Sashe 37
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Qarfe biyar a qofar gidan tayi masa,yana sanye da wani yadi mai qarancin kauri ruwan bula mai haske wanda aka yiwa aiki da ruwan bula mai turuwa,duk da sauyawar yanayinsa da rama amma hakan bai hanashi kyau ba,sam rayuwar gidan bata masa dadi saboda a yanzun shikewa kansa komai,hakan ya sanya ya nemi wani saurayi wanda ke zuwa ya masa share share.
Halima ce ta soma ganinsa,ta yiwa mamansu magana aka bashi izini ya shiga,duk da yaran yanzun basa sakewa da shi kamar da,hakan baya masa dadi sam don baiga abinda su ya shiga tsakaninsu ba.
Cikin girmamawa ya gaida maman ta tambayeshi su yahanasun ya amsa mata duk lafiya qalau shi kuma ya tambayi masu jiki(wato sumayya),ba wata hira dama tun da can ke shiga tsakaninsu ba daya wuce gaisuwar,hakan ne ya sanyashi ya miqe bayan an gama shigo da kayan ya musu sallama ya fice.
Sai ya kasa tafiya ya tsaya a soron,yana da muradin ganin cikinsa gashi ko gilmawarta bai gani ba bare yaji muryarta,hakan babu wanda ya masa zancanta,jingina yayi da bangon soron hannunsa harde a qirjinsa yana tunanin ta yadda zai ganta din,cikin ikon Allah sai ga zainab ta fito tana sanya hijabinta zata shagon kusa da gidansu ta karbo klien zata wanke kwanukan da suka kammala abincin dare da su
"Yauwa zainab,don Allah taimaka min ki fito min da yayarki mu gaisa" ya fada yana gyara tsaiwarsa,mamaki ya cikata,kamar tace wani abun kuma sai ta fasa ta juya ta koma ciki.
A dakin sumayyan ta tarad da maman tsaye kanta tana mata fadan rashin fitowa su gaisa da mukhtar,tundanko banza dai ai uban d'anta ne,abinda ya faru kuma babu wanda ya ruga ya gogeshi cikin KUNDIN QADARARTA,hawaye ta soma gogewa abinda maman bata so kenan
"Amma mama meye amfanin fitar tawa mu gaisa,tunda dai lafiya qalau nake"
"Na san da wannan,ko banza ai ko baya ta taki zai so ya tabbatar da lafiyar abinda ke cikinki ko" maman ta fadi
"Shikenan kiyi haquri mama zan dinga gasheshi" tausayinta ya kamata,tana shirin yin magana zainab din ta shigo ta fada mata abinda mukhtar din ya buqata
"Kin gani ai,sai kije ku gaisa" ta fada ta juya tana ficewa,hajibinta ta janyi dake rataye jikin sif ta zura sannan tayo waje.
Tunda ta fito ya zuba mata ido yake kallonta,sosai wannan karon cikin ya fito fiye da waccan karon,hatta tafiyarta ta soma sauyawa,kanta ma qasa din bata son hada ido da shi har ta qaraso,daga can gefe guda ta tsaya sannan tace
"Ina yini" ba tare data daga kai ta dubeshi ba
"Lafiya lau,ya jikin naki"
"Alhamdulillah" ta fada cikin sanyi,sai shiru ya biyo baya kowa da abinda ke saqawa cikin zuciyarsa,tsaiwar ta fara mata tsauri har ya lura da haka,sai ya waiwaya ya gangaro mata wani dutse da suke tokare qofa da shi ya furta
"Ga guri zauna" bata musa ba ta zauna din don tana da buqatar hakan
"Me yasa sumayya?,why?,kinga ayanzun kin zama silar da zamu raini yaronmu a mabanbanta gurare abinda ko a mafarki ban taba hasashen faruwarsa ba"ya furta wani daci na zagaya harshensa,idanuwansa na sauya launi,da sauri ta daga kai ta watsa masa fararen idanuwanta,take wani bacin rai ya soma bijiro mata,wato har yanzun zarginta yake kenan?,dama abinda yake son gaya mata kenan da har ya fiddo ta tana zaman zamanta tana lallaba rayuwarta.
