Sashe 109
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 7 min read
Kyakkyawan gani idanunshi suka yi masa,da fari ya dauke kanshi kasancewarsa wanda baison shiga sabgar da ba tashi ba amma sai qwaqwalwarsa ke gaya mishi kamar ya santa,sake maida idanuwansa yayi wajen,ita dince,gaban motar wani yana janye mata mayafi,ci gaba da kallon wajen yayi har ta kammala ta ta maida kanga ciki taja murfin ta rufe
"Yammatan yanzu?,duka sammakal suke ne?" Ya tambayi kanshi,sai ya danna madanni glass din ya koma ya rufe yadda yake,wani tsakin ya kuma ja,gwara ya yita shan zafin da idanuwansa su dinga shishshigi kan lamuran da ba huruminsa bane.
Sam bata ma san abdur rahman ya janye mata mayafin ba,ta kammala ta kiqa masa gorar tana masa godiya
"Ai yiwa kaine" ya fada yana murmushi,itama murmushin tayi don a yanzu ita ba qaramar yarinya bace ta fuskanci me yake fadi.
Fita sukayi dukansu har bahijja tace zata shiga ta gaida mama,bai hanata ba don yana da buqatar sararin da zaiyi magana da ita,kallonta yake har ta gaji ta tanka
"Kada fa ka cinyeni"
"Da hakan zai yiwu da nafi kowa farinciki,kinga idan ma cinyeki kin tabbata mallakina ni kadai har abada,wani ma bazai ganki ba bare ya qyasa" kunya kalamansa suka bata,saita maida kanta daya barin tana sauke murmushi
"Naga ma sai wani shamin qamshi ake,ko da yake girmanki ne,shekara kwana inji 'yan magana,ina maganarmu ta kwana sumayya?,nayi haquri sosai fa,dukkan kuma wani abu da nake saka ran kammaluwarshi ya kammala,jibi in sha Allah za'a bude asibiti,ya muke ciki,ko baki yarda ba wannan karon inajin ta qarfin tuwo zan qwace ki"
"Amma dai kasan ko budurwa bai halatta ayi mata auren dole va bare bazawara" ta fada tana dariya qasa qasa
"Kada ki yimin haka sumayya" ya fada a marairaice,ta jima tana nazarin abdur rahman din,bata da wata mafita yanzu,babu hanyar tsira,koda bata auri abdur rahman ba dole ta auri wani a gaba wanda bata san wayeshi ba,ta tabbata malam bazai barta ta rayu haka ba tunda har ya fara yi mata gugar zana,zata tanqwara zuciyarta,ta kwatanta karbarsa taga ni,bata san me gaba zata haifar ba,amma me mutane zasu ce idan sukaji zata auri dan wan baban mukhtar,wanda shi saurayi ne ita din bazawara ce?,wacce iriyar fassara zasu masu,meye matsayar hajiyarshi?,da wace fuska zata kalli batun
"Ka cancanta abdur rahman,bazan hanaka damarka da Allah ya baka ba,amma kamim haquri kada ka sanar da malam har zuwa sanda za'a kammala bikin zainab,na tabbata idan ka gaya masa yanzu zaice zai hada da ni ne,wanda ya kamata kafin sannan ace mun sake fahimtar juna kan zaman da zamu tukara da tsara abinda ya dace" hannunshi ya dunqule kawaj saboda tsabar farinciki
"Amincewa da yardarki kawai ta isheni farinciki,na godewa Allah,bazan takura ki ba ki kammala shirinki a nutse,amma don Allah a yimin alfarma nayi azumim bana a dakina"ya fada a marairaice,dariya ya bata har sai data qunshe bakinta,wai a dakinsa sai kace wani mace
"Allah ya zaba mana abinda yafi alkhairi"
"Amin ya Allah,ki shiga ki sauya kaya ki huta naga kaman yoghourt din dake jikinsu ya hanaki sakewa,bazan iya shiga gun mama ba kunyarta nakeji kinsan ta zaka suruka,sai gobe insha Allah zan kawo musu katin gayyatar bude asibitin shi da yaya abbakaf,ki turon bahijja" ya fada yana sanya mata kudade a jakarta,kudi sam ba matsalarta bane yanzun amma tun kafin tace komai yace baiso tace komai din,tilas ta dauki jakar tana masa godiya ya bita da kallo har ta shige gidan wani madaukakin farinciki na ratsashi.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽[1/25, 11:26 PM] +234 909 381 1661: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
