Sashe 3
Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa Dashan Allah✊ðŸ?)
5&6
Bayan mun koma gurin tsayuwar mu mun nutsu sai maimartaba ya umarci yaron nasa daya fito ya nunawa jama'a farin cikinsa na dawowarsa masarauta lafiya....A lokacin idanun jamaa yayi caaa! a kansa kowa kokarinsa yayi tozali dashi, ni dai sunkuyar da kaina qasa nayi saboda jin yanda gabana yake faduwa haka kurrum naji bana bukatar kallonsa ba dan komai ba sai dan mugun halinsa na rashin ganin darajar mutane........Wani bafade ne yay gaggawar gyara masa abin magana ya saita masa daidai bakinsa, kamar wanda akayi wa dole yay gyara sai da yaja lokaci tukkuna cikin rashin walwala a fuskarsa da maganarsa yace."Alhamdullilah Allah kaine abin godiya. hakika nayi farin ciki mutuka daga dawo dani gida cikin koshin lafiya gami da tarin nasarori masu yawa." shiru yayi tare da sunkuyar da kansa qasa. Jin yayi shiru yasa nayi saurin dago kaina ina kallon gurin da yake, gani nayi kansa a sunkuye yana kallon 'kasan gurun tamkar me neman wani abu......Tsaki naja a cikin zuciyata nace"Wannan anyi d'an wulaqanci ya sani sarai jama'a shi suke sauraro amma ya fara magana yayi shiru, kaina na d'auke ina jin takaicin abinda yake......Gyaran murya ya kuma yi kafin ya cigaba da magana..."Sannan kuma nayi farin cikin samun iyayena da 'yan uwana da dukkanin wanda ke k'ark'ashin masarautar nan lafiya hakika naji dadi sosai da ganin yanda kuka fito 'ya'yanku da jikokin ku kuka nuna farin cikin ku dangane da dawowa ta gida Nagode sosai inayi muku fatan alkairi." yana k'are maganarsa ya janye bakinsa daga gurin abin maganar can kusa da Waziri ya koma ya tsaya har yanzu babu fara'a a fuskarsa.
Hayaniya da kace kace ne ya cika gurin, Wani bafade yayi tsawa tare da umartar kowa yay shuru kafin minti biyu gurin yayi tsit! Maimartaba ya miqe a nutse ya karasa gurin da abin magana yake, kafin ya fara magana sai da ya d'aga hannuwan sa sama alamar gaisuwa ga tarin jama'ar dake gurin.....Gurin ya sake rikicewa da hayaniya kowa sai fadin albarkacin bakinsa yake akan maimartaba. Da kyar aka samu sukayi shuru suka bar maimartabar yayi jawabi gami da miqa godiyarsa ga Allah ya kuma miqa godiyarsa ga tarin manyan mutanan da suka samu hallatar gurin suma bayin dake karkashin masarautarsa sai da ya miqa godiyarsa a gurinsu sannan ya koma ya zauna gurin zamansa, Baba Waziri yazo yay nasa jawabin Galadima da Ciroma suma sukayi nasu daidai gwargwado sannan maimartaba ya rufe taron da addua, ya miqe da niyyar shiga cikin gida fadawa ne suka kewaye shi suna ta gyara kintsi dai."!! Gurin ya karad'e da bushebushe gami da tashin muryoyin maro'ka da hayaniyar jama'a, sai da Sarki da muqarrabansa suka shiga gida tukkuna aka samu lafiya, jama'ar gurin suka watse kowa ya nufi 'bangaran da yake a cikin gidan.........Nida iyayena Cikin yanayi na ciwo muka shiga gurin mu, da sauri muka zaunar dashi, Tambaya ta ri'ke kafadarsa ni kuma hankali a tashe naje na d'ebo masa ruwa jiki na kyarma nazo na tallafo kansa ina kokarin bashi ruwan, bakinsa ya bud'e ina sa masa ruwan yana dawowa, lokaci guda zuciyoyinmu suka karye nida mahaifiyata hawaye muka fara, cikin karfin hali gami da kokarin janyo maganar yace."Ku daina kuka bashi ne abinda nake bukata ba."!