Qin tankawa tayi sai ma yunqurin miqewa da ta soma yi saboda bata ga alfanun ci gaba da tsaiwa a gabansa ba,ganin tana niyyar wucewa ba tare da ya gaya mata abinda zaya fadi ba yace
" idan nayi lissafi dai dai cikin ya kusa shiga wata na tara,zuwa yanzu ya kamata ace anyi siyayya,ki rubuta duk abinda kike da buqata jibi zan dawo na karba in sha Allah"
"Ka kawo duk abinda kake ganin zaka iya" ta fada tana mai shigewa gidan ba tare da ko ta waiwayoshi ba zuciyarta na suya,idanunta na zafi.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
3⃣5⃣
_______________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wallazi yumutuni summa yuhyi,wallazi adma'u ay yagfirali khadi aty yau maddin*
______________________________
A makare ya tashi yau wanda hakan ya sabba ba masa yin sallar asubahi cikin gida,tunda ya idar da sallar yake zaune saman daddumar bai tashi ba kamar yadda bai aiwatar da komai ba,tunanin sumayya ne fal zuciyarsa yau ya wayi gari da shi,hakanan yake jin wunin yau ba zai iya qarewa ba ba tare da yaje ya ganta da lafiyar abinda ke cikinta ba,kusan tunda ta shiga watan haihuwarta da ita yaje kwana yake tashi.
Qarar wayarsa ce ta katse masa hanzari,ya juya bangaren da take ya jawota ya duba,baquwar lamba ce,ya latsa sannan ya kara a kunnensa,runtse idanunsa yayi zuciyarsa ta soma quna saboda muryar wadda yaji,bai taba jin ya tsani wani abu tsana mai tsanani ba irin na mamallakiyar muryar,zainab ce take magana cikin maqale murya da wani irin salo nason tafiyar da hankali,tun a daren jiya bokanta wanda take kira da malam ya bata wannan sa'ar ya kuma tabbatar mata bayan sallar asubahi ne zata sameshi,sanda ya daga wayar zuciyarta sai ta cika da farincikin samun nasara,don dama ya sanar mata bayan sallar asubar a gobe bazai koma bacci ba,jin tana ta magana ya mata shiru ya sanya ta fashewa da wani makirin kuka
"Habaa my mukhtar,dama laifin wani kan iya shafar wani?,mene laifina ni a ciki?,duk iya yina nayi don inga abinda ke cikin yarinyar nan ya kubuta,duk tarin hidima dana dinga yi da ita rana daya duk ka mance ka watsar da alkhairi na a gareku ka sakeni,kuma ma tunda an samu cikin na nan ba shikenan ba komai ya wuce sai ka maidani daki na ko?".
Kamar garwashin wuta haka yaji kalaman nata,cikin harzuqa ya dakatar da ita
" ke wacce iriyar jahila ce wai?,shin kin manta zama ni dake a yanzu ya haramta ne sau nawa zan nana ta miki,ke koda kuwa ma zamanmu ya halatta bazan iya zama da kowacce mace ba a yanzu,tunda sumayya da na raina da kaina ta iya min haka babu wata diya mace da ba zata iya aikata min makamancin haka koma fiye da shi ba,saboda haka gargadina dake na qarshe,kada ki sake gigin kiran layi na ko tarar hanyar da kika san zan bi,idan kuma kinqi ji ba zaki qi gani ba"daga haka ya katse kiran ya ajjiye wayar a fusace.
