Sashe 92
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 7 min read
Shuru amiran tayi tana duban sumayya cike da qwarin gwiwa da kuma yaqini cikin zancanta,itama dubanta sumayyan keyi kafin ta saki murmushi sannan ya kada kai
"Ni nayi kuskure amira,ni na yi masa kallon mukhtar dina bayan bashi bane kamanceceniyar iya murya ce kawai,koma waye zaiyi zaton ba lafiya tunda baisan farkon lamarin ba,amira,bana jin so ko qaunar ko wanne namiji bare na yi sha'awar zaman aure da shi,banqi a ce nabi mukhtar ba muyi zamanmu cikin rahamar ubangiji,abunda kawai nake tausayawa abdallah na" ta fadi cikin karyewar murya da rauni,duk da qoqarin kaucewa hakan da takeyi,tausayinta ya sake kama amira
"Da gaske amiran umman khalipha kin taba aure kuma ma har da boy?" Ta tambaya cikin zumudi,kai ta gyada mata tana murmushi
"Zanso naga boy din nan,na tabbata zaiyi kyau kamar mamarsa" wannan karon har dariya taso sara,saboda ta tabo gudan jininta,yaron da shima tun kafin ya shaqi iskar duniya ya fara fuskantar gwagwarmaya da matsalar rayuwa,koda ya shigo cikin duniyar ma ba'a barshi ya huta ba sai da aka so saida rayuwarsa,zainab ta fado mata,ko yanzu tana wacce duniya,baki daya sai taji son aure ya sake fita daga zuciyarta,itakam yanzu me zata ci da aure
"Amma zanso amira ki amincewa qudirina,na tabbata cewa rayuwar yaya man zata sauya zuwa yanayin da muke masa fata da hange,zan iya cewa ANTY SU'AD bata da wani amfani a rayuwanshi" cewar amira tana duban sumayya,kai ta shiga girgizawa
"Duk mai qaunata amira ba zai sake min sha'awar aure ba a yanzu,nikam me zanci da aure,auren ma na mai mata"
"Me kike cewa ne?,amira zanso sanin wace ke,na tabbatar akwai wani abu a rayuwarki ba wai mukhtar bane zalla" miqewa tayi a hankali ta zauna tana duban amiran
"Babu lokaci,duba kiga goma na dare"
"Ko zan kwana anan nasan babu damuwa,ina son ki ban labarinki don Allah,naji anty dije na fadin wasu abubuwa da ban gane ma kansu ba"murmushi tayi
"Me zakici da labarina banda kayan sanya hawaye a ciki,babu komai a labarina face wuya da naci game da kishiyoyi da abokan zama na" idanuwa amiran ta zaro
"Kina nufin bama aure daya kika yi ba amiran umman khalipha?,ina cewa zamuyi sa'anni dake fa?" Dariya tayi wannan karon
"Hala mass com kika karanta ko,ina ce miki dare yayi amma baki damu ba?"
Dariya itama ta saki tare da miqewa ba don taso ba
"Zan tafi,amma zan dawo ki bani labarinki"
"Sai kinzo,sai da safe na gode"
"Nice da godiya kuma kiyi haquri da abinda ya faru"
"Babu komai QADDARA CE!" ta ambata wani abu na taba ranta,juyawa amiran tayi ta fice tana murmushi
****** ******* *******
Sukuku haka ta wuni washegari,duk da ba wani abu take ji na ciwo a jikinta ba amma baki daya bata da kuzari kamar wadda aka zarewa laka,da yammaci tana kwance a falon,babu kowa gidan daga ita sai anty dije,su laila sun tafi gidan kakarsu,itama rashin qwarin jiki ne ya hanata zuwa taji muryar amira tana sallama,miqewa tayi daga kwanciyar tana amsawa tare da maida daurin dankwalinta da ya zame,sai taga ashe su biyu ne ita da anty maamaa,miqewa tayi fuskarta qunshe da fara'a tana musu sannu da zuwa,kitchen ta juya ta dauko lemo saman tray ruwa da kofuna ta ajjiye musu sannan ta haura sama don kiran anty dije.