6⃣9⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*KU SHIGO CIKI KUJI*
*ALLAH YANA FADA CIKIN QUR'ANINSA MAI GIRMA*
*MISALIN ALJANNAR DA AKA YIWA MASU IMANI ALQAWARI,A CIKINTA AKWAI QORAMU NA RUWA WANDA BAI JIRKITA BA,DA QORAMU NA NONO WANDA DANDANONSA BAI SAUYA BA,DA QORAMU NA GIYA WADDA TAKE MAI DADIN DANDANO GA MASU SHA(WADDA BATA SAKA MAYE KO TAMBELE),DA QORAMU NA ZUMA TATACCIYA,KUMA A CIKINTA SUNA DA(SU 'YAN ALJANNA)NAU'IN KOWANNE IRIN KAYAN MARMARI(DAN ICE)*
*kai jama'a wannan ni'ima da yawa take,idan kaso ka zama TATACCEN QASAITACCEN DAN GIYA AMMA FA NA ALJANNAH,ya Allah ka sanyamu cikinta don rahamarka*
________________________________________
Kafin su kai ga fita daga airphort din ruwan sama ya sauka,hakan ya hadu da duhun magariba ya kawo qarancin jama'a bisa titi,idanuwan sumayya qur bisa kwalta yadda ruwan ke sauka yana wanketa,a duk sanda ruwam sama zai sauka sai ya mata tunin mukhtar kamar ko yaushe.
Rashin daukewar ruwan har suka isa gida shi ya sabbaba driban ya shige da su baki daya cikin gidan baaban ba tare da sumayya ta samu damar sauka ba kamar yadda taso,saboda Abdallah wanda ya jima da yin barci kan cinyar amira,ruwan na iya tabashi,da ita daya ce da da sauqi.
Lema kubra ta shiga ta dauko musu sannan suka fito,suka taka har cikin gidan.
Lallai kam wannan biki ba qarami bane,baki daya harabar gidan ko ina an kafa tempol,duk da gidan bai wani cika rana ba,duk da ruwan da ake tsulawa hakan bai hanaka ganin mutane na kai kawo daga wannan sashi zuwa wancan sashi ba,a haka suka qarasa bangaren ummee,falonta cike yake da baqi,yan uwa qawaye da abokan arziqi,ga 'yan rano nan wanda ko ba'a gaya ma ba kana kallonsu kasan jinin ummee ne,jinin sarauta,ga 'yammata nan ko ina zazzaune kowa na nashi harkan,shigar amiran ya sanya hanaklin sh dawowa kanta,masu tsokana nayi masu mata barka da dawowa nayi,da qyar ta yakice suka hau falon sama na ummee wanda tana can.
Karon farko da sumayyan ta taba shigarshi,falo ne dan gaske,wanda ya mallaki duk wasu kayan alfarma,baki daya kwalliyar falon ta da duk abinda aka zuba mishi na sarauta ne,kama daga royal chairs zuwa fentin falon,yayi matuqar burge sumayyan ba kadan ba,ummen ma zaune kan daya cikin kujerun falon tana irga sabbabin kudi wanda suke daure a rafarsu,ita da wasu mata ne wadanda kusan cousin dinta ne da suka taso tare tun zamanin 'yammatanci,qarasawa amira tayi ta kwantar da abdallah kan daya cikin kujerun,ummee ta dubeshi tana musu sannu da qarasowa ita da sauran 'yan dakin,a ladabce sumayya ta qarasa gabanta ta duqa tana gaidata,ta amsa fuska sake tana cewa
"Amira ta hanaki sakat ko sai data daukoki" murmushi tayi kawai amiran tace
"Ummee ba'a shiga tsakaninmu"
"Au ai dama itaku amira" ta fada tana kiran daya daga cikin ma'aikatanta ta wayar hannu tana tambayarta an gama gyara dakin da tace,sai data gama wayar ta dubi amira
"Kije an gama gyara muku dakin,saiki sanya a kawo muku abinci,ki duba abinda kuke da buqata ki kira mama uwani ki sanar mata,su ummu salma ma ina zaton suna dakin tun dazun suke qorafin rashin dawowarki gashi gobe kamu"
"To ummee na" amiran ta fada tana miqewa
"Muje,ummee idan abdallah ya tashi ki bada shi a kawo mana shi" ta fada tana nuna abdallahn dake kwance yana baccinsa lakadan,kai ummim ta daga don bata son yin magana ta sake bata a lissafin.
