← Book details Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 56 OF 210

Sashe 56

Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read

_haqiqa Allah baya canzawa mutane(halin ko yanayin da suke ciki)har sai sun canza da kansu_

______________________________

Ungawa ce mai matuqar kyau da tsari,akwai nauikan mutane daban daban cikinta,saidai akasarin mzauna cikinta din masu hannu da shuni ne da kuma masu rufin asiri ko wadanda suke ma'aikatan gwamnatin tarayya ta basu gida su zauna kamar su anty dije.

Sai da mansur ya fidda kayanta baki daya ya shigar mata cikin gidan ta masa godiya sosai sannan ya ja motarsa ya shige wani katafare kuma hamshaqin gida dake kallon nasu.

Dukka yaran gidan na nan kasancewar ranar qarshen mako ce,laila ita ce babba,sai hafiz mai bi mata,sannan khalifa sai nasir sai auta amina minal,a qalla laila zata yi shekaru goma sha hudu,ita ta fara ganin shigowar sumayya falon,ihu ta sanya wanda ya janyo hankalin 'yan uwanta ta nufi sumayya ta rungumeta,haka sauran suka baibayeta wanda ya janyo musu faduwa a qasa dukansu suna dariya,da qyar ta samu suka dagata suka koma saman kujera sannan ta soma tambayarsu anty dijen don bata ji motsinta ba,dining laila ta nuna wa sumayyan tana cewa
"Kinga yaya sumayya can duka abincinki ne,tun dazu mama ke jiranki baku iso ba har ta gaji ta shiga gidan daddy prof,amma bari naje na kirata" ta fada tana yafa dan yalolon mayafinta tayi waje da sauri,khalifa sumayya tasa ya fara nuna mata toilet ta shiga tayi alwala,tana kammala alwalar anty dije na shigowa
"Sai yanzu?,gaskiya kunyi nauyi a hanya kamar wadanda suka hau motar haya inji hajiya bilki" murmushi sumayya tayi tana duban anty dije wadda ta sake gogewa bisa dukkan alamu zaman garin ya karbeta matuqa,ta kuma zama 'yar gayu ita da yaranta baki daya
"Wallahi anty sai da muka biya kasuwa muka karbo wasu kaya sannan har mun dau hanya wani oga ko yallabai ya maida ku zoo road karbo dinki"
"Eh inaga man ne dinkunan su'ad ce,maza yi sallar kizo kici abinci kafin mu zauna hirar yashe gamo" ta fada tana sanya su laila dauke akwatunta zuwa wani daki da aka tanada saboda baqi irinta.

Sai da taci ta qoshi sannan suka baje a falon ana hiran yaushe gamo,kusan haka suka qarar da wunin ranar,ko da malamar lesson din yaran ma tazo guduwa sukayi suka qi zuwa sai tafiya tayi,da dare ma yayi da qyar suka tafi dakinsu don cewa sukayi tare da sumayyan zasu kwana,saida anty dije ta korasu saboda tana son suyi zance,sosai suka sake kuwa don mai gidan ta baya nan sun tafi semina lagos,sosai anty dije ta sake kwantar mata da hankali tare da bata shawarwari ta rufe da fadi cikin sigar tsokana
"Duk da nasan sumayyan tawa zuwa yanzu ta fara girma,hankali ya fara zuwa mata" itama dariya tayi,sai wajen sha daya da rabi sannan ta fita ta barta,to nan din ma lukman bai barta ba da hira sai data ce tana jin bacci sannan yace
"Ki kula min da kanki to na baki amanar kanki my dear kinji"ajiyar zuciya ta saki sannan ta amsa masa ta katse kiran,taso kiran halina taji ya abdallah yake,amma ganin dare yayi nisa ya sanyata ta haqura ta barwa gobe,duk sai taji tana kewar yaron nata.