Daga daya bangaren nata itama ajjiye wayar tayi tana huci sannan ta dubi qawar tata
"Wannan wanne irin mutum ne haka?,duk zama da wuyar da muka sha wajen malam ta tashi kenan a banza,kinji maganganun banzan da yake gaya min?,to wallahi wannan karon babban aikin zan saka a masa koda duniya zata zageni,ko zanyi yawo babu zanin daurawa" kafada ta daga tana fadin
"Au ho sai yanzu kika gane kenan?,tuntuni ai malam din ya gaya miki ki saki naira kiga aikin da ko uwarsa dake kabari ba zai ganta a gabansa ba sai ke" miqewa tayi ta fice daga dakin fuuu tana fadin
"Ai anzo gurin kuma".
A hasale ya kuma waiwayowa ga wayar tasa jin ta sake tsuwwa a karo na biyu yana zaton ita din ce ta sake kiransa,sai jikinsa yayi sanyi gabansa ya fara faduwa ganin sunan abubakar kan screen din,cikin sanyi da sallama ya amsa wayar,lumshe idanuwa yayi wata rahama na sauka cikin zuciyarsa lokacin da abubakar ke furta masa albishir mafi dadi da ya taba sauraro tsawon rayuwarsa,sumayya ta haihu ta haifa masa yaro,baisan adadin lokacin da ya dauka ba cikin duniyar madaukakin farinciki shidai ya farka yaga har kiran na abubakar ya katse.
Faduwa yayi saman a bin sallar yayi sujudush shukur yana mai tasbihi ga ubangiji,bai wani jinkiri ba ya miqe ya fada makewayi ya shiga wanka,cikin mintina talatin ya fito,kai tsaye gaban sif dinsa ya isa bayan ya tsane jikinsa,ya bude yana kallon kayan,a sanyaye ya sauke hannayensa yana duban kayan kala bakwai da suke sababbi dukkansu,ba zai manta randa ya bada dinkinsu ba,tun cikin sumayya na da wata uku a lokacin tana gidan,musamman ya tanadesu ya dinkasu saboda ya sanyasu tun daga rana ta farko da aka haifa masa yaronsa har ranar suna,baya iya manta lokacin da take dariya tana tsokanarsa da cewa gandoki,sai ya koma bakin gadon ya zauna yana yarfa hannu,yana jin yadda bacin rai ke taso masa yana son danne farincikin da yake ciki,baisan mai yasa har yau zuciyarsa ta kasa daina jin ciwon abinda tayi masa ba duk da cewa an cimma nasarar tsallakewar cikin gashi har yau Allah ya nufa ya iso duniya.
Da qyar ya samu ya hadiye wani dunqulen abu mai daci sannan ya miqe ya shirya cikin wani yadi mai kyau na maza fari sol wanda ya masa kyau sosai,ko abinda zai sawa cikinsa bai nema ba ya fito don dama ba ko yaushe yake samun damar karyawar safe ba,yana shirin tada motarsa ya kira ya yahansu ya shaida mata,hamdala ta dinga yi matiqa da gaske tana jin dadi a zuciyarta,ta kuma shaida masa lalle ya biyo gidan nata kafin ya wuce.
Kafin sha daya na safe tuni gidan ya cika da jama'a 'yan uwa da abokan arzuqi,kowa barka yake mata tare da tayata farincikin wannan rana da aka jima ana saka ran zuwanta,sam ita bata san me ake ba ma,bacci take sosai ita daya a dakinsu,yaron shima nashi baccin yake,sai da ya farka ya fara kuka alamar yunwa sannan mama ta baro dakinta wanda suke zaune da mutane ta shigo dakin ta tasheta,sai data sake hada mata shayi mai kauri ta sake sha sannan ta dora mata shi saman cinyarta ta fara koya mata yadda zata shayar da shi,runtse tayi sannan ta fara qorafin zafi maman tace
"A haka zaki daure har ki saba".
Halima ce ta soma ganinsa,ta yiwa mamansu magana aka bashi izini ya shiga,duk da yaran yanzun basa sakewa da shi kamar da,hakan baya masa dadi sam don baiga abinda su ya shiga tsakaninsu ba.