Tare suka sauko,fuskarta dauke da fara'a itama take musu lale da zuwa,ta zauna suka gaisa sannan sumayya ta gaida antyn kafin ta waiwaya ga amira suka gaisa
"Zuwa nayi dubiya,jiya muna cikin gida ashe haka abu ya faru,sam ban sani ba sai dazu da mahmoud ya shigo yake gayan,sai kuma farida itama ta sanarmin su suka kawota gida"
"Wallahi kuwa,abin sai addu'a,damuwar dake ranta ce ta mata tasiri har ta haifar da hakan"
"Allah ya kiyaye gaba,baki daya ma banga mustaphan ba yau,yana ta shirye shiryen komawa,inason tambayarsa ya akai hakan ta faru,banji dadi ba sam bai kyauta ba,ai ba'a haka.....sannu sumayya ya jikin?" A kunyace kanta na qasa tana murza yatsun hannunta,tana jin tamkar ta jawowa kanta wani babban abun kunya ne,kada ma wasu su tsammaci saboda shi ta suma tace
"Na warke ai anty"
"Allah ya sawwaqe ya qara afuwa"
"Amin anty dije ta amsa,amiran ce ta dubi sumayya
"muje ina son in ganki"tana dariya,sai ta miqe tayi gaba amiran ta biyo bayanta.
Bakin gado suke zaube baki dayansu amiran ta kalleta
"ina alqawarina?"
"Labarina bazai yiwu ba yanzu amira,ki bari na sake samun sauqi ko?"shiru ta danyi tana kada kai
"To shikenan,Allah ya qara baki lafiya"
"Amin" ta fada tana murmushi,jefi jefi amiran ta dinga sako mata hita,wata ta 'yan uwa wata ta qawayenta wata ta gidansu duk don ta sake sakin jiki,yawanci duka bata sansu ba,amma abun yana burgeta,saidai tayi murmushi kawai,a nan ta fahimci su'ad itace matar mustapha.
Suna zaune anty dije ta leqo tace anty zata tafu,miqewa tayi tana cewa
"Nima tafiya zanyi,zamu je unguwa ne yau duka 'yammatan,sai na dawo"
"Allah ya tsare,na gode ki gaida ummee"
"Zataji kuwa,don batasan abinda ya faru ba,da yau ya man ya shiga uku wallahi,inaga ma sai na guntsa mata batun" ta fada tana dariya gami da ficewa,sumayyan nason ce mata kada tayi amma tuni tayi gaba abinta.
Kiran wayar bdur rahaman ita ta qarasa tayata hira har sha biyu na dare sunata hira,yana ta bata labarin yadda shirye shirye suka kankama na bude islamic clinic dinshi,yana so ya soko mata maganar yadda yayi missing dinta da kuma yadda yake son ganinta saidai yana tsoron kada damar da ya samu ya rasata,sam bata gaya masa zata zo kano ba har sukayi sallama.
******* ******* ********
A hankali ya dinga takowa cikin tafiyar sa ta qasaita har cikin falon baabaa prof din,sanye da short sleev polo t.shirt jaa da touches na baqi,straight leg trouser sai safa a qafarnshi,hannunsa soke a aljihun wandonsa,wanda ya zame masa al'ada idan ya sanya qananun kaya,idan ba waya hannunshi to zaka samu hannayen cikin aljihu ko harde a qirji.
Sallamarsa ce ta sanya baabaan dago kai yana dubansa,mai hali bai sauya halinsa,wasu daga al'adar turawa har yau sunqi barin mustaphan,ko da yake ta yaya zasu barshin bayan har yau shima bai bar cikinsu ba,sam baison manyan kaya,da wuya ka ganshi da su,cikin girmamawa ya qaraso ya duqa gaban baabaan yana gaida shi,amsawa shima yayi saidai fuskanshi sam babu walwala sabanin yadda ya saba ganinsa
"Yaushe ne zaka koma" hannayensa soke cikin juna ya amsa kamar wanda baison yin maganar
"Cikin wannan satin in sha Allah"
"Allah ya lamunce"
"Amin ya Allah". Shiru ne ya dan ratsa tsakaninsu,shi mustpha na sauraron me baaban zai gaya mishi tunda shi ya aikata takanas sashensa aka kira shi,yayin da shi kuma baaban yayi banza da shi,yana so yau ya qure miskilancinsa,yaci gaba da bude shafukan jaridar dake hannunsa,sam baka rabashi da duba jaridu,duk da bai cikin sabgogi da al'amuran gwamnati a bayyane amma a badini gangar jiki da zuciyarsa na tare da su.