Zama nayi kusa dashi na rike hannunsa har yanzu hawaye bai da zubo min ba nace"Baba wai dan Allah me yake damunka kwana biyu ka'ki lafiya kullum cikin rashin kuzari da karfin jiki gashi kuma ka'ki ka bari a kira mai kula da lafiya yazo ya duba ka."
A hankali yace."Sumayya ba wani ciwo mai tsanani bane yake damuna zazza'bi ne mai zafi sai hajijiya gami da rashin kuzari to ni dik a tunani na ko shawara ce shiyasa na mayar da hankalina gurin shan maganinta amma yanzu ina ganin dole kije ki kira d'aya daga cikin masu kula da lafiya yazo ya dubani dan ni kadai nasan abinda nakeji a cikin jikina.
Tambaya hawaye ta share a sanyaye ta kalleni da fadin"Kiji can bangaran masu kula da lafiyar ki kirawo daya daga cikinsu yazo ya dubashi ni kaina jikina yay sanyi da wannan rashin lafiyar tasa a tsaitsaye fa ya kai sati hudu yanayi duk da yana shan maganin shawarar babu sauki kullum jikin rikicewa keyi."
Miqewa nayi da sauri nace "Bari naje can gurinsu na samesu." takalma na zura da saurin gaske na kama hanyar sashen masu kula da lafiyar gabad'aya bana cikin hayyacina ina tsananin kaunar mahaifina shiyasa rashin lafiyarsa ta d'aga min hankali mutuka.
"Sumayya." Sunana naji an kira da sauri na tsaya ina waigen bayana.
babu walwala a fuskarsa ya karaso inda nake tsaye kai tsaye yace."Ina Lawi yake ya bar aikinsa kamata yayi ace kafin mu fita gurin taro ya zubawa dokuna abinci yanda zai ishesu yanzu yanzu na shiga gurin na tarar da gabad'aya babu abinci a gabansu idan fa maimartaba ya samu labarin abinda yake zai fuskanci hukunci."
A marairace nace"Buba dan Allah kayi hakuri kada ka kai 'korafi wallahi babana bashi da lafiya tsayin sati hudu yake ciwo a tsaitsaye dukkanin abinda yake dauriya kawai yake dan Allah ka taimaka masa kana bawa dawakan abincin kafin yaji sauqi.
"Ke! saurara da wannan maganar.'' Nayi saurin kallonsa kwalla na kokarin zobomin, Ya cigaba da cewa''Kowa da kika gani akawai aikinsa a masarautar nan nawa aikin ma yafi nasa wahala tinda ni kwana nake a tsaye ina zirga zirga banga dalilin da zai sanya na d'auki nauyin wani na d'orawa kaina ba, ke aikin me kike da ba zaki d'auki nauyin mahaifinki ba kafin ya samu lafiya.
Hannu nasa na goge hawayen da suka zubo min nace" Shikkenan zanyi kokari ganin na dauki ragamar kula da dawakan kamar yanda babana yake yi amma ka san dai muna zaman karatu ranaku uku a sati ko kuma idan mun zauna tin safe sai yamma muke tashi.
D'aga kafad'a yay yace."Ke zaki tsarawa kanki yanda al'amura zasu tafi ni dai na fad'a miki ku kula da aikin ku kada maimartaba yaji wata magana.
Ajiyar zuciya na sauke mai zafi! nace"Shikkenan Buba nagode sosai insha Allahu zan iyakacin bakin kokarina." Gyda kansa yayi ya bar gurin, nima da sauri na wuce domin nufar inda nayi niyya.
Na jima a tsaye a bakin kofar d'akin nasu ina sallama kafin naji an amsa da fadin"Ko wacece ta shigo.'' Jim nayi ina tunanin shiga dan gabad'ayansu maza ne a ciki ina ganin kamar hakan bai dace ba.