****** ****** ******

Kwanakin da tayi a garin kwanaki ke da suka yi mata dadi sosai,kullum yaran na nanuqe da ita suna hira,sauqin abun sun gama jarabawa hutu kawai suke jira,wani lokaci da yammaci anty dije kan debe su da motar mai gidan da ya barta a gida ta kaisu park su dan sha iska suyi ciye ciye su dawo,hakan na yiwa sumayya dadi,lallai ko yaya ka motsa daga wani gu zuwa wani gu zaka samu sauyi zuciyarka zata yi dadi.

Duk wani abu da ya kamata a yiwa amarya anty dije da kanta ta yiwa sumayya,cikin kwana goma ta hadata tsaf.

Ana ya gobe zasu koma kanon laila na kwance kan cinyar sumayya sumayyan na tsefe mata kitsonta zasu wankin gashi da yamma anty dije ta fito ta dubesu
"zan dan shiga gidan daddy prof zamuyi sallama da su,Allah baiyi da ni za'a yi sunan nan ba"sumayya ta daga kai ta dubi anty dije
" au haihuwa akayi halan?"
"Sai yau zaki tambaya kenan,kwana na nawa ina leqa su amma baki taba karar ki shiga ku gaisa da mutanen ba,direban gidan ya dauko ki daga kano fa,surukar gidan ce ta haihu" murmushi sumayya tayi
"To ai ban sansu bane anty"
"Ni ai na sansu kuma gashi na gaya miki,mutanen akwai tsabar mutunci da karrama mutum,duk yadda Allah ya musu tsabar arziqi amma basu raina na qasansu,mai gidan bakiga yadda ya dauki abban khalifa ba kamar dan cikinsa,su khalifa kuwa ya maidasu tamkar jikokinsa" jinjina kai sumayya keyi sannan tace
"Allah ya saka musu da alkhairi,kice ina musu barka"
"Zasuji tunda ba zaki din ba" inji anty dije ta fice tana mita sumayya ta bita da dariya.

Basu jima da kammala tsifar ba anty dijen ta dawo hannunya dauke da baqar leda,ta cillar kan cinyar sumayya
"Da baki iya zuwa gaida mutane ba gashinan haj bilkisu tace na kawo miki kiyi fitar biki,ta yaba da zabin leshin ki wai kin iya zabar kala,ashe tare kuka shiga shagon da mansur din". Baki ta saki sanda ta fiddo leshin taga daya daga cikin wadanda suka siya dinne
"Anty kinsan kuwa nawa ne farashinsa duk guda daya?". Dariya anty dijen tayi
"Hmmmmm,bakisan mutan gidan bane sumayya,kinga ku tashi ku shirya ku wuce wankin kan nan kada dare yayi muku hanya"ta furta tana miqewa ta nufi kitchen.

****** ******* *******

Sanda suka isa kwanaki biyu sukayi saura a daura aure don babu wani event da sumayyan ta tsara yi,yaya abubakar ne kawai zaiyi walima bayan an gama daura aure.

Kusa awa guda kenan da shigowarta gidan amma bata ga wulgawar abdallah ba,tun tana kawaici bata tambaya ba har sai data magantu
"wai nikam ina abdallah ne?" Maimakon maman ta amsa mata sai tace da ita
"Kije malam nason magana da ke" hakanan taji jikinta bai bata ba,ta miqe ta zura hijabinta ta fice.