Dakina babba sosai wanda ya babu komai cikinsa sai carfet da aka malale shi da shi,katifune saman carfet din ko ina aka kwakwkwantar,yayin da aka lullube kowacce katifa da zanin gado abun rufa da filo qwaya daya alamar kowacce ta kwanciyar mutum guda ce,sai toilet qwaya biyu cikin dakim,da qaton madubi da ya kusa cinye rabin bango,mutum biyar suka taras a dakin,wasunsu na hira wasu na cin abinci,shewa suka sanya da ganin shigowar amaryar,kowacce da abinda zata fadi,nan suka zube aka gaisa suna ci gaba da surutaj,itakam sumayya na gefe tana kallonsu,rayuwar wayewa kawai ake a wannan familyn,kowacce ka gani tana ji da wayewa kyau da arziqin gidansu,akwai alama dake nuna suna da zumunci da kara,sannan akwai sabo da fahimtar juna tsakaninsh,wanda hakan baya rasa nasaba da yadda baabaa prof ya hadasu baki daya ya rungume kowa,duk sallah babba da qarama duk 'ya'yan 'yan uwan na gidansa,baya banbantawa da nashi dangin dana matansa,shi ya sanya kowa yasan kowa,'yammata ne hadaddu wannan na wace wancan ta fada a ranta tana murmushi.
Agogon fata na kamfanin gucci purple dake daure a hannunta ta duba ganin ruwan ya tsagaita sai yayyafi wanda take iya gani ta window din dakin albarkacin hasken lanatarkin da yake tarwai kowane lungu da saqo na gidan
"Zan wuce fa amira" inji sumayya ganin yadda amiran ta bararraje tana kwasar hira,duka sai hankalin su ya dawo kanta har taji nauyin yadda kowa ya dora mata idonshi
"Wasa fa kike amirah,kin manta alqawarinmu,ai ga gun kwanaki nan har na bar gidan nan" sai ta karyar da wuya tana murmushi
"Amma dai ai kya bari naje naga anty ko?"
"Eh,wannan kuma,kuma ai ban ma gama ganinki ba,muje part din anty maamaa akwai abinda zaki gani idan kin dawo na nuna miki sauran" ta fada tana miqewa,itama tashin tayi suka fito,har sun kai qofa tace
"One minute don Allah sis,bari na dauko kayan waccan jarababbar na kai mata,Allah yasa ya musty bai nan" kafin tace komai har ta juya da sauri ta koma,tsayawa tayi tana jiranta gabanta na faduwa,tana addu'an kada Allah ya sa tace sai ta rakatan,don gaskiya ba abinda zai hanata ce mata ba zata ba.
"Yammatan yanzu?,duka sammakal suke ne?" Ya tambayi kanshi,sai ya danna madanni glass din ya koma ya rufe yadda yake,wani tsakin ya kuma ja,gwara ya yita shan zafin da idanuwansa su dinga shishshigi kan lamuran da ba huruminsa bane.
Sam bata ma san abdur rahman ya janye mata mayafin ba,ta kammala ta kiqa masa gorar tana masa godiya
"Ai yiwa kaine" ya fada yana murmushi,itama murmushin tayi don a yanzu ita ba qaramar yarinya bace ta fuskanci me yake fadi.
Fita sukayi dukansu har bahijja tace zata shiga ta gaida mama,bai hanata ba don yana da buqatar sararin da zaiyi magana da ita,kallonta yake har ta gaji ta tanka
"Kada fa ka cinyeni"
"Da hakan zai yiwu da nafi kowa farinciki,kinga idan ma cinyeki kin tabbata mallakina ni kadai har abada,wani ma bazai ganki ba bare ya qyasa" kunya kalamansa suka bata,saita maida kanta daya barin tana sauke murmushi
"Naga ma sai wani shamin qamshi ake,ko da yake girmanki ne,shekara kwana inji 'yan magana,ina maganarmu ta kwana sumayya?,nayi haquri sosai fa,dukkan kuma wani abu da nake saka ran kammaluwarshi ya kammala,jibi in sha Allah za'a bude asibiti,ya muke ciki,ko baki yarda ba wannan karon inajin ta qarfin tuwo zan qwace ki"
"Amma dai kasan ko budurwa bai halatta ayi mata auren dole va bare bazawara" ta fada tana dariya qasa qasa
