Sashe 31
Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ajiyar zuciya ya sauke yace."Sumayya idan baki rufe bakin ki ba wallahi zanyi miki abinda yafi haka! har ni kike tofawa yawu saboda kawai ina bukatarki to idan baki fadawa mahaifiyata ba bakya kaunar Allah da annabi."
"Kaga yallabai sakar min hannu tunda kayi abinda kake so." a zafafe nayi maganar.....hannuwana ya sake d'amkewa yace."Wannan tsiwar taki ita zata janyo miki komai nifa ba cewa nayi sai na shiga ramin ki ba ki bani wannan kawai ya isa ya gamsar dani." Yana maganar yana kallon kirjina.
Shuru nayi zuciyata sai tunzurani take...."Sumayya ki taimaika min dan Allah ki bari na samu satisfaction dake ba zan rabaki da budurcin ki ba."
Hawayen da nake makalewa suka zubo a kumatuna ni yau na rasa wane irin mutum Allah ya had'ani dashi wannan wane irin naci ne? hawayen fuskata ya shiga lashewa yana tsotsar kumatuna, na dinga jin tsigar jikina na tashi bakina yake so ya kama na kautar da fuskarta, hannu yasa ya juyo da ita, muka dinga kallon juna, ''Kin amince ko."? cikin mayaudariyar mirya yayi maganar." Girgiza kaina nayi nace"Ban amince ba." mirya na rawa yace."To yanzu ya kike so ayi ni dai ba zan bari ki fita ba sai bukatata ta biya." shuru nayi ina shawarwari da zuciyata nace"Ranka ya dad'e sha'awata kake ba sona kake ba ko."? Eh ina sha'awarki Sumayya ki bani jikinki na biya bukatata." na dinga kallonsa ina mamakin maganarsa..."Na amince zan baka jikina ka biya bukatarka amma ta hanyar aure." da sauri ya kalleni, kaina na daga masa nace"Ka aure ni na amince idan bukatarka ta biya a kaina ka sake ni ina ganin haka shine mafita.
Ina sane nayi masa wannan maganar saboda nasan abin ba zai yuwu ba.
"Ke a ganinki ni na dace da zama mijinki.''? cikin izgilanci yay maganar. Nace" Be dace ba amma ai kaji abinda nace ko nace idan bukatarka ta biya sai ka sake ni nidai ba zan baka kaina ba sai da aure.
Tsaki yaja da fadin''Ke bana san ki 'bata min rai ki sanja wata shawarar wannan ba tayi ba ni ba sa'an auranki bane kin gane ko.''? nace"To shikkenan sai ka danne sha'awarka a kaina tunda ka ki'yin yanda nace." Bina yay da kallo yace."ba zan aureki ba saboda baki dace dani ba ta kowane fanni kawai ki gindaya kudin da kike bukata sai na biya mutukar zaki mallaka min albarkatun jikinki.
Cikin zafin zuciya na ture shi na mike tsaye "Bana bukatar komai a gurinka na yanke shawara idan ba tayi maka ba sai kayi hakuri ." Kafata ya janyo da karfi na fada kansa matse ni yay a jikinsa daidai kunnena yace."Bafa fin karfina kikayi ba wallahi yanzu zanyi miki rashin mutunci ." Imani na cire na dasa masa hakora na a wuyansa, da sauri ya sake ni yana yamutsa fuska, da sauri na dauki dankwalina na daura na fita daga dakin, duk rintsi na daina shiga dakinsa sai dai duk abinda zaiyi min yayi.
Sai da muka dauki tsayin sati biyu bama magana da juna kullum idan na shiga sashen aikin gabana nake nayi tafiyata shima nasa bangaran fushi yake dani sosai dan har na gama aikina baya kallon inda nake kullum fuskarsa a murtuke, sai dai duk sanda Gimbiya Lawisa ta kawo masa ziyara ina shan dariya dan kafin su rabu sai sunyi fada yafi a 'kirga sam bata da zuciya sai tayi ta bashi hakuri alhalin duk rabin laifin nasa ne amma sai ta dauka ta dorawa kanta cikin zuciyata nace aiki ya same ki.
