Sashe 54
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abinda bata sani ba malam din na sane da komai,bata san da hakan ba sai ranar da aka kai kudin auren abubakar da saka rana wanda baki daya aka tsaida watanni biyu,washegarin ranar malam din yayi kiranta falonsa,bayan ya kammala duka abubuwan da yake ya dubeta
"Am sumayya,nasan cewa kinsan tsarina da al'ada ta gidan nan,sannan alhamdulillah kin san mutuncin mace dakin mijinta,baki da inda yafi nan daraja,dukkan wani abu da ya faru a baya mu ajjiyeshi gefe haka Allah ya tsarama rayuwarki,cikin KUNDIN QADDARARKI yake,babu wanda ya isa ya goge miki ko ya kautar miki da shi"
"Haka ne malam" ta fada kanta na duqe zuciyarta ba bugawa kamar zata bullo,addu'a take kada Allah yasa malam ya bullo mata da zancan da bata da buqatar jinsa a yanzu
"Sumayya,yaron nan abdur rahman yazo guna ya gabatar min da kansa a matsayin manenin aurenki,to amma kasancewarki bazawara a yanzu addini ya baki damar zabawa kanki mijin aure ya sanya nace sai na tambayeki naji mene ne ra'ayinki,kada ki zalunci kanki a yanzu kina da dama,sannan zaman aure zama ne bana yau ko gobe kawai ba,zama ne na har abada". Wani tashin hankali ne ya rikito mata,abubuwan da suka dinga faruwa da ita zamanin tana auren mukhtar tsaf suka dinga dawo mata,a hankali ta bude bakinta muryarta na rawa
"Kayi haquri malam,abdur rahman dan uwa ne ga mukhtar dan wan babansa ne nasan kasan haka malam" murmushi ya saki
"Sumayya,sumayya kenan,wannan duka ba abun damuwa bane tunda dai aure ya halasta a tsakaninku ba haramun bane" tashin hankali ta fada cikin zuciyarta,'yan uwan mukhtar fa sune dai 'yan uwan abdur rahman,ba'a canzawa tuwo suna
"Malam,ina tsoron sake kasancewa da ahalin su mukhtar...." Sai tayi shiru ta kasa qarasawa,shima shirun yayi yana nazarin maganarta,tabbas sumayya yarinya ce mai matuqar zurfin ciki,a iya zamanta na aure bazai iya fadar ranar data kawo matsalarta ba,saidai idan an fahimta a maganta mata.
"Ke kike da zabi a hannunki ai,ba zan miki auren dole ba"
"Malam,ina so abdur rahman ya janye daga qudurinsa,bana son sake shiga ahalinsu" ta fada zuciyarta na raurawa muryarta na rawa
"Shikenan zancansa ya wuce,sai ki fidda miji ina son hada aurenki da na yayanki abubakar idan ta kama har da su halima baki daya"
"Amma malam ba......."
"Sumayya,bana son qorafi ko wata magana,kinsan ba zaiyiwu kici gaba da zama a gida ba,shekara nawa,shekara daya ana gab da cika ta biyu" shuru tayi don tafi kowa sanin waye malam,amma ina mafita meye mafitarta?,
"Sumayyan luqman fa?" Taji ya jefo mata tambayar wadda ta sanya dago kanta ta dubeshi,murmushi ya kuma yi yana dubanta
"Mamaki kike yadda na sanshi?,ya fara zuwa gunki ba da izini ba ya karya doka ta,hakan ya sanya nayi bincike a kansa,na samu gamsassun bayanai a kansa,mutumin kirki ne bakin gwargwado" sai ya dan ja fasali yana dubanta kafin yaci gaba da cewa.