Sallama na sakeyi, naji anyi min tsawa! da fad'in "Wai wacece take sallama ne ki shigo ki fadi uzirinki." Shahada nayi na tura kaina dakin....wasu na kwance kan katifunsu wasu kuma na zazzaune daga su sai gajerun wanduna.
Daga bakin kofa na tsaya nace"Dan Allah d'aya yazo ya duba babana Lawi bashi da lafiya."
Shuru sukayi min kowa ya cigaba da sabgarsa, raina ya 'baci! nace"Magana fa nakeyi muku kuna jina." 'Dantala ya zaburo min da hayaniya yace."Ke! babu wanda zai katse abinda yake a cikinmu yaje ya duba babanki idan kina so ayi miki abinda kike so ki shigo ciki muna bukatarki."
Cike da mamaki nake kallonsu nace"aikin ku ne fa mai zai sanya kuce sai nayi muku wani abu sannan zakuyi to ni ba 'yar iska bace idan kun saba latsa 'yan matan dake masarautar to ni ba' irinsu bace kuma wallahi idan bakuyi wasa ba yanzu zanje fadar sarki na sheda masa abinda kuke aikatawa..........A fusace! naga ya miqe yayo kaina zai mareni na kauce da sauri ina kare fuskata....wanda yake da sauqin halin cikinsu ne ya miqe tare da zira rigarsa ya kalleni da fadin" Shige muje na duba jikin mahaifin naki." Da sauri na fita daga dakin gabana sai faduwa yake......Tafiya nake zugwi zugwi ina mamakin al'amarin, kawai naji ana ta'ba min mazaunai! Da sauri na juyo ina kallonsa, murmushi yayi ya sosa kansa ido jawur yace."A gaskiya Sumayya Allah yayi miki baiwa mai mutukar daukar hankali, kina da duk abinda d'a namiji ke bukata a jikin mace kirjinki a cike yake dam-dam uwa uba mazaunai masu masifar rikimin lissafi wallahi tunda kika shiga dakinmu sha'awata ta tashi dan Allah ki bani damar mallakar wannan jikin naki wanda yake kokarin fitar dani hayyacina.
Kallonsa kawai nake wani 'katoton abu ya tokare min a ma'koshi nace"Yanzu Usman ashe kaima halinku d'aya dasu Dantala a zahiri inayi maka kallon salihi ashe kaima baka da d'abi'a mai kyau Usuman dan Allah meye amfanin lalata da kukeyi da 'ya'yan mutane idan fa masarauta ta samu labarin abinda kukeyi ba zakuji dad'i ba.
A sanyaye ya sosa kansa cikin jin kunya yace."Sumayya dan Allah kiyi hakuri wallahi ni ban fiya haikewa 'yan matan masarautar nan ba su Dantala ne masuyi kema yanzu hankalina ne ya tashi sosai shiyasa na gaza hakuri na kai hannuna mazaunanki amma kiyi hakuri dan Allah kada naji maganar a bakin kowa.
Cikin takaici na girgiza kaina tare da juyawa na cigaba da tafiya raina a masifar 'kuntacce.
To koda Usuman ya duba babana nan ya gano cewa hawan jini ne ke damunsa hankalinmu ya tashi nida tambaya muka dinga kuka dan mun riga mun san ciwon hawan jini babban ciwo ne gani muke kamar mun kusa muyi bankwana dashi shiyasa gabadaya hankalinmu ya tashi....Usuman ganin duk muna hawaye yasa ya rarrashe mu tare da bamu shawarwarin yanda zamu kula dashi da lafiyarsa yace "Insha Allahu mutukar aka bi dokar da ake bukata masu dauke lalurar suka bi to zai samu lafiya, Ya miqe tare da fad'in " Zaije yanzu ya kawo masa magungunan da zasu taimaka masa...godiya mukayi masa muna zubar da hawayen tausayi......
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALEðŸ’_ *[email protected]*
*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊�*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_
*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa Dashan Allah✊ðŸ?)
