Sashe 193
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tun daga lokacin matuqar tana kitchen din zata mata iya gyaran da ya dace,bata damu da duk abinda zata fada ba,tana yine kawai saboda almustaphan,tun tana masifa har ta dawo saidai harara,sau tari dariya take baiwa sumayyan,saboda ta lura da cewa tsabar girman kai ne kawai ke dawainiya da su'ad din,wani lokaci qunshe dariyarta take kawai idan tana girki,abin sai wanda ya gani,taka hau yanar gizo ne ta dubo yadda ake yi,wani abun bai ciyuwa hatta gurin wanda ya takura din sai ta dinga yi,idan har ya ciyu to ranan sumayya na kusa ta sanya hannu,cikin qanqanin lokaci su'ad din ta fara gane shayi ruwa ne,tayi roqon tayi magiyar ya samo mata mai aiki yayi funfurus da ita,har kukan takaici da wuya duka sai da tayi ,ya share tamakar baisan tana yi ba,don wannan ce kadai hanyar da zai hora ta kan iskancin da take ji saman kanta,har sumayya a wani dare take roqarshi ua samo matan wadda zata kama mata,saboda tana ganin yadda ake gwagwagwa wajen dafa shayi ma kawai,har yau ta kasa dauke yadda ake,ita dinma shiru ya nata kaman baiji me tace ba,ganin hakan ya sanya taja bakinta ta tsuke,tasan tunda yayi hakan baison zancen ne,sai da ya tabbatar ta dahu sannan ya samo wadda zata dinga taimaka mata,da sharadin tare zasu dinga yi tana ganin yadda akeyi.
Abu na gaba daya soma jan hankalinta shine yadda ta fuskanci maan din na nuna tsantsar kulawa da riritawa ga cikin dake jikin sumayyan,da fari ta dauki abun duka wasa,sannu sannu ta soma fahimtar soyayyar da bata taba gani yana yiwa wani abu ba ita yake gwadawa abinda ke cikin dako duniya bai iso ba,bata tabbatar da haka ba sai a wani yammaci wanda ranar sumayya zata karbi girki.
Tun da yamma tana zaune babban falonsu,bata faye zama cikinsa ba sai jifa jifa amma yau ta kasa ta tsare,sam sumayyan bata damu da zamanta ba,sabgoginta take hankali kwance,zuwa qarfe biyar ta gama shirya masa dining tsaf da kalar abincin da yace yana so,bayan itama ta hada wanda ranta ke so,shinkafa ta dafa ta zuba wake a kai ta bare kifin gwangwani a kai,sannan ta soya manja ta yanka salad tumatir albasa da cocumber,tana da yajinta tun daga gida wanda kusan shi ya tada mata kwadayin cin fara da man ma,salad dinne kawai bata gyara ba don haka ta barshi ta shiga wanka,ta shirya tsaf cikin wani wando ya lafe a jikinta kamar a jikin nata aka dinka shi,da kadan ya zarta gwiwa,wandon baqi ne hakan ya sanya ta saka shirt fara,ta gyara gashinta ta daureshi da baqin ribbom ya sauka har saman kafadunta,fashion tayi amfani da su baqaqe masu adon farin stone ajiki,lite make up ce a fuskarta wadda tasan tafi burge almustaphan,feshe jikinta tayi da turare sannan ta laluba cikin kayanta ta zaro abaya,har ta zura sai kuma ta cire,sam yau sai taji bata sha'awar saka ta,bata bari su'ad ra ganta cikin irin wannan shigar,yawanci tafi zama haka sanda suke falonshi ko nata falon su biyu,wasu slippers masu kyau baqaqe da suka bayyana kyan farar qafarta ta zura sannan ta tako a hankali ta fito.