"Kada ki yimin haka sumayya" ya fada a marairaice,ta jima tana nazarin abdur rahman din,bata da wata mafita yanzu,babu hanyar tsira,koda bata auri abdur rahman ba dole ta auri wani a gaba wanda bata san wayeshi ba,ta tabbata malam bazai barta ta rayu haka ba tunda har ya fara yi mata gugar zana,zata tanqwara zuciyarta,ta kwatanta karbarsa taga ni,bata san me gaba zata haifar ba,amma me mutane zasu ce idan sukaji zata auri dan wan baban mukhtar,wanda shi saurayi ne ita din bazawara ce?,wacce iriyar fassara zasu masu,meye matsayar hajiyarshi?,da wace fuska zata kalli batun
"Ka cancanta abdur rahman,bazan hanaka damarka da Allah ya baka ba,amma kamim haquri kada ka sanar da malam har zuwa sanda za'a kammala bikin zainab,na tabbata idan ka gaya masa yanzu zaice zai hada da ni ne,wanda ya kamata kafin sannan ace mun sake fahimtar juna kan zaman da zamu tukara da tsara abinda ya dace" hannunshi ya dunqule kawaj saboda tsabar farinciki
"Amincewa da yardarki kawai ta isheni farinciki,na godewa Allah,bazan takura ki ba ki kammala shirinki a nutse,amma don Allah a yimin alfarma nayi azumim bana a dakina"ya fada a marairaice,dariya ya bata har sai data qunshe bakinta,wai a dakinsa sai kace wani mace
"Allah ya zaba mana abinda yafi alkhairi"
"Amin ya Allah,ki shiga ki sauya kaya ki huta naga kaman yoghourt din dake jikinsu ya hanaki sakewa,bazan iya shiga gun mama ba kunyarta nakeji kinsan ta zaka suruka,sai gobe insha Allah zan kawo musu katin gayyatar bude asibitin shi da yaya abbakaf,ki turon bahijja" ya fada yana sanya mata kudade a jakarta,kudi sam ba matsalarta bane yanzun amma tun kafin tace komai yace baiso tace komai din,tilas ta dauki jakar tana masa godiya ya bita da kallo har ta shige gidan wani madaukakin farinciki na ratsashi.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽[1/25, 11:26 PM] +234 909 381 1661: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
6⃣9⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*KU SHIGO CIKI KUJI*
*ALLAH YANA FADA CIKIN QUR'ANINSA MAI GIRMA*
*MISALIN ALJANNAR DA AKA YIWA MASU IMANI ALQAWARI,A CIKINTA AKWAI QORAMU NA RUWA WANDA BAI JIRKITA BA,DA QORAMU NA NONO WANDA DANDANONSA BAI SAUYA BA,DA QORAMU NA GIYA WADDA TAKE MAI DADIN DANDANO GA MASU SHA(WADDA BATA SAKA MAYE KO TAMBELE),DA QORAMU NA ZUMA TATACCIYA,KUMA A CIKINTA SUNA DA(SU 'YAN ALJANNA)NAU'IN KOWANNE IRIN KAYAN MARMARI(DAN ICE)*
*kai jama'a wannan ni'ima da yawa take,idan kaso ka zama TATACCEN QASAITACCEN DAN GIYA AMMA FA NA ALJANNAH,ya Allah ka sanyamu cikinta don rahamarka*
________________________________________
Kafin su kai ga fita daga airphort din ruwan sama ya sauka,hakan ya hadu da duhun magariba ya kawo qarancin jama'a bisa titi,idanuwan sumayya qur bisa kwalta yadda ruwan ke sauka yana wanketa,a duk sanda ruwam sama zai sauka sai ya mata tunin mukhtar kamar ko yaushe.
Rashin daukewar ruwan har suka isa gida shi ya sabbaba driban ya shige da su baki daya cikin gidan baaban ba tare da sumayya ta samu damar sauka ba kamar yadda taso,saboda Abdallah wanda ya jima da yin barci kan cinyar amira,ruwan na iya tabashi,da ita daya ce da da sauqi.
Lema kubra ta shiga ta dauko musu sannan suka fito,suka taka har cikin gidan.
Lallai kam wannan biki ba qarami bane,baki daya harabar gidan ko ina an kafa tempol,duk da gidan bai wani cika rana ba,duk da ruwan da ake tsulawa hakan bai hanaka ganin mutane na kai kawo daga wannan sashi zuwa wancan sashi ba,a haka suka qarasa bangaren ummee,falonta cike yake da baqi,yan uwa qawaye da abokan arziqi,ga 'yan rano nan wanda ko ba'a gaya ma ba kana kallonsu kasan jinin ummee ne,jinin sarauta,ga 'yammata nan ko ina zazzaune kowa na nashi harkan,shigar amiran ya sanya hanaklin sh dawowa kanta,masu tsokana nayi masu mata barka da dawowa nayi,da qyar ta yakice suka hau falon sama na ummee wanda tana can.