Har ya kammala karatun jaridarsa baiji yace komai ba,hasalima da ya daga kansa sai yaga ya jingina bayansa da jikin kujera gami da miqe qafafunsa idanuwansa a lumshe,ajjiye jaridar yayi yana sauke ajiyar zuciya,glass dinsa ya zare shima ya ajjiye gefe yana dubansa
"wato ba zaka iya tambayar dalilin da ya sanya na kiraka ba kenan"miqewa yayi ya zauna sosai yana duban baaban
"nayi zaton baka kammala abinda kake bane,banson kuma katse ka"shuru yai ya jinjina kai,duk cikin 'ya'yansa bai haifi kamar mustapha ba har yau ta kowanni fanni ya tsrerema 'yan uwansa maza da mata
"me ya kaika ture yarinyar mutane har ta suma"
"Yarinyar mutane har ta suma?" Abinda ya dinga maimaitawa ciki kwanyarsa kenan,sam ya mance wace ce,wa baabaa ke fadi ya ambata cikin zuciyarsa
"Yarinya baquwa 'yar gidan alhj farouq" har ga Allah bai fuskanci kan wa baba ke magana ba,don shi baki daya ya mance lamarin,baaban ya kalla kamar yanason qarin bayani kan abinda yake cewa,baabaan yasan irin kallo,indai mustaphan yayi ba shakka yana buqatar qarin bayani
"Tashi kaje,ka kyauta ka kuma yi abinda ya dace,nima zanyi abinda ya dace din" duk da bai gane da wa yake nufin ba amma ya miqe kasancewar ya riga ya bashi umarni,cikin girmamawa ya rusuna yana cewa
"A huta lafiya" baban bai amsa shi ba har ya miqe ya juy,har ya taka daya biyu sai kuma ya juyo ya dawo ya sake rusunawa aladabce
"Dambun naman naka ya qare?" Ya fahimci me yake nufi,dambun naman da sumayya tayi masa ne,ya ganshi yana ci ya tsokaneshi da cewa gun saidawa aka siyo masa don yasan baison cimar siyarwa,yace idan ya qare zai masa magana ya sake siyo masa a inda aka siyo
"Bai qare ba" baban ya bashi amsa idonsa akanshi har ya miqe,baiyi qarya ba,mustaphan daban yake cikin yaranshi,kamar yadda yake da wasu baqin halaye haka dabi'unsa na kula da iyayensa suke,daban ya daukesu,martaba da darajarsu bai hada ta daya data wani halitta ba,cikin kowanne yanayi ko motsi nashi yakan sanya shi gaba,fatarshi da addu'arshi daya Allah ya azurta shi da zuriyya dayyiba saliha,wadda zata ji qansa yadda yake jin qan nashi iyayen.
***** ****** ****** *****
"Ni nayi kuskure amira,ni na yi masa kallon mukhtar dina bayan bashi bane kamanceceniyar iya murya ce kawai,koma waye zaiyi zaton ba lafiya tunda baisan farkon lamarin ba,amira,bana jin so ko qaunar ko wanne namiji bare na yi sha'awar zaman aure da shi,banqi a ce nabi mukhtar ba muyi zamanmu cikin rahamar ubangiji,abunda kawai nake tausayawa abdallah na" ta fadi cikin karyewar murya da rauni,duk da qoqarin kaucewa hakan da takeyi,tausayinta ya sake kama amira
"Da gaske amiran umman khalipha kin taba aure kuma ma har da boy?" Ta tambaya cikin zumudi,kai ta gyada mata tana murmushi
"Zanso naga boy din nan,na tabbata zaiyi kyau kamar mamarsa" wannan karon har dariya taso sara,saboda ta tabo gudan jininta,yaron da shima tun kafin ya shaqi iskar duniya ya fara fuskantar gwagwarmaya da matsalar rayuwa,koda ya shigo cikin duniyar ma ba'a barshi ya huta ba sai da aka so saida rayuwarsa,zainab ta fado mata,ko yanzu tana wacce duniya,baki daya sai taji son aure ya sake fita daga zuciyarta,itakam yanzu me zata ci da aure
"Amma zanso amira ki amincewa qudirina,na tabbata cewa rayuwar yaya man zata sauya zuwa yanayin da muke masa fata da hange,zan iya cewa ANTY SU'AD bata da wani amfani a rayuwanshi" cewar amira tana duban sumayya,kai ta shiga girgizawa
"Duk mai qaunata amira ba zai sake min sha'awar aure ba a yanzu,nikam me zanci da aure,auren ma na mai mata"
"Me kike cewa ne?,amira zanso sanin wace ke,na tabbatar akwai wani abu a rayuwarki ba wai mukhtar bane zalla" miqewa tayi a hankali ta zauna tana duban amiran
"Babu lokaci,duba kiga goma na dare"
"Ko zan kwana anan nasan babu damuwa,ina son ki ban labarinki don Allah,naji anty dije na fadin wasu abubuwa da ban gane ma kansu ba"murmushi tayi
"Me zakici da labarina banda kayan sanya hawaye a ciki,babu komai a labarina face wuya da naci game da kishiyoyi da abokan zama na" idanuwa amiran ta zaro
"Kina nufin bama aure daya kika yi ba amiran umman khalipha?,ina cewa zamuyi sa'anni dake fa?" Dariya tayi wannan karon
"Hala mass com kika karanta ko,ina ce miki dare yayi amma baki damu ba?"