Qarar bude qofar falon nata da rufewa ita ta soma jan hankalin su'ad din,idanu ta zuba mata baki daya,sannu a hankali wani kishi ya soma sokarta na ganin yadda sumayyan tayi kyau kamar 'yar tsana,kai kace drowing ne na girly,cikin da take tsammani zai batata sai gashi ya zame wani ado a jikinta,ya shiga wata na biyar ya zauna daras a jikinta abin sha'awa,ko daya bai tafi da hips da boobs da take da su ba saima qara fito da su da yayi,karon farko data soma ganinta cikin yanayin shigar,a hankali ta janye idanunta daga kanta kishi na nuqurqusarta,da ciki ma kenan ina ga tana ita kadai?,ta yiwa kanta wannan tambayar,da qyar ta iya hadiye yawu ta maida idanunta kan t.v taci gaba da kallo ba don tana fahimta ba,itakam dukkan abin nan da take batasan tana yi ba,kanta tsaye ta shige kitchen tana daga tsaye ta soma gyaran salad dinta.
Tunda ya shigo baki daya tayi gaba da dukkanin imaninsa,ruwa ya shigo sha amma baki daya ya nemi qishirwar ya rasa,sai kawai ya harde hannunshi a qirji ya jingina da qofa yana kallonta,baiso ma tasan ya shigo bare ya ta daina kaikawonta,ilahirin jikinta yake bi da kallo,wani sanyi da farinciki na saukar masa,godiya yakewa Allah cikin zuciyarsa,ba shakka duk yadda yaso ga son dai daita matsayinta cikin zuciyarshi da sauran mata yasan yayiwa kanshi qarya,abune ba mai yiwuwa ba,koda ciwon makanta da ciwon bacewar tunani zai kamashi yana da tabbacin zai iya gane randa yake ranar girkinta,tun daga harabar gidan da yake iya ajje motarsa kama da duk wani lungu da saqo na gidan sauyawa yake,ba'a magana qamshi tsafta da sauransu,sai yake jin kamar harda iskar gidan ma sauyata ake,babu mamaki ko don tsananin soyayyarta da kullum kwanan duniya ake linka masa ne?.
Sai data gama yankawa ta isa gaban famfo ta tara shi cikin ruwa,da hanzari taji an jawota,ko da daga bacci ta tashi tasan waye,mannata yayi da jikinsa ya zagaye hannayensa saman cikinta,sannan ya dora kanshi kan kafadarta
"Barka da dawowa....barka da dawowa sanyin idaniya hasken cikin gidansa....tun dazu naji yanayin gidan ya sauya ashe yariman maza ne ya iso" baisan sanda ta juyi da ita suna fuskantar juna ba,idanunta cikin nashi tana masa wani irin kallo,shi dinma kallon yake jifarta da shi,ya gaza cewa komai,ko yaushe furucinta na musamman ne a gurinsa,duk abinda zata furta ya isa kunnenshi mai dadi ne,mai laushi ne,mai taushi ne mau faranta zuciya tare da zare mata gajiya da baqinciki,kasa cewa komai yayi sai kallon kallo tsakaninsu tare da jifan juna da murmushi,bakinsu kawai ya hade waje daya yana aijata mata da wasu kisses masu zafin gaske,ganin yana neman wuce gona da iri a muhallin da bai dace ba ya sanyata tureshi suna maida numfashi,ya matsa din amma bai bar jikinta ba,dubanta yake da rikitattun idanunshi da suka sauya lokaci daya,cike da shauqi yake dubantan nata
"A kitchen muke fa" ta fada a shagwabe,hancinta ya kama ya dan jaa
"To waye ya jawo?,irin wannan shigar ko gaban wa na ganki hakan na iya faruwa" ya fada da qyar cikin muryarshi dara fara jirkicewa
"Bamu gaisa da baby ba" murmushi ta saki
"Wannan baby......wanne irin qauna ne haka my maan" kada kai kawai yayi yana murmushi,qugunta ya riqo baki daya da hannayenshi
"Qauna?,indai wannan ce qauna to kam bakiga komai ba,babu abinda kika gani babe....banajin zan iya bayyana qaunar da nake mishi ko mata,daga cikin dalilan da ya sanya kenan ban damu da duba me zaki haifa min ba,ko me kika haifamin ina so ina maraba da shi,gudan jin muhammad almustapha ne da summyn malam" murmushi ta saki sosai saboda sunan da ya kirata da shi har fararen haqoranta na bayyana,dubanta yake shima yana murmushi wani farinciki na shigarshi,da kanta ta yaye masa t.shirt din dake jikinta zuwa saman cikinta,ya durqusa a hankali hannunshi saman cikin.