Hidima ce ta tashi a gidan sarautar sai shirye shirye ake ana gyara gurin da za gudanar da gagarimar Walimar da maimartaba ya shirya domin murna bud'e katafaran asibitin daya ginawa yaron nashi, hankalin Uwargida da 'yayanta ya tashi suka dinga sintiri a gidan suna 'kulle-'kullen yanda zasu tarwatsa taron jama'ar da maimartaba ya gayyato domin su tayashi farin ciki......Muddibo ya zama tamkar mahaukaci sai shige da fice yake gurin malamai burinsa kawai bukatarsa ta biya
Gama aikina kenan na fito da niyyar tafiya aunty Safiyya ta shigo, har 'kasa na durkusa na gaisheta, ta amsa a lokacin da take kokarin zama kan kujera, mikewa nai tsaye tace"Yarima na sama."? da sauri nace"E ranki ya dad'e." Tace."Je kice masa nazo yazo mu gaisa." Da sauri na amsa da to.
Aunty Safiyya na ganin 'bacewar Sumayya da sauri ta mi'ke ta isa bakin benan ta shiga barbad'a wani abu tana yi tana kiran sunansa, sai da tayi sau bakwai tukkuna ta koma ta zauna.
Bubbuga kofar dakin nayi gabana na fad'uwa! ciki ciki naji maganarsa, nace"Ranka ya dade aunty Safiyya ce tazo tana falo tana jiranka."
"Gani nan." abinda ya fada kenan. nayi saurin barin gurin, samun ta nayi tana duba wayarta nace"Ranki ya dade gashi nan zuwa." Tace."Okey kawo min ruwa." da sauri na nufi kicin domin cika umarninta.
Hannuna ri'ke da tire me dauke da goran ruwa da kwalin lemo na fito daga kicin din daidai lokacin da yake kokarin saukowa hawa biyu ya taka amma sauran be iya ba takawa ba kansa ya dinga juyawa yana ganin dishi dishi kafin nayi aune kawai na hango shi yana gangarowa! salati na kurma tire din hannuna ya fadi a guje na nufe shi ina kiran sunansa, duk tsayin benan da yawan steps haka ya dinga gangarowa yana buge kansa, zuwa nayi domin tareshi kafin nayi wani yunk'uri ya tunkud'e ni na fad'i a gurin tare muka dinga gangarowa har sai da muka dire kasa, na mike zumbur! ina nishi da salati! aunt Safiyya ta karaso gurin sai salati take tare muka isa inda yake kwance tamkar wanda ya mutu haka yay numfashinsa sai fita yake da sauri, wasu hawayen fargaba da tashin hankali ne suka shiga zubo min....."Ke! maza jeki dauko ruwa suma yayi." miryar ta ta dawo dani da sauri na bar gurin.....Tun daga nesa na hange ta tana danna kirjinsa tare da kara kunnanta a kirjinsa.. murya na rawa nace"Aunty ga ruwan! kar'ba tayi ta bude ta shiga shafa masa a fuska, shuru be farfado ba, jikina na rawa nace"Ranki ya dade ko naje na fadawa Mamma." Girgixa kanta tayi tace"Zo ki cigaba da shafa masa ruwan bari naje na sanar da maimartaba." Da sauri na zauna inda ta tashi na cigaba da shafa masa ruwan a fuskarsa kuka kawai nake ina tofa masa addua, kansa na tallafo na rungume a kirjina goran ruwan na ajiya na cigaba da tofa masa duk adduar da tazo bakina gabadaya na kasa tsayar da hawayen dake zuba.
Zazzafar ajiyar Zuciya ya sauke naji yayi motsi, da sauri na kalli fuskarsa naga ya bude idonsa Allah na godewa kana na kira sunansa, "Ranka ya dade sannu me yake damunka."
jikinsa ya cire anawa ya tsira min ido minti biyu kafin yace."Me ya faru jikina ciwo yake min.'' naji wani irin rauni gami da tsabar tausayinsa.
" Gangarowa kayi daga sama." nafada ina goge hawayen dake zubo min.'' juyawa naga yayi yana kallon tsayin benan.'" Ya juyo nai saurin kauda kaina...."Ina aunty Safiyyan." ?
"Taje kiran Maimartaba." mikewa yay yace."Zoki hada min ruwan zafi na gasa jikina kamar anyi min dukan tsiya haka nake ji.'' Na mike da sauri na rike hannunsa, kallona yayi nace."Kada ka sake hawa benan ka zauna a falo."
"Sabida me."? ya fada cikin sigar tuhuma! cikin fargabar masifar sa nace ni dai nace kada ka hau." Kasa yayi da kansa yana nazari kafin ya cire hannunsa yaje ya zauna a kan kujera, da sauri na nufi kicin......kanwa na jika a madaidaicin bokiti na fito benan na nufa da addua a bakina na shiga bin Steps d'in one by one ina yayyafa ruwan kanwar ina addua a bakina, sai da ruwan kanwar ya bushe na same shi a zaune a inda yake nace"Kana iya hawa." mikewa yayi ba tare da yace komai ba ya nufi saman nace"Ranka ya dade ka hau kana karanta ayatulkursiyu." bece min komai ba ya fara hawa steps din. ajiyar zuciya na sauke bayan hawansa Allah nagodewa kana nabi bayansa domin hada masa ruwan wankan daya b'ukata..