5&6
Bayan mun koma gurin tsayuwar mu mun nutsu sai maimartaba ya umarci yaron nasa daya fito ya nunawa jama'a farin cikinsa na dawowarsa masarauta lafiya....A lokacin idanun jamaa yayi caaa! a kansa kowa kokarinsa yayi tozali dashi, ni dai sunkuyar da kaina qasa nayi saboda jin yanda gabana yake faduwa haka kurrum naji bana bukatar kallonsa ba dan komai ba sai dan mugun halinsa na rashin ganin darajar mutane........Wani bafade ne yay gaggawar gyara masa abin magana ya saita masa daidai bakinsa, kamar wanda akayi wa dole yay gyara sai da yaja lokaci tukkuna cikin rashin walwala a fuskarsa da maganarsa yace."Alhamdullilah Allah kaine abin godiya. hakika nayi farin ciki mutuka daga dawo dani gida cikin koshin lafiya gami da tarin nasarori masu yawa." shiru yayi tare da sunkuyar da kansa qasa. Jin yayi shiru yasa nayi saurin dago kaina ina kallon gurin da yake, gani nayi kansa a sunkuye yana kallon 'kasan gurun tamkar me neman wani abu......Tsaki naja a cikin zuciyata nace"Wannan anyi d'an wulaqanci ya sani sarai jama'a shi suke sauraro amma ya fara magana yayi shiru, kaina na d'auke ina jin takaicin abinda yake......Gyaran murya ya kuma yi kafin ya cigaba da magana..."Sannan kuma nayi farin cikin samun iyayena da 'yan uwana da dukkanin wanda ke k'ark'ashin masarautar nan lafiya hakika naji dadi sosai da ganin yanda kuka fito 'ya'yanku da jikokin ku kuka nuna farin cikin ku dangane da dawowa ta gida Nagode sosai inayi muku fatan alkairi." yana k'are maganarsa ya janye bakinsa daga gurin abin maganar can kusa da Waziri ya koma ya tsaya har yanzu babu fara'a a fuskarsa.
Hayaniya da kace kace ne ya cika gurin, Wani bafade yayi tsawa tare da umartar kowa yay shuru kafin minti biyu gurin yayi tsit! Maimartaba ya miqe a nutse ya karasa gurin da abin magana yake, kafin ya fara magana sai da ya d'aga hannuwan sa sama alamar gaisuwa ga tarin jama'ar dake gurin.....Gurin ya sake rikicewa da hayaniya kowa sai fadin albarkacin bakinsa yake akan maimartaba. Da kyar aka samu sukayi shuru suka bar maimartabar yayi jawabi gami da miqa godiyarsa ga Allah ya kuma miqa godiyarsa ga tarin manyan mutanan da suka samu hallatar gurin suma bayin dake karkashin masarautarsa sai da ya miqa godiyarsa a gurinsu sannan ya koma ya zauna gurin zamansa, Baba Waziri yazo yay nasa jawabin Galadima da Ciroma suma sukayi nasu daidai gwargwado sannan maimartaba ya rufe taron da addua, ya miqe da niyyar shiga cikin gida fadawa ne suka kewaye shi suna ta gyara kintsi dai."!! Gurin ya karad'e da bushebushe gami da tashin muryoyin maro'ka da hayaniyar jama'a, sai da Sarki da muqarrabansa suka shiga gida tukkuna aka samu lafiya, jama'ar gurin suka watse kowa ya nufi 'bangaran da yake a cikin gidan.........Nida iyayena Cikin yanayi na ciwo muka shiga gurin mu, da sauri muka zaunar dashi, Tambaya ta ri'ke kafadarsa ni kuma hankali a tashe naje na d'ebo masa ruwa jiki na kyarma nazo na tallafo kansa ina kokarin bashi ruwan, bakinsa ya bud'e ina sa masa ruwan yana dawowa, lokaci guda zuciyoyinmu suka karye nida mahaifiyata hawaye muka fara, cikin karfin hali gami da kokarin janyo maganar yace."Ku daina kuka bashi ne abinda nake bukata ba."!