wani wawan tsaki mai shiga kunnuwa suka ji anja,su'ad ce wadda tun shigowarshi cikin kitchen din ta kasa samun nutsuwa,baki dayan hankalinta ya karkata kitchen ne,ta kasa zama har sai data biyo bayansu,kusan duk rabin maganar tasu cikin kunne da idanunta suja yisu,wanda sam basu san da shigowar tata ba banda yanzun,ko kusa ko alama bata taba sanin cewa haka almustaphan ke qaunar haihuwa ba,tayi tsammanin cewa ra'ayinsu daya a qidarsu daya,saboda ganin ko alama bai taba mata magana kan rashin samun juna biyunta ba,abinda bata sani ba shine yana sawa rashi lokaci ne,idan yayi zata haifa masa,bugu da qari yana tausayim macen da bata haihu ba,hakan ya sanya yake ganin girma da qimar ni'imah har gobe
"Amma dai wannan abun bai dace ba ko?" Ta fada zuciyarta kamar zata fadi qasa,waiwayowa yayi yana dubanta
"Shigowa kai tsaye ba tare da yin sallama bane bai dace ba ko ko meye?" Kasa cewa komai tayi don tasan ita ta kawo kanta,ta sani cewa duk ranan girkinta hatta da zurga zurga sumayyan bata fiya ba,data gama uzurorinta ta masa sallama shikenan sai da safe,mazewa ta sake yi kishi na cinta
"Kitchen wajen kowa ne,na shigo daukar abu sai na fasa saboda ku?"
"Yaushe kika fara labe?,kina tsammamin banga shigowarki ba?,kina tsaye tsohon minti goma?" Mamaki ya cikata,bata yi zaton ya ganta ba,da shigowa daukan abu tayi niyyar fakewa tayi boren qarya,da idanu ya tsatstsareta yana hukuntata da kallonshi,wanda ta san fassarar hakan sarai,duk sai ta daburce,numfasawa yayi ya dauke kanshi daga gareta fuskanshi daure ya maida ga sumayya data soma wanke salad dinta
"Muje ki shiryan ruwa nayi wanka"amsa masa tayi da to,ta rufe salad dinta ta ajjiye gefe sannan ta ratsa ta fice,sai data fice daga kitchen din sannan ya maida kallonsa ga su'ad dake tsaye tana cije baki cikin takaici,a hankali ya tako zuwa gabanta,daf da ita ya tsaya tazarar dake tsakaninsu bata da yawa
"Me yasa ko yaushe baki daukan gyara?,baki gyaran kuskurenki cikin sauqi?,Kada kiyi abinda zai siya miki raini,ki guji yin abinda bai dace ba,abinda duk kikasan ba'a yi miki ki nisanci yiwa wani,umarni na baki ba shawara ba" baya ya danja sannan ya juya shima ya fice,yafi kowa sanin halinta,tafi gane tsauri,daukar sauqi take tamkar wata isa ce tata tasa ake mata hakan.
Abu na gaba daya soma jan hankalinta shine yadda ta fuskanci maan din na nuna tsantsar kulawa da riritawa ga cikin dake jikin sumayyan,da fari ta dauki abun duka wasa,sannu sannu ta soma fahimtar soyayyar da bata taba gani yana yiwa wani abu ba ita yake gwadawa abinda ke cikin dako duniya bai iso ba,bata tabbatar da haka ba sai a wani yammaci wanda ranar sumayya zata karbi girki.
Tun da yamma tana zaune babban falonsu,bata faye zama cikinsa ba sai jifa jifa amma yau ta kasa ta tsare,sam sumayyan bata damu da zamanta ba,sabgoginta take hankali kwance,zuwa qarfe biyar ta gama shirya masa dining tsaf da kalar abincin da yace yana so,bayan itama ta hada wanda ranta ke so,shinkafa ta dafa ta zuba wake a kai ta bare kifin gwangwani a kai,sannan ta soya manja ta yanka salad tumatir albasa da cocumber,tana da yajinta tun daga gida wanda kusan shi ya tada mata kwadayin cin fara da man ma,salad dinne kawai bata gyara ba don haka ta barshi ta shiga wanka,ta shirya tsaf cikin wani wando ya lafe a jikinta kamar a jikin nata aka dinka shi,da kadan ya zarta gwiwa,wandon baqi ne hakan ya sanya ta saka shirt fara,ta gyara gashinta ta daureshi da baqin ribbom ya sauka har saman kafadunta,fashion tayi amfani da su baqaqe masu adon farin stone ajiki,lite make up ce a fuskarta wadda tasan tafi burge almustaphan,feshe jikinta tayi da turare sannan ta laluba cikin kayanta ta zaro abaya,har ta zura sai kuma ta cire,sam yau sai taji bata sha'awar saka ta,bata bari su'ad ra ganta cikin irin wannan shigar,yawanci tafi zama haka sanda suke falonshi ko nata falon su biyu,wasu slippers masu kyau baqaqe da suka bayyana kyan farar qafarta ta zura sannan ta tako a hankali ta fito.
