon Sumayya dake bacci! cikin zuciyarta tace"Wannan yarinya babu abinda zance dake a duniyar nan kinyi min hallaci tabbas samun irin masu halinki zaiyi wahalar gaske........Ajiyar zuciya ta sauke tace"Lawisa daina kuka ki saurareni." hawaye ta share tace"Ina jinki Mamma." Tace"Kiyi hakuri kinji ko insha Allah haka ba zata sake faruwa ba, sannan duk ranar daya kuma zuwa zai sadu dake da kwaroro a jikinsa kada ki amince dashi! idan kun dawo gida zan dauki mataki akansa inaso kuma ki rufa asirin maganar nan dan idan kin fito kin fada kin tonawa kanki asiri sannan kuma kin tona asirin mijinki amma hakikanin gaskiya babana bai kyauta miki ba amma kada ki damu zan dauki mataki akansa." Zuciyarta tayi sanyi tace"To shikkenan Mamma nagode sosai Allah ya kara girma." Sallama sukayi ta kashe wayar tana jin sanyi a cikin ranta, tana juyowa suka hada ido ya fito tun dazu kuma komai kunnensa. hannu ya mika mata da fadin" Bani waya ta." jiki a sanyaye ta mika masa ya kar'ba yana kallonta yace."Sai da kika fada mata ko."? hawaye ta goge tace"Ya za'ayi ba zan fada mata ba kana cutata.'' Yace'' To kin janyowa kanki saki." kallonsa tai gabanta na mugun faduwa! yace." Na fada miki cewa duk ranar da kika kuskura kika fitar da sirrina wani yaji to zan miki hukunci da bakiyi tsammani ba munyi haka da Sumayya kuma ta kiyaye ke da yake baki da mutunci kika kira mahaifiyata ko? to kisa a ranki cewa daga yau ke ba matata bace."!! Ihu! ta kurma! ta zube a gurin tana kuka da rokonsa akan kada ya saketa ya tausaya mata, fizge kafarsa yayi yasa kayansa ya fita daga dakin ransa a mugun bace.