_yauma dai amin uziri_
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
*ASSALAMU ALAIKUM*
*mas’alar saki uku cikin kalma guda*
_idan mutum ya saki matarsa saki uku_ _karkashin kalma daya ana daukan haka a matsayin saki daya ne tun asali.Haka wannan mas’alar take tun zamanin manzo S.A.W. har zamanin mulkin_ _sayyadina Abubakar.A lokacin da Khalifa Umar ya hau karagar khalifanci da shekaru biyu,sai sake-saken mata ya yawaita, don haka sai ya tsawatar da cewa; duk wanda ya sake sakin iyalinsa saki uku, to zamu dauka saki ukunne da gaske !!!_
_A mazhabarmu ta Malikiyya wadda da ita muke aiki duk macen da aka saka saki uku a kalma guda ta saku saki uku, amma akwai malaman da suke ganin za'a bar shi a saki daya, tun da haka ake hukuntawa a zamanin Annabi S.A.W. da zamanin Abubakar RA da wani bangare na_ _zamanin Umar RA, kamar yadda hadisin Ibnu Abbas ya tabbatar da hakan_
_Allah ne mafi sani._
_Mafiya yawancin malamai sun rinjayar da saki uku a kalma daya ya tabbata saki ukun ne saboda toshe qofar barna kamar yadda sayyadina umar R.A yayi,saboda a zamanin da muke ciki muna hukunci da saki ukun idan akayi ya tabbata ya muka cika balle kuma ace ukun a matsayin daya yake?_
_Allah shine mafi sani._
*hhh,har yau fans kun kasa cankar dai dai game da abinda zai faru gaba cikin littafin kundin qaddara ta,saidai wasu kan kwatanta,so saboda haka ku bani gari kawai kuyi kurum kuci gaba da bibiya ta*
_______________________________
"Lukman na da matar aure daya da yara hudu,hakan shike nuna zaiyi riqon Allah tunda har yana da wata matar ya saba riqon macen aure,bawai zaiyi aurensa na fari bane,amma kije kiyi tunani kina da sauran lokaci har kwanaki talatin,Allah ya zaba mana abinda yafi alheri,tashi kije".
Tamkar kazar da qwai ya fashewa a ciki haka take tafiya har ta isa dakin ta,kusan ranar baki daya akwance ta yita,tana jin abdallah yana qiriniyarsa har ya gama yayi bacci anan wurin.
**** ***** ***** *****
Mukhtar bai fasa zuwa ganin yaronsa ba kamar yadda abdur rahman bai fasa zuwa gidan ba,saidai baki dayansu ganinta ya musu wahala,ba wanda take yarda ya ganta saidai bacin rana,ta bangare daya lukman naci gaba da nacin sake zuwa wajenta,saidai ko sau daya taqi yarda ya kuma zuwa din,wani irin so lukmam din ke mata wanda ke bata mamaki kuma ya fara sanya mata tausayinshi,duk randa baiji muryarta ba yakan zamo kamar wani soko ko zautacce,yayi ta jera kiran kenan har sai ta gaji ta daga,hakan ya sanya sau tari takan dan sassauta masa.
Lokaci ne yaci gaba da tafiya,kwanakin da malam ya diba mata na kuma tafiya,a haka har aka cimma kwanaki talatin din cif,saidai shirun da taji malam din bai tada mata maganar ba ya sanya ta kwantar da hankali ta ta kuma sake sakankancewa abinta,har aka fara sabgar shirye shiryen auren yaya abubakar da ita.
Ranar wata juma'a da wani yammaci wanda ya tasamma kwanaki arba'in da yin maganarta da malam bayan sakkowa sallar juma'a malam din ya dawo gida yaci abinci sannan ya sanya aka kira masa ita.
Tunda taji kiransa hankalinta yayi mummunan tashi,a lokacin suna dakin mama suna shirya akwatin kayan lefan yaya abubakar da ake saka ran kaiwa satin sama.
"Ya ake ciki sumayya,kwanakin da na diba miki sun shude har da doriya ba tare da naji komai daga bakinki ba".
Cikin yanayi na daburcewa tace
" eh malam dama.....dama.."
"Unhmmm,dama mene?,kin haqura kin zabi abdur rahman dinne" da sauri ta girgiza kai
"Ok,lukman din ne?" Nan ma kai ta girgiza,sai malam din ya sauya fuska sosai sannan yace
"Ki bude baki kimin magana sosai,idan ba haka ba zan bawa abdur rahman dama ya turo,saboda daga shi har lukman din babu mai aibu a cikinsa,aure kuwa mutunci da kamala shine abu mafi muhimmanci da za'a fara nema a cikinsa" tuni hawaye ya fara wanke mata fuska
"Malam bana son sake hada zama da su abdur rahman ka yimin afuwa" karo na farko da ta fara yima malam din musu,duk sai tajita wani iri,tana jin kamar tayi ba dai dai ba
"Shikenan,a bawa lukman din dama ya fito kenan?" Shiru tayi kamar wadda ruwa ya cinye,ta yaya zata sake musa masa bayan ba al'adarta bace?,baya ga haka kuma yayi bincike halayyarsa ta yi masa me zata ce kuma?,ganin batayi magana ba ya sanya ya sake maimaita tambayar tasa saidai nan ma shiru ne ya biyo baya bata ce komai ba,a bisa ga abinda addini ya nuna shiru alamar amincewa ce da hakan malam ya dauka cewa ta amince
"Shikenan,Allah ya tabbatar da alkhairi,Allah yayi miki albarka ya albarkaci aurenku,tashi ki tafi" abinda taji malam din ya fada kenan.