Zama nayi kusa dashi na rike hannunsa har yanzu hawaye bai da zubo min ba nace"Baba wai dan Allah me yake damunka kwana biyu ka'ki lafiya kullum cikin rashin kuzari da karfin jiki gashi kuma ka'ki ka bari a kira mai kula da lafiya yazo ya duba ka."
A hankali yace."Sumayya ba wani ciwo mai tsanani bane yake damuna zazza'bi ne mai zafi sai hajijiya gami da rashin kuzari to ni dik a tunani na ko shawara ce shiyasa na mayar da hankalina gurin shan maganinta amma yanzu ina ganin dole kije ki kira d'aya daga cikin masu kula da lafiya yazo ya dubani dan ni kadai nasan abinda nakeji a cikin jikina.
Tambaya hawaye ta share a sanyaye ta kalleni da fadin"Kiji can bangaran masu kula da lafiyar ki kirawo daya daga cikinsu yazo ya dubashi ni kaina jikina yay sanyi da wannan rashin lafiyar tasa a tsaitsaye fa ya kai sati hudu yanayi duk da yana shan maganin shawarar babu sauki kullum jikin rikicewa keyi."
Miqewa nayi da sauri nace "Bari naje can gurinsu na samesu." takalma na zura da saurin gaske na kama hanyar sashen masu kula da lafiyar gabad'aya bana cikin hayyacina ina tsananin kaunar mahaifina shiyasa rashin lafiyarsa ta d'aga min hankali mutuka.
"Sumayya." Sunana naji an kira da sauri na tsaya ina waigen bayana.
babu walwala a fuskarsa ya karaso inda nake tsaye kai tsaye yace."Ina Lawi yake ya bar aikinsa kamata yayi ace kafin mu fita gurin taro ya zubawa dokuna abinci yanda zai ishesu yanzu yanzu na shiga gurin na tarar da gabad'aya babu abinci a gabansu idan fa maimartaba ya samu labarin abinda yake zai fuskanci hukunci."
A marairace nace"Buba dan Allah kayi hakuri kada ka kai 'korafi wallahi babana bashi da lafiya tsayin sati hudu yake ciwo a tsaitsaye dukkanin abinda yake dauriya kawai yake dan Allah ka taimaka masa kana bawa dawakan abincin kafin yaji sauqi.
"Ke! saurara da wannan maganar.'' Nayi saurin kallonsa kwalla na kokarin zobomin, Ya cigaba da cewa''Kowa da kika gani akawai aikinsa a masarautar nan nawa aikin ma yafi nasa wahala tinda ni kwana nake a tsaye ina zirga zirga banga dalilin da zai sanya na d'auki nauyin wani na d'orawa kaina ba, ke aikin me kike da ba zaki d'auki nauyin mahaifinki ba kafin ya samu lafiya.
Hannu nasa na goge hawayen da suka zubo min nace" Shikkenan zanyi kokari ganin na dauki ragamar kula da dawakan kamar yanda babana yake yi amma ka san dai muna zaman karatu ranaku uku a sati ko kuma idan mun zauna tin safe sai yamma muke tashi.
D'aga kafad'a yay yace."Ke zaki tsarawa kanki yanda al'amura zasu tafi ni dai na fad'a miki ku kula da aikin ku kada maimartaba yaji wata magana.
Ajiyar zuciya na sauke mai zafi! nace"Shikkenan Buba nagode sosai insha Allahu zan iyakacin bakin kokarina." Gyda kansa yayi ya bar gurin, nima da sauri na wuce domin nufar inda nayi niyya.
Na jima a tsaye a bakin kofar d'akin nasu ina sallama kafin naji an amsa da fadin"Ko wacece ta shigo.'' Jim nayi ina tunanin shiga dan gabad'ayansu maza ne a ciki ina ganin kamar hakan bai dace ba.