Dariya itama ta saki tare da miqewa ba don taso ba
"Zan tafi,amma zan dawo ki bani labarinki"
"Sai kinzo,sai da safe na gode"
"Nice da godiya kuma kiyi haquri da abinda ya faru"
"Babu komai QADDARA CE!" ta ambata wani abu na taba ranta,juyawa amiran tayi ta fice tana murmushi
****** ******* *******
Sukuku haka ta wuni washegari,duk da ba wani abu take ji na ciwo a jikinta ba amma baki daya bata da kuzari kamar wadda aka zarewa laka,da yammaci tana kwance a falon,babu kowa gidan daga ita sai anty dije,su laila sun tafi gidan kakarsu,itama rashin qwarin jiki ne ya hanata zuwa taji muryar amira tana sallama,miqewa tayi daga kwanciyar tana amsawa tare da maida daurin dankwalinta da ya zame,sai taga ashe su biyu ne ita da anty maamaa,miqewa tayi fuskarta qunshe da fara'a tana musu sannu da zuwa,kitchen ta juya ta dauko lemo saman tray ruwa da kofuna ta ajjiye musu sannan ta haura sama don kiran anty dije.
Tare suka sauko,fuskarta dauke da fara'a itama take musu lale da zuwa,ta zauna suka gaisa sannan sumayya ta gaida antyn kafin ta waiwaya ga amira suka gaisa
"Zuwa nayi dubiya,jiya muna cikin gida ashe haka abu ya faru,sam ban sani ba sai dazu da mahmoud ya shigo yake gayan,sai kuma farida itama ta sanarmin su suka kawota gida"
"Wallahi kuwa,abin sai addu'a,damuwar dake ranta ce ta mata tasiri har ta haifar da hakan"
"Allah ya kiyaye gaba,baki daya ma banga mustaphan ba yau,yana ta shirye shiryen komawa,inason tambayarsa ya akai hakan ta faru,banji dadi ba sam bai kyauta ba,ai ba'a haka.....sannu sumayya ya jikin?" A kunyace kanta na qasa tana murza yatsun hannunta,tana jin tamkar ta jawowa kanta wani babban abun kunya ne,kada ma wasu su tsammaci saboda shi ta suma tace
"Na warke ai anty"
"Allah ya sawwaqe ya qara afuwa"
"Amin anty dije ta amsa,amiran ce ta dubi sumayya
"muje ina son in ganki"tana dariya,sai ta miqe tayi gaba amiran ta biyo bayanta.
Bakin gado suke zaube baki dayansu amiran ta kalleta
"ina alqawarina?"
"Labarina bazai yiwu ba yanzu amira,ki bari na sake samun sauqi ko?"shiru ta danyi tana kada kai
"To shikenan,Allah ya qara baki lafiya"
"Amin" ta fada tana murmushi,jefi jefi amiran ta dinga sako mata hita,wata ta 'yan uwa wata ta qawayenta wata ta gidansu duk don ta sake sakin jiki,yawanci duka bata sansu ba,amma abun yana burgeta,saidai tayi murmushi kawai,a nan ta fahimci su'ad itace matar mustapha.
Suna zaune anty dije ta leqo tace anty zata tafu,miqewa tayi tana cewa
"Nima tafiya zanyi,zamu je unguwa ne yau duka 'yammatan,sai na dawo"
"Allah ya tsare,na gode ki gaida ummee"
"Zataji kuwa,don batasan abinda ya faru ba,da yau ya man ya shiga uku wallahi,inaga ma sai na guntsa mata batun" ta fada tana dariya gami da ficewa,sumayyan nason ce mata kada tayi amma tuni tayi gaba abinta.
Kiran wayar bdur rahaman ita ta qarasa tayata hira har sha biyu na dare sunata hira,yana ta bata labarin yadda shirye shirye suka kankama na bude islamic clinic dinshi,yana so ya soko mata maganar yadda yayi missing dinta da kuma yadda yake son ganinta saidai yana tsoron kada damar da ya samu ya rasata,sam bata gaya masa zata zo kano ba har sukayi sallama.