Qarar bude qofar falon nata da rufewa ita ta soma jan hankalin su'ad din,idanu ta zuba mata baki daya,sannu a hankali wani kishi ya soma sokarta na ganin yadda sumayyan tayi kyau kamar 'yar tsana,kai kace drowing ne na girly,cikin da take tsammani zai batata sai gashi ya zame wani ado a jikinta,ya shiga wata na biyar ya zauna daras a jikinta abin sha'awa,ko daya bai tafi da hips da boobs da take da su ba saima qara fito da su da yayi,karon farko data soma ganinta cikin yanayin shigar,a hankali ta janye idanunta daga kanta kishi na nuqurqusarta,da ciki ma kenan ina ga tana ita kadai?,ta yiwa kanta wannan tambayar,da qyar ta iya hadiye yawu ta maida idanunta kan t.v taci gaba da kallo ba don tana fahimta ba,itakam dukkan abin nan da take batasan tana yi ba,kanta tsaye ta shige kitchen tana daga tsaye ta soma gyaran salad dinta.
Tunda ya shigo baki daya tayi gaba da dukkanin imaninsa,ruwa ya shigo sha amma baki daya ya nemi qishirwar ya rasa,sai kawai ya harde hannunshi a qirji ya jingina da qofa yana kallonta,baiso ma tasan ya shigo bare ya ta daina kaikawonta,ilahirin jikinta yake bi da kallo,wani sanyi da farinciki na saukar masa,godiya yakewa Allah cikin zuciyarsa,ba shakka duk yadda yaso ga son dai daita matsayinta cikin zuciyarshi da sauran mata yasan yayiwa kanshi qarya,abune ba mai yiwuwa ba,koda ciwon makanta da ciwon bacewar tunani zai kamashi yana da tabbacin zai iya gane randa yake ranar girkinta,tun daga harabar gidan da yake iya ajje motarsa kama da duk wani lungu da saqo na gidan sauyawa yake,ba'a magana qamshi tsafta da sauransu,sai yake jin kamar harda iskar gidan ma sauyata ake,babu mamaki ko don tsananin soyayyarta da kullum kwanan duniya ake linka masa ne?.