*Na kudi ne..!*
Kika karanta baki biya ba Allah ya isa, idan kina so ki biya kudinki ga yanda abin yake...Vip gruop#600 normal #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
59&60
Tsaye na sameshi a bakin toilet din kallona yake har na karaso kusa dashi ina kokarin shige shi na shiga toilet din ya tare hanya, kallonsa nayi gabana na fad'uwa yace."Ki fada min gaskiyar abinda ya faru dani." Nace"Ranka ya dade abinda na sani shi na fada maka gangarowa kayi daka sama." Okey to meye amfanin abinda kika yayyafa a jikin steps. " yafada yana tsare ni da ido, duk sai naji gwiwata tayi sanyi ina jin tsoron kada ya zargeni da wani abun nace''Ruwan kanwa ne na yayyafa." "Kina nufin me kenan."? haushi ya bani nace" Dan Allah ka bar maganar tunda dai Allah ya kare shikkenan."
Shuru yayi yana kallona sauri nayi na shiga toilet din bayana ya biyo koda na ganshi a tsaye yana kallona sai na sake tamke fuska na hada masa komai na wankan da sauri na fita.
Wanka yake yana tunanin al'amarin jikinsa ya soma sanyi ya kuma soma gazgata abubuwan dake faruwa 'yan uwanshi na kokarin suga bayanshi ya rasa me yasa suka damu dashi da duk abunda ya Shafeshi sarauta suke so shi kuma baya so sune suke wahalar da kansu a banza.
Na jima zaune a falon ina jiran dawowar aunty Safiyyar shuru har kusan mintina talatin bata dawo ba cikin zuciyata nace dama karya take babu wanda zata kira, ajiyar zuciya na sauke ina mamakin al'amarin babu shakka wani mugun abun ta shigo dashi gashi nan yaso yayi tasiri a tare dashi mikewa nayi da fadin''Insha Allahu haka zaku gaji ku bari, gurin mu na nufa ina cike da mamakin al'amarin.
"Kaga yallabai sakar min hannu tunda kayi abinda kake so." a zafafe nayi maganar.....hannuwana ya sake d'amkewa yace."Wannan tsiwar taki ita zata janyo miki komai nifa ba cewa nayi sai na shiga ramin ki ba ki bani wannan kawai ya isa ya gamsar dani." Yana maganar yana kallon kirjina.
Shuru nayi zuciyata sai tunzurani take...."Sumayya ki taimaika min dan Allah ki bari na samu satisfaction dake ba zan rabaki da budurcin ki ba."
Hawayen da nake makalewa suka zubo a kumatuna ni yau na rasa wane irin mutum Allah ya had'ani dashi wannan wane irin naci ne? hawayen fuskata ya shiga lashewa yana tsotsar kumatuna, na dinga jin tsigar jikina na tashi bakina yake so ya kama na kautar da fuskarta, hannu yasa ya juyo da ita, muka dinga kallon juna, ''Kin amince ko."? cikin mayaudariyar mirya yayi maganar." Girgiza kaina nayi nace"Ban amince ba." mirya na rawa yace."To yanzu ya kike so ayi ni dai ba zan bari ki fita ba sai bukatata ta biya." shuru nayi ina shawarwari da zuciyata nace"Ranka ya dad'e sha'awata kake ba sona kake ba ko."? Eh ina sha'awarki Sumayya ki bani jikinki na biya bukatata." na dinga kallonsa ina mamakin maganarsa..."Na amince zan baka jikina ka biya bukatarka amma ta hanyar aure." da sauri ya kalleni, kaina na daga masa nace"Ka aure ni na amince idan bukatarka ta biya a kaina ka sake ni ina ganin haka shine mafita.
Ina sane nayi masa wannan maganar saboda nasan abin ba zai yuwu ba.
"Ke a ganinki ni na dace da zama mijinki.''? cikin izgilanci yay maganar. Nace" Be dace ba amma ai kaji abinda nace ko nace idan bukatarka ta biya sai ka sake ni nidai ba zan baka kaina ba sai da aure.