Karon farko da sumayyan ta taba shigarshi,falo ne dan gaske,wanda ya mallaki duk wasu kayan alfarma,baki daya kwalliyar falon ta da duk abinda aka zuba mishi na sarauta ne,kama daga royal chairs zuwa fentin falon,yayi matuqar burge sumayyan ba kadan ba,ummen ma zaune kan daya cikin kujerun falon tana irga sabbabin kudi wanda suke daure a rafarsu,ita da wasu mata ne wadanda kusan cousin dinta ne da suka taso tare tun zamanin 'yammatanci,qarasawa amira tayi ta kwantar da abdallah kan daya cikin kujerun,ummee ta dubeshi tana musu sannu da qarasowa ita da sauran 'yan dakin,a ladabce sumayya ta qarasa gabanta ta duqa tana gaidata,ta amsa fuska sake tana cewa
"Amira ta hanaki sakat ko sai data daukoki" murmushi tayi kawai amiran tace
"Ummee ba'a shiga tsakaninmu"
"Au ai dama itaku amira" ta fada tana kiran daya daga cikin ma'aikatanta ta wayar hannu tana tambayarta an gama gyara dakin da tace,sai data gama wayar ta dubi amira
"Kije an gama gyara muku dakin,saiki sanya a kawo muku abinci,ki duba abinda kuke da buqata ki kira mama uwani ki sanar mata,su ummu salma ma ina zaton suna dakin tun dazun suke qorafin rashin dawowarki gashi gobe kamu"
"To ummee na" amiran ta fada tana miqewa
"Muje,ummee idan abdallah ya tashi ki bada shi a kawo mana shi" ta fada tana nuna abdallahn dake kwance yana baccinsa lakadan,kai ummim ta daga don bata son yin magana ta sake bata a lissafin.
Dakina babba sosai wanda ya babu komai cikinsa sai carfet da aka malale shi da shi,katifune saman carfet din ko ina aka kwakwkwantar,yayin da aka lullube kowacce katifa da zanin gado abun rufa da filo qwaya daya alamar kowacce ta kwanciyar mutum guda ce,sai toilet qwaya biyu cikin dakim,da qaton madubi da ya kusa cinye rabin bango,mutum biyar suka taras a dakin,wasunsu na hira wasu na cin abinci,shewa suka sanya da ganin shigowar amaryar,kowacce da abinda zata fadi,nan suka zube aka gaisa suna ci gaba da surutaj,itakam sumayya na gefe tana kallonsu,rayuwar wayewa kawai ake a wannan familyn,kowacce ka gani tana ji da wayewa kyau da arziqin gidansu,akwai alama dake nuna suna da zumunci da kara,sannan akwai sabo da fahimtar juna tsakaninsh,wanda hakan baya rasa nasaba da yadda baabaa prof ya hadasu baki daya ya rungume kowa,duk sallah babba da qarama duk 'ya'yan 'yan uwan na gidansa,baya banbantawa da nashi dangin dana matansa,shi ya sanya kowa yasan kowa,'yammata ne hadaddu wannan na wace wancan ta fada a ranta tana murmushi.
Agogon fata na kamfanin gucci purple dake daure a hannunta ta duba ganin ruwan ya tsagaita sai yayyafi wanda take iya gani ta window din dakin albarkacin hasken lanatarkin da yake tarwai kowane lungu da saqo na gidan
"Zan wuce fa amira" inji sumayya ganin yadda amiran ta bararraje tana kwasar hira,duka sai hankalin su ya dawo kanta har taji nauyin yadda kowa ya dora mata idonshi
"Wasa fa kike amirah,kin manta alqawarinmu,ai ga gun kwanaki nan har na bar gidan nan" sai ta karyar da wuya tana murmushi
"Amma dai ai kya bari naje naga anty ko?"
"Eh,wannan kuma,kuma ai ban ma gama ganinki ba,muje part din anty maamaa akwai abinda zaki gani idan kin dawo na nuna miki sauran" ta fada tana miqewa,itama tashin tayi suka fito,har sun kai qofa tace
"One minute don Allah sis,bari na dauko kayan waccan jarababbar na kai mata,Allah yasa ya musty bai nan" kafin tace komai har ta juya da sauri ta koma,tsayawa tayi tana jiranta gabanta na faduwa,tana addu'an kada Allah ya sa tace sai ta rakatan,don gaskiya ba abinda zai hanata ce mata ba zata ba.