Ita dai bata san yadda aka yi ta kai kanta dakinta ba,sai tsintar kanta tayi saman katifarta tana malelekuwa hawaye na malala daga idanunta
"Shikenan,shikenan lukman cikin KUNDIN QADDARATA?," abinda ta dinga nanatawa kanta kenan,kuka tayi na fitar rai a ranar,sai ta dinga jin wani banbarakwai wai yau ita zata sake auren wani?,su zauna suyi rayuwar aure da shi.
Washe gari lukman ya kirata,murna kamar ya taka rawa cikin waya,daga qarshe yace mata jibi yana tafe in sha Allah bayan masu kawo kudi sun tafi.
Washe garin kuwa iyayen lukman suka iso,naira dubu dari suka kawo kudin har da kudin sa rana,sannan suka ce sati na sama za'a kawo lefe,duk yadda malam ya dakatar da bidi'ar da ya lura suna shirin yi amma sunqi,ganin cewa ko aurenta na fari bai karbi kudin aurenta har haka ba bare yanzu,sunce angon keson hakan tilas ya haqura.
Qarfe takwas ya kira wayarta ya shaida mata ya iso,ba wani abu da ta sanya ko ta sauya,kayan dake jikinta da hijabinta duka da su ta fita,fuskarnan duka a kode saboda kuka,mama na lura da ita amma sai ta alaqanta hakan da cewa wata qila tsananin sabo da rayuwar da sukayi da mukhtar ya sanyata take jin duka ba dadi zata sauya sheqa,ita dai da addu'a take binta tare da fatan alheri.
Yana zaune cikin motarsa sanye da shadda cream colour sai maiqo take,ta masa cas tare da yi masa kyau ta kuma haska kwantacciyar fatarsa kalar choculet,fuskarsa kawai zaka kalla kasan cike yake da farinciki da annashuwa,murmushi ne zallah kan fuskar tasa kadan kadan,lukman na cikin sahun tsaka tsaki na kyawawan maza,waqa ce ke tashi a motar tasa wadda aka ragewa sauti sautinta can qasa,wanda kalaman soyayya me kawai zalla cikin baitukan waqar.
"Am sumayya,nasan cewa kinsan tsarina da al'ada ta gidan nan,sannan alhamdulillah kin san mutuncin mace dakin mijinta,baki da inda yafi nan daraja,dukkan wani abu da ya faru a baya mu ajjiyeshi gefe haka Allah ya tsarama rayuwarki,cikin KUNDIN QADDARARKI yake,babu wanda ya isa ya goge miki ko ya kautar miki da shi"
"Haka ne malam" ta fada kanta na duqe zuciyarta ba bugawa kamar zata bullo,addu'a take kada Allah yasa malam ya bullo mata da zancan da bata da buqatar jinsa a yanzu
"Sumayya,yaron nan abdur rahman yazo guna ya gabatar min da kansa a matsayin manenin aurenki,to amma kasancewarki bazawara a yanzu addini ya baki damar zabawa kanki mijin aure ya sanya nace sai na tambayeki naji mene ne ra'ayinki,kada ki zalunci kanki a yanzu kina da dama,sannan zaman aure zama ne bana yau ko gobe kawai ba,zama ne na har abada". Wani tashin hankali ne ya rikito mata,abubuwan da suka dinga faruwa da ita zamanin tana auren mukhtar tsaf suka dinga dawo mata,a hankali ta bude bakinta muryarta na rawa
"Kayi haquri malam,abdur rahman dan uwa ne ga mukhtar dan wan babansa ne nasan kasan haka malam" murmushi ya saki
"Sumayya,sumayya kenan,wannan duka ba abun damuwa bane tunda dai aure ya halasta a tsakaninku ba haramun bane" tashin hankali ta fada cikin zuciyarta,'yan uwan mukhtar fa sune dai 'yan uwan abdur rahman,ba'a canzawa tuwo suna
"Malam,ina tsoron sake kasancewa da ahalin su mukhtar...." Sai tayi shiru ta kasa qarasawa,shima shirun yayi yana nazarin maganarta,tabbas sumayya yarinya ce mai matuqar zurfin ciki,a iya zamanta na aure bazai iya fadar ranar data kawo matsalarta ba,saidai idan an fahimta a maganta mata.