Tsaki yaja da fadin''Ke bana san ki 'bata min rai ki sanja wata shawarar wannan ba tayi ba ni ba sa'an auranki bane kin gane ko.''? nace"To shikkenan sai ka danne sha'awarka a kaina tunda ka ki'yin yanda nace." Bina yay da kallo yace."ba zan aureki ba saboda baki dace dani ba ta kowane fanni kawai ki gindaya kudin da kike bukata sai na biya mutukar zaki mallaka min albarkatun jikinki.
Cikin zafin zuciya na ture shi na mike tsaye "Bana bukatar komai a gurinka na yanke shawara idan ba tayi maka ba sai kayi hakuri ." Kafata ya janyo da karfi na fada kansa matse ni yay a jikinsa daidai kunnena yace."Bafa fin karfina kikayi ba wallahi yanzu zanyi miki rashin mutunci ." Imani na cire na dasa masa hakora na a wuyansa, da sauri ya sake ni yana yamutsa fuska, da sauri na dauki dankwalina na daura na fita daga dakin, duk rintsi na daina shiga dakinsa sai dai duk abinda zaiyi min yayi.
Sai da muka dauki tsayin sati biyu bama magana da juna kullum idan na shiga sashen aikin gabana nake nayi tafiyata shima nasa bangaran fushi yake dani sosai dan har na gama aikina baya kallon inda nake kullum fuskarsa a murtuke, sai dai duk sanda Gimbiya Lawisa ta kawo masa ziyara ina shan dariya dan kafin su rabu sai sunyi fada yafi a 'kirga sam bata da zuciya sai tayi ta bashi hakuri alhalin duk rabin laifin nasa ne amma sai ta dauka ta dorawa kanta cikin zuciyata nace aiki ya same ki.
Hidima ce ta tashi a gidan sarautar sai shirye shirye ake ana gyara gurin da za gudanar da gagarimar Walimar da maimartaba ya shirya domin murna bud'e katafaran asibitin daya ginawa yaron nashi, hankalin Uwargida da 'yayanta ya tashi suka dinga sintiri a gidan suna 'kulle-'kullen yanda zasu tarwatsa taron jama'ar da maimartaba ya gayyato domin su tayashi farin ciki......Muddibo ya zama tamkar mahaukaci sai shige da fice yake gurin malamai burinsa kawai bukatarsa ta biya
Gama aikina kenan na fito da niyyar tafiya aunty Safiyya ta shigo, har 'kasa na durkusa na gaisheta, ta amsa a lokacin da take kokarin zama kan kujera, mikewa nai tsaye tace"Yarima na sama."? da sauri nace"E ranki ya dad'e." Tace."Je kice masa nazo yazo mu gaisa." Da sauri na amsa da to.
Aunty Safiyya na ganin 'bacewar Sumayya da sauri ta mi'ke ta isa bakin benan ta shiga barbad'a wani abu tana yi tana kiran sunansa, sai da tayi sau bakwai tukkuna ta koma ta zauna.
Bubbuga kofar dakin nayi gabana na fad'uwa! ciki ciki naji maganarsa, nace"Ranka ya dade aunty Safiyya ce tazo tana falo tana jiranka."
"Gani nan." abinda ya fada kenan. nayi saurin barin gurin, samun ta nayi tana duba wayarta nace"Ranki ya dade gashi nan zuwa." Tace."Okey kawo min ruwa." da sauri na nufi kicin domin cika umarninta.
Hannuna ri'ke da tire me dauke da goran ruwa da kwalin lemo na fito daga kicin din daidai lokacin da yake kokarin saukowa hawa biyu ya taka amma sauran be iya ba takawa ba kansa ya dinga juyawa yana ganin dishi dishi kafin nayi aune kawai na hango shi yana gangarowa! salati na kurma tire din hannuna ya fadi a guje na nufe shi ina kiran sunansa, duk tsayin benan da yawan steps haka ya dinga gangarowa yana buge kansa, zuwa nayi domin tareshi kafin nayi wani yunk'uri ya tunkud'e ni na fad'i a gurin tare muka dinga gangarowa har sai da muka dire kasa, na mike zumbur! ina nishi da salati! aunt Safiyya ta karaso gurin sai salati take tare muka isa inda yake kwance tamkar wanda ya mutu haka yay numfashinsa sai fita yake da sauri, wasu hawayen fargaba da tashin hankali ne suka shiga zubo min....."Ke! maza jeki dauko ruwa suma yayi." miryar ta ta dawo dani da sauri na bar gurin.....Tun daga nesa na hange ta tana danna kirjinsa tare da kara kunnanta a kirjinsa.. murya na rawa nace"Aunty ga ruwan! kar'ba tayi ta bude ta shiga shafa masa a fuska, shuru be farfado ba, jikina na rawa nace"Ranki ya dade ko naje na fadawa Mamma." Girgixa kanta tayi tace"Zo ki cigaba da shafa masa ruwan bari naje na sanar da maimartaba." Da sauri na zauna inda ta tashi na cigaba da shafa masa ruwan a fuskarsa kuka kawai nake ina tofa masa addua, kansa na tallafo na rungume a kirjina goran ruwan na ajiya na cigaba da tofa masa duk adduar da tazo bakina gabadaya na kasa tsayar da hawayen dake zuba.