Sallama na sakeyi, naji anyi min tsawa! da fad'in "Wai wacece take sallama ne ki shigo ki fadi uzirinki." Shahada nayi na tura kaina dakin....wasu na kwance kan katifunsu wasu kuma na zazzaune daga su sai gajerun wanduna.
Daga bakin kofa na tsaya nace"Dan Allah d'aya yazo ya duba babana Lawi bashi da lafiya."
Shuru sukayi min kowa ya cigaba da sabgarsa, raina ya 'baci! nace"Magana fa nakeyi muku kuna jina." 'Dantala ya zaburo min da hayaniya yace."Ke! babu wanda zai katse abinda yake a cikinmu yaje ya duba babanki idan kina so ayi miki abinda kike so ki shigo ciki muna bukatarki."
Cike da mamaki nake kallonsu nace"aikin ku ne fa mai zai sanya kuce sai nayi muku wani abu sannan zakuyi to ni ba 'yar iska bace idan kun saba latsa 'yan matan dake masarautar to ni ba' irinsu bace kuma wallahi idan bakuyi wasa ba yanzu zanje fadar sarki na sheda masa abinda kuke aikatawa..........A fusace! naga ya miqe yayo kaina zai mareni na kauce da sauri ina kare fuskata....wanda yake da sauqin halin cikinsu ne ya miqe tare da zira rigarsa ya kalleni da fadin" Shige muje na duba jikin mahaifin naki." Da sauri na fita daga dakin gabana sai faduwa yake......Tafiya nake zugwi zugwi ina mamakin al'amarin, kawai naji ana ta'ba min mazaunai! Da sauri na juyo ina kallonsa, murmushi yayi ya sosa kansa ido jawur yace."A gaskiya Sumayya Allah yayi miki baiwa mai mutukar daukar hankali, kina da duk abinda d'a namiji ke bukata a jikin mace kirjinki a cike yake dam-dam uwa uba mazaunai masu masifar rikimin lissafi wallahi tunda kika shiga dakinmu sha'awata ta tashi dan Allah ki bani damar mallakar wannan jikin naki wanda yake kokarin fitar dani hayyacina.
Kallonsa kawai nake wani 'katoton abu ya tokare min a ma'koshi nace"Yanzu Usman ashe kaima halinku d'aya dasu Dantala a zahiri inayi maka kallon salihi ashe kaima baka da d'abi'a mai kyau Usuman dan Allah meye amfanin lalata da kukeyi da 'ya'yan mutane idan fa masarauta ta samu labarin abinda kukeyi ba zakuji dad'i ba.
A sanyaye ya sosa kansa cikin jin kunya yace."Sumayya dan Allah kiyi hakuri wallahi ni ban fiya haikewa 'yan matan masarautar nan ba su Dantala ne masuyi kema yanzu hankalina ne ya tashi sosai shiyasa na gaza hakuri na kai hannuna mazaunanki amma kiyi hakuri dan Allah kada naji maganar a bakin kowa.
Cikin takaici na girgiza kaina tare da juyawa na cigaba da tafiya raina a masifar 'kuntacce.
To koda Usuman ya duba babana nan ya gano cewa hawan jini ne ke damunsa hankalinmu ya tashi nida tambaya muka dinga kuka dan mun riga mun san ciwon hawan jini babban ciwo ne gani muke kamar mun kusa muyi bankwana dashi shiyasa gabadaya hankalinmu ya tashi....Usuman ganin duk muna hawaye yasa ya rarrashe mu tare da bamu shawarwarin yanda zamu kula dashi da lafiyarsa yace "Insha Allahu mutukar aka bi dokar da ake bukata masu dauke lalurar suka bi to zai samu lafiya, Ya miqe tare da fad'in " Zaije yanzu ya kawo masa magungunan da zasu taimaka masa...godiya mukayi masa muna zubar da hawayen tausayi......
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALEðŸ’_ *[email protected]*
*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊�*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_
*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)