"Ke kike da zabi a hannunki ai,ba zan miki auren dole ba"
"Malam,ina so abdur rahman ya janye daga qudurinsa,bana son sake shiga ahalinsu" ta fada zuciyarta na raurawa muryarta na rawa
"Shikenan zancansa ya wuce,sai ki fidda miji ina son hada aurenki da na yayanki abubakar idan ta kama har da su halima baki daya"
"Amma malam ba......."
"Sumayya,bana son qorafi ko wata magana,kinsan ba zaiyiwu kici gaba da zama a gida ba,shekara nawa,shekara daya ana gab da cika ta biyu" shuru tayi don tafi kowa sanin waye malam,amma ina mafita meye mafitarta?,
"Sumayyan luqman fa?" Taji ya jefo mata tambayar wadda ta sanya dago kanta ta dubeshi,murmushi ya kuma yi yana dubanta
"Mamaki kike yadda na sanshi?,ya fara zuwa gunki ba da izini ba ya karya doka ta,hakan ya sanya nayi bincike a kansa,na samu gamsassun bayanai a kansa,mutumin kirki ne bakin gwargwado" sai ya dan ja fasali yana dubanta kafin yaci gaba da cewa.
_yauma dai amin uziri_
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
*ASSALAMU ALAIKUM*
*mas’alar saki uku cikin kalma guda*
_idan mutum ya saki matarsa saki uku_ _karkashin kalma daya ana daukan haka a matsayin saki daya ne tun asali.Haka wannan mas’alar take tun zamanin manzo S.A.W. har zamanin mulkin_ _sayyadina Abubakar.A lokacin da Khalifa Umar ya hau karagar khalifanci da shekaru biyu,sai sake-saken mata ya yawaita, don haka sai ya tsawatar da cewa; duk wanda ya sake sakin iyalinsa saki uku, to zamu dauka saki ukunne da gaske !!!_
_A mazhabarmu ta Malikiyya wadda da ita muke aiki duk macen da aka saka saki uku a kalma guda ta saku saki uku, amma akwai malaman da suke ganin za'a bar shi a saki daya, tun da haka ake hukuntawa a zamanin Annabi S.A.W. da zamanin Abubakar RA da wani bangare na_ _zamanin Umar RA, kamar yadda hadisin Ibnu Abbas ya tabbatar da hakan_
_Allah ne mafi sani._
_Mafiya yawancin malamai sun rinjayar da saki uku a kalma daya ya tabbata saki ukun ne saboda toshe qofar barna kamar yadda sayyadina umar R.A yayi,saboda a zamanin da muke ciki muna hukunci da saki ukun idan akayi ya tabbata ya muka cika balle kuma ace ukun a matsayin daya yake?_
_Allah shine mafi sani._
*hhh,har yau fans kun kasa cankar dai dai game da abinda zai faru gaba cikin littafin kundin qaddara ta,saidai wasu kan kwatanta,so saboda haka ku bani gari kawai kuyi kurum kuci gaba da bibiya ta*
_______________________________
"Lukman na da matar aure daya da yara hudu,hakan shike nuna zaiyi riqon Allah tunda har yana da wata matar ya saba riqon macen aure,bawai zaiyi aurensa na fari bane,amma kije kiyi tunani kina da sauran lokaci har kwanaki talatin,Allah ya zaba mana abinda yafi alheri,tashi kije".
Tamkar kazar da qwai ya fashewa a ciki haka take tafiya har ta isa dakin ta,kusan ranar baki daya akwance ta yita,tana jin abdallah yana qiriniyarsa har ya gama yayi bacci anan wurin.
**** ***** ***** *****
Mukhtar bai fasa zuwa ganin yaronsa ba kamar yadda abdur rahman bai fasa zuwa gidan ba,saidai baki dayansu ganinta ya musu wahala,ba wanda take yarda ya ganta saidai bacin rana,ta bangare daya lukman naci gaba da nacin sake zuwa wajenta,saidai ko sau daya taqi yarda ya kuma zuwa din,wani irin so lukmam din ke mata wanda ke bata mamaki kuma ya fara sanya mata tausayinshi,duk randa baiji muryarta ba yakan zamo kamar wani soko ko zautacce,yayi ta jera kiran kenan har sai ta gaji ta daga,hakan ya sanya sau tari takan dan sassauta masa.