Zazzafar ajiyar Zuciya ya sauke naji yayi motsi, da sauri na kalli fuskarsa naga ya bude idonsa Allah na godewa kana na kira sunansa, "Ranka ya dade sannu me yake damunka."
jikinsa ya cire anawa ya tsira min ido minti biyu kafin yace."Me ya faru jikina ciwo yake min.'' naji wani irin rauni gami da tsabar tausayinsa.
" Gangarowa kayi daga sama." nafada ina goge hawayen dake zubo min.'' juyawa naga yayi yana kallon tsayin benan.'" Ya juyo nai saurin kauda kaina...."Ina aunty Safiyyan." ?
"Taje kiran Maimartaba." mikewa yay yace."Zoki hada min ruwan zafi na gasa jikina kamar anyi min dukan tsiya haka nake ji.'' Na mike da sauri na rike hannunsa, kallona yayi nace."Kada ka sake hawa benan ka zauna a falo."
"Sabida me."? ya fada cikin sigar tuhuma! cikin fargabar masifar sa nace ni dai nace kada ka hau." Kasa yayi da kansa yana nazari kafin ya cire hannunsa yaje ya zauna a kan kujera, da sauri na nufi kicin......kanwa na jika a madaidaicin bokiti na fito benan na nufa da addua a bakina na shiga bin Steps d'in one by one ina yayyafa ruwan kanwar ina addua a bakina, sai da ruwan kanwar ya bushe na same shi a zaune a inda yake nace"Kana iya hawa." mikewa yayi ba tare da yace komai ba ya nufi saman nace"Ranka ya dade ka hau kana karanta ayatulkursiyu." bece min komai ba ya fara hawa steps din. ajiyar zuciya na sauke bayan hawansa Allah nagodewa kana nabi bayansa domin hada masa ruwan wankan daya b'ukata..
*Na kudi ne..!*
Kika karanta baki biya ba Allah ya isa, idan kina so ki biya kudinki ga yanda abin yake...Vip gruop#600 normal #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊ðŸ?)
59&60
Tsaye na sameshi a bakin toilet din kallona yake har na karaso kusa dashi ina kokarin shige shi na shiga toilet din ya tare hanya, kallonsa nayi gabana na fad'uwa yace."Ki fada min gaskiyar abinda ya faru dani." Nace"Ranka ya dade abinda na sani shi na fada maka gangarowa kayi daka sama." Okey to meye amfanin abinda kika yayyafa a jikin steps. " yafada yana tsare ni da ido, duk sai naji gwiwata tayi sanyi ina jin tsoron kada ya zargeni da wani abun nace''Ruwan kanwa ne na yayyafa." "Kina nufin me kenan."? haushi ya bani nace" Dan Allah ka bar maganar tunda dai Allah ya kare shikkenan."
Shuru yayi yana kallona sauri nayi na shiga toilet din bayana ya biyo koda na ganshi a tsaye yana kallona sai na sake tamke fuska na hada masa komai na wankan da sauri na fita.
Wanka yake yana tunanin al'amarin jikinsa ya soma sanyi ya kuma soma gazgata abubuwan dake faruwa 'yan uwanshi na kokarin suga bayanshi ya rasa me yasa suka damu dashi da duk abunda ya Shafeshi sarauta suke so shi kuma baya so sune suke wahalar da kansu a banza.
Na jima zaune a falon ina jiran dawowar aunty Safiyyar shuru har kusan mintina talatin bata dawo ba cikin zuciyata nace dama karya take babu wanda zata kira, ajiyar zuciya na sauke ina mamakin al'amarin babu shakka wani mugun abun ta shigo dashi gashi nan yaso yayi tasiri a tare dashi mikewa nayi da fadin''Insha Allahu haka zaku gaji ku bari, gurin mu na nufa ina cike da mamakin al'amarin.