******* ******* ********
A hankali ya dinga takowa cikin tafiyar sa ta qasaita har cikin falon baabaa prof din,sanye da short sleev polo t.shirt jaa da touches na baqi,straight leg trouser sai safa a qafarnshi,hannunsa soke a aljihun wandonsa,wanda ya zame masa al'ada idan ya sanya qananun kaya,idan ba waya hannunshi to zaka samu hannayen cikin aljihu ko harde a qirji.
Sallamarsa ce ta sanya baabaan dago kai yana dubansa,mai hali bai sauya halinsa,wasu daga al'adar turawa har yau sunqi barin mustaphan,ko da yake ta yaya zasu barshin bayan har yau shima bai bar cikinsu ba,sam baison manyan kaya,da wuya ka ganshi da su,cikin girmamawa ya qaraso ya duqa gaban baabaan yana gaida shi,amsawa shima yayi saidai fuskanshi sam babu walwala sabanin yadda ya saba ganinsa
"Yaushe ne zaka koma" hannayensa soke cikin juna ya amsa kamar wanda baison yin maganar
"Cikin wannan satin in sha Allah"
"Allah ya lamunce"
"Amin ya Allah". Shiru ne ya dan ratsa tsakaninsu,shi mustpha na sauraron me baaban zai gaya mishi tunda shi ya aikata takanas sashensa aka kira shi,yayin da shi kuma baaban yayi banza da shi,yana so yau ya qure miskilancinsa,yaci gaba da bude shafukan jaridar dake hannunsa,sam baka rabashi da duba jaridu,duk da bai cikin sabgogi da al'amuran gwamnati a bayyane amma a badini gangar jiki da zuciyarsa na tare da su.
Har ya kammala karatun jaridarsa baiji yace komai ba,hasalima da ya daga kansa sai yaga ya jingina bayansa da jikin kujera gami da miqe qafafunsa idanuwansa a lumshe,ajjiye jaridar yayi yana sauke ajiyar zuciya,glass dinsa ya zare shima ya ajjiye gefe yana dubansa
"wato ba zaka iya tambayar dalilin da ya sanya na kiraka ba kenan"miqewa yayi ya zauna sosai yana duban baaban
"nayi zaton baka kammala abinda kake bane,banson kuma katse ka"shuru yai ya jinjina kai,duk cikin 'ya'yansa bai haifi kamar mustapha ba har yau ta kowanni fanni ya tsrerema 'yan uwansa maza da mata
"me ya kaika ture yarinyar mutane har ta suma"
"Yarinyar mutane har ta suma?" Abinda ya dinga maimaitawa ciki kwanyarsa kenan,sam ya mance wace ce,wa baabaa ke fadi ya ambata cikin zuciyarsa
"Yarinya baquwa 'yar gidan alhj farouq" har ga Allah bai fuskanci kan wa baba ke magana ba,don shi baki daya ya mance lamarin,baaban ya kalla kamar yanason qarin bayani kan abinda yake cewa,baabaan yasan irin kallo,indai mustaphan yayi ba shakka yana buqatar qarin bayani
"Tashi kaje,ka kyauta ka kuma yi abinda ya dace,nima zanyi abinda ya dace din" duk da bai gane da wa yake nufin ba amma ya miqe kasancewar ya riga ya bashi umarni,cikin girmamawa ya rusuna yana cewa
"A huta lafiya" baban bai amsa shi ba har ya miqe ya juy,har ya taka daya biyu sai kuma ya juyo ya dawo ya sake rusunawa aladabce
"Dambun naman naka ya qare?" Ya fahimci me yake nufi,dambun naman da sumayya tayi masa ne,ya ganshi yana ci ya tsokaneshi da cewa gun saidawa aka siyo masa don yasan baison cimar siyarwa,yace idan ya qare zai masa magana ya sake siyo masa a inda aka siyo
"Bai qare ba" baban ya bashi amsa idonsa akanshi har ya miqe,baiyi qarya ba,mustaphan daban yake cikin yaranshi,kamar yadda yake da wasu baqin halaye haka dabi'unsa na kula da iyayensa suke,daban ya daukesu,martaba da darajarsu bai hada ta daya data wani halitta ba,cikin kowanne yanayi ko motsi nashi yakan sanya shi gaba,fatarshi da addu'arshi daya Allah ya azurta shi da zuriyya dayyiba saliha,wadda zata ji qansa yadda yake jin qan nashi iyayen.
***** ****** ****** *****