A ladabce ta gaisheshi ya amsa yana tsokanarta abuja ta karbeta,sai ya bata kunya ta sunkui da kai tana murmushi yayin da tausayinta kuma ya darsu a zuciyar malam din
"Sumayya maganar da zamuyi da ke nasan ba zata miki dadi ba,domin raba da da uwa sai Allah,saidai babu yadda muka iya,bayan tafiyarki mukhtar yazo ya karbi yaronsa...." A firgice ta dago ta dubeshi muryarta na rawa idanunta na fidda ruwan hawaye
"Amma malam me yasa zaimin haka,rabamu ken......."kaaa qarasawa tayi tayi qas da kanta
" kiyi haquri sumayya,shi ya fiki a haqqu da shi,sannan ya riga da yace baiso yaron yayi zaman a golanci gidan wani kamar yadda shima yayi,kiyu haquri nasan ba wai ya rabaku bane na har abada saboda yadda yazo mana bada nuna isa ko qarfa qarfa bane,abinda na lura shine bazai iya jurar rashin ganin yaron bane,tunda idan har kika tafi da shi bashi yiwuwa ya dinga binki gidan mijinki da sunan yazk ganin dansa,kiyi haquri babu komai ai kuna tare,na tabbata za'a dinga kai miki shi"malam ya fada cikin tausasawa. Haka malam din ya dinga lallashinta yana bata kalamai har ta samu ta danji sauqin zugin zuciyarta,saidai abinda take ji na game da kewar yaron har yau bai sauya ba.

Data koma daki taga sauran kayayyakinsa kasa ci gaba da daurewar tayi,ba shakka raba da da uwa ba qaramin abu bane,shi yasa aka ce ko mutuwa tana shakkar idon uwa,yaya wadanda suka rabu da 'ya'yayensu suke ji rabuwa ta har abada?,ashe da sauqi ita tunda yana nan cikin duniyarta kusa da ita amma duk da haka ta gaza daurewa,kuka tayi mai yawan gaske wanda shi ya haifar mata da zazzabin da ciwon kai mai tsanani har ranar da aka daura auren,haka nan aka tattarata aka kaita dakinta tana mai ci gaba da kuka mai qunshe da abubuwa iri daban daban

**** *9:30 pm* *****

Lukman Bashir shine asalin sunansa,haifaffen garin kano cikin qaramar hukumar kano municipal,yayi karatunsa iya N.C.E sai ya fada kasuwanci gadan gadan,mahaifiyarsa hajiya kubra shi kadai tallin tal ta haifa,hakan ya sanya ta dauki so da qauna da kulawa ta dora masa,wannan shine dalilin da ya sanya duk lokacin da yayi aure ta fuskanci yana mutuwar son matar take rabasu don wai ba zata bari a mallake mata yaro ba tana kallo,kasancewar gidansu daya part guda yayi mata da ya tashi ginin gidansa,a haka a haka ta sanya lukman ya rabu da mata kusan hudu kenan duk da cewa yana dacen matan aure masu matuqar haquri da biyayya saidai ita sam bata gani,haquri da biyayyar da sukewa lukman din ita ke jawo musu qauna gunsa,amma ita gani taje tsabar asiri ne matan suke yi,sam matan basu da sukuni,hatta zanin daurawa idan zai musu ita ke karbar kudin ta siyo ta bada adinka musu ita kuwa sai wanda ta zaba zata sanya,hakanan duk cikin matan da yake aurowa mutum daya ce ta haihu da shi don na wani dadewa take bari suyi ba,ita din ma a gidansu ta haife sai da ta yaye hajiyan tasa aka karbota,'ya mace ta haifa wadda ake kira da nuwaira.

Hausawa suka ce alhaki kwikuyo ne,a irin haka ne Allah ya hada lukman da KARIMA gogaggiya mai idanu a tsakiyar kaa wadda ita ta haifa masa yara uku dukka mata zaitun marwa da radiya,da fari kariman lumbu lumbu ta yiwa hajiyan har ta saki jiki da ita,sannan daga bisani ta sanya gaba daya daga lukman din har hajiyan aka sanya su qarqashin ikonta,daga lukman din har hajiyan umarni suke karba daga wajenta,babu wanda ya isa ya tsallake abinda ta shimfida masa,sai a bayan idonta su yita takaici da jimami amma a gaban idonta ko tari ba wanda ya isa yayi,mutane da yawa sunyi murna sunyi shewa da wannan sauyi domin ya zamewa hajiya kubra izina.
Chapter 56 · 0% Book details