Lokaci ne yaci gaba da tafiya,kwanakin da malam ya diba mata na kuma tafiya,a haka har aka cimma kwanaki talatin din cif,saidai shirun da taji malam din bai tada mata maganar ba ya sanya ta kwantar da hankali ta ta kuma sake sakankancewa abinta,har aka fara sabgar shirye shiryen auren yaya abubakar da ita.
Ranar wata juma'a da wani yammaci wanda ya tasamma kwanaki arba'in da yin maganarta da malam bayan sakkowa sallar juma'a malam din ya dawo gida yaci abinci sannan ya sanya aka kira masa ita.
Tunda taji kiransa hankalinta yayi mummunan tashi,a lokacin suna dakin mama suna shirya akwatin kayan lefan yaya abubakar da ake saka ran kaiwa satin sama.
"Ya ake ciki sumayya,kwanakin da na diba miki sun shude har da doriya ba tare da naji komai daga bakinki ba".
Cikin yanayi na daburcewa tace
" eh malam dama.....dama.."
"Unhmmm,dama mene?,kin haqura kin zabi abdur rahman dinne" da sauri ta girgiza kai
"Ok,lukman din ne?" Nan ma kai ta girgiza,sai malam din ya sauya fuska sosai sannan yace
"Ki bude baki kimin magana sosai,idan ba haka ba zan bawa abdur rahman dama ya turo,saboda daga shi har lukman din babu mai aibu a cikinsa,aure kuwa mutunci da kamala shine abu mafi muhimmanci da za'a fara nema a cikinsa" tuni hawaye ya fara wanke mata fuska
"Malam bana son sake hada zama da su abdur rahman ka yimin afuwa" karo na farko da ta fara yima malam din musu,duk sai tajita wani iri,tana jin kamar tayi ba dai dai ba
"Shikenan,a bawa lukman din dama ya fito kenan?" Shiru tayi kamar wadda ruwa ya cinye,ta yaya zata sake musa masa bayan ba al'adarta bace?,baya ga haka kuma yayi bincike halayyarsa ta yi masa me zata ce kuma?,ganin batayi magana ba ya sanya ya sake maimaita tambayar tasa saidai nan ma shiru ne ya biyo baya bata ce komai ba,a bisa ga abinda addini ya nuna shiru alamar amincewa ce da hakan malam ya dauka cewa ta amince
"Shikenan,Allah ya tabbatar da alkhairi,Allah yayi miki albarka ya albarkaci aurenku,tashi ki tafi" abinda taji malam din ya fada kenan.
Ita dai bata san yadda aka yi ta kai kanta dakinta ba,sai tsintar kanta tayi saman katifarta tana malelekuwa hawaye na malala daga idanunta
"Shikenan,shikenan lukman cikin KUNDIN QADDARATA?," abinda ta dinga nanatawa kanta kenan,kuka tayi na fitar rai a ranar,sai ta dinga jin wani banbarakwai wai yau ita zata sake auren wani?,su zauna suyi rayuwar aure da shi.
Washe gari lukman ya kirata,murna kamar ya taka rawa cikin waya,daga qarshe yace mata jibi yana tafe in sha Allah bayan masu kawo kudi sun tafi.
Washe garin kuwa iyayen lukman suka iso,naira dubu dari suka kawo kudin har da kudin sa rana,sannan suka ce sati na sama za'a kawo lefe,duk yadda malam ya dakatar da bidi'ar da ya lura suna shirin yi amma sunqi,ganin cewa ko aurenta na fari bai karbi kudin aurenta har haka ba bare yanzu,sunce angon keson hakan tilas ya haqura.
Qarfe takwas ya kira wayarta ya shaida mata ya iso,ba wani abu da ta sanya ko ta sauya,kayan dake jikinta da hijabinta duka da su ta fita,fuskarnan duka a kode saboda kuka,mama na lura da ita amma sai ta alaqanta hakan da cewa wata qila tsananin sabo da rayuwar da sukayi da mukhtar ya sanyata take jin duka ba dadi zata sauya sheqa,ita dai da addu'a take binta tare da fatan alheri.
Yana zaune cikin motarsa sanye da shadda cream colour sai maiqo take,ta masa cas tare da yi masa kyau ta kuma haska kwantacciyar fatarsa kalar choculet,fuskarsa kawai zaka kalla kasan cike yake da farinciki da annashuwa,murmushi ne zallah kan fuskar tasa kadan kadan,lukman na cikin sahun tsaka tsaki na kyawawan maza,waqa ce ke tashi a motar tasa wadda aka ragewa sauti sautinta can qasa,wanda kalaman soyayya me kawai zalla cikin baitukan waqar.