Sai data gama yankawa ta isa gaban famfo ta tara shi cikin ruwa,da hanzari taji an jawota,ko da daga bacci ta tashi tasan waye,mannata yayi da jikinsa ya zagaye hannayensa saman cikinta,sannan ya dora kanshi kan kafadarta
"Barka da dawowa....barka da dawowa sanyin idaniya hasken cikin gidansa....tun dazu naji yanayin gidan ya sauya ashe yariman maza ne ya iso" baisan sanda ta juyi da ita suna fuskantar juna ba,idanunta cikin nashi tana masa wani irin kallo,shi dinma kallon yake jifarta da shi,ya gaza cewa komai,ko yaushe furucinta na musamman ne a gurinsa,duk abinda zata furta ya isa kunnenshi mai dadi ne,mai laushi ne,mai taushi ne mau faranta zuciya tare da zare mata gajiya da baqinciki,kasa cewa komai yayi sai kallon kallo tsakaninsu tare da jifan juna da murmushi,bakinsu kawai ya hade waje daya yana aijata mata da wasu kisses masu zafin gaske,ganin yana neman wuce gona da iri a muhallin da bai dace ba ya sanyata tureshi suna maida numfashi,ya matsa din amma bai bar jikinta ba,dubanta yake da rikitattun idanunshi da suka sauya lokaci daya,cike da shauqi yake dubantan nata
"A kitchen muke fa" ta fada a shagwabe,hancinta ya kama ya dan jaa
"To waye ya jawo?,irin wannan shigar ko gaban wa na ganki hakan na iya faruwa" ya fada da qyar cikin muryarshi dara fara jirkicewa
"Bamu gaisa da baby ba" murmushi ta saki
"Wannan baby......wanne irin qauna ne haka my maan" kada kai kawai yayi yana murmushi,qugunta ya riqo baki daya da hannayenshi
"Qauna?,indai wannan ce qauna to kam bakiga komai ba,babu abinda kika gani babe....banajin zan iya bayyana qaunar da nake mishi ko mata,daga cikin dalilan da ya sanya kenan ban damu da duba me zaki haifa min ba,ko me kika haifamin ina so ina maraba da shi,gudan jin muhammad almustapha ne da summyn malam" murmushi ta saki sosai saboda sunan da ya kirata da shi har fararen haqoranta na bayyana,dubanta yake shima yana murmushi wani farinciki na shigarshi,da kanta ta yaye masa t.shirt din dake jikinta zuwa saman cikinta,ya durqusa a hankali hannunshi saman cikin.
wani wawan tsaki mai shiga kunnuwa suka ji anja,su'ad ce wadda tun shigowarshi cikin kitchen din ta kasa samun nutsuwa,baki dayan hankalinta ya karkata kitchen ne,ta kasa zama har sai data biyo bayansu,kusan duk rabin maganar tasu cikin kunne da idanunta suja yisu,wanda sam basu san da shigowar tata ba banda yanzun,ko kusa ko alama bata taba sanin cewa haka almustaphan ke qaunar haihuwa ba,tayi tsammanin cewa ra'ayinsu daya a qidarsu daya,saboda ganin ko alama bai taba mata magana kan rashin samun juna biyunta ba,abinda bata sani ba shine yana sawa rashi lokaci ne,idan yayi zata haifa masa,bugu da qari yana tausayim macen da bata haihu ba,hakan ya sanya yake ganin girma da qimar ni'imah har gobe
"Amma dai wannan abun bai dace ba ko?" Ta fada zuciyarta kamar zata fadi qasa,waiwayowa yayi yana dubanta
"Shigowa kai tsaye ba tare da yin sallama bane bai dace ba ko ko meye?" Kasa cewa komai tayi don tasan ita ta kawo kanta,ta sani cewa duk ranan girkinta hatta da zurga zurga sumayyan bata fiya ba,data gama uzurorinta ta masa sallama shikenan sai da safe,mazewa ta sake yi kishi na cinta
"Kitchen wajen kowa ne,na shigo daukar abu sai na fasa saboda ku?"
"Yaushe kika fara labe?,kina tsammamin banga shigowarki ba?,kina tsaye tsohon minti goma?" Mamaki ya cikata,bata yi zaton ya ganta ba,da shigowa daukan abu tayi niyyar fakewa tayi boren qarya,da idanu ya tsatstsareta yana hukuntata da kallonshi,wanda ta san fassarar hakan sarai,duk sai ta daburce,numfasawa yayi ya dauke kanshi daga gareta fuskanshi daure ya maida ga sumayya data soma wanke salad dinta
"Muje ki shiryan ruwa nayi wanka"amsa masa tayi da to,ta rufe salad dinta ta ajjiye gefe sannan ta ratsa ta fice,sai data fice daga kitchen din sannan ya maida kallonsa ga su'ad dake tsaye tana cije baki cikin takaici,a hankali ya tako zuwa gabanta,daf da ita ya tsaya tazarar dake tsakaninsu bata da yawa
"Me yasa ko yaushe baki daukan gyara?,baki gyaran kuskurenki cikin sauqi?,Kada kiyi abinda zai siya miki raini,ki guji yin abinda bai dace ba,abinda duk kikasan ba'a yi miki ki nisanci yiwa wani,umarni na baki ba shawara ba" baya ya danja sannan ya juya shima ya fice,yafi kowa sanin halinta,tafi gane tsauri,daukar sauqi take tamkar wata isa ce tata tasa ake mata hakan.