Cikin girmamawa ya gaida maman ta tambayeshi su yahanasun ya amsa mata duk lafiya qalau shi kuma ya tambayi masu jiki(wato sumayya),ba wata hira dama tun da can ke shiga tsakaninsu ba daya wuce gaisuwar,hakan ne ya sanyashi ya miqe bayan an gama shigo da kayan ya musu sallama ya fice.
Sai ya kasa tafiya ya tsaya a soron,yana da muradin ganin cikinsa gashi ko gilmawarta bai gani ba bare yaji muryarta,hakan babu wanda ya masa zancanta,jingina yayi da bangon soron hannunsa harde a qirjinsa yana tunanin ta yadda zai ganta din,cikin ikon Allah sai ga zainab ta fito tana sanya hijabinta zata shagon kusa da gidansu ta karbo klien zata wanke kwanukan da suka kammala abincin dare da su
"Yauwa zainab,don Allah taimaka min ki fito min da yayarki mu gaisa" ya fada yana gyara tsaiwarsa,mamaki ya cikata,kamar tace wani abun kuma sai ta fasa ta juya ta koma ciki.
A dakin sumayyan ta tarad da maman tsaye kanta tana mata fadan rashin fitowa su gaisa da mukhtar,tundanko banza dai ai uban d'anta ne,abinda ya faru kuma babu wanda ya ruga ya gogeshi cikin KUNDIN QADARARTA,hawaye ta soma gogewa abinda maman bata so kenan
"Amma mama meye amfanin fitar tawa mu gaisa,tunda dai lafiya qalau nake"
"Na san da wannan,ko banza ai ko baya ta taki zai so ya tabbatar da lafiyar abinda ke cikinki ko" maman ta fadi
"Shikenan kiyi haquri mama zan dinga gasheshi" tausayinta ya kamata,tana shirin yin magana zainab din ta shigo ta fada mata abinda mukhtar din ya buqata
"Kin gani ai,sai kije ku gaisa" ta fada ta juya tana ficewa,hajibinta ta janyi dake rataye jikin sif ta zura sannan tayo waje.
Tunda ta fito ya zuba mata ido yake kallonta,sosai wannan karon cikin ya fito fiye da waccan karon,hatta tafiyarta ta soma sauyawa,kanta ma qasa din bata son hada ido da shi har ta qaraso,daga can gefe guda ta tsaya sannan tace
"Ina yini" ba tare data daga kai ta dubeshi ba
"Lafiya lau,ya jikin naki"
"Alhamdulillah" ta fada cikin sanyi,sai shiru ya biyo baya kowa da abinda ke saqawa cikin zuciyarsa,tsaiwar ta fara mata tsauri har ya lura da haka,sai ya waiwaya ya gangaro mata wani dutse da suke tokare qofa da shi ya furta
"Ga guri zauna" bata musa ba ta zauna din don tana da buqatar hakan
"Me yasa sumayya?,why?,kinga ayanzun kin zama silar da zamu raini yaronmu a mabanbanta gurare abinda ko a mafarki ban taba hasashen faruwarsa ba"ya furta wani daci na zagaya harshensa,idanuwansa na sauya launi,da sauri ta daga kai ta watsa masa fararen idanuwanta,take wani bacin rai ya soma bijiro mata,wato har yanzun zarginta yake kenan?,dama abinda yake son gaya mata kenan da har ya fiddo ta tana zaman zamanta tana lallaba rayuwarta.
Qin tankawa tayi sai ma yunqurin miqewa da ta soma yi saboda bata ga alfanun ci gaba da tsaiwa a gabansa ba,ganin tana niyyar wucewa ba tare da ya gaya mata abinda zaya fadi ba yace
" idan nayi lissafi dai dai cikin ya kusa shiga wata na tara,zuwa yanzu ya kamata ace anyi siyayya,ki rubuta duk abinda kike da buqata jibi zan dawo na karba in sha Allah"
"Ka kawo duk abinda kake ganin zaka iya" ta fada tana mai shigewa gidan ba tare da ko ta waiwayoshi ba zuciyarta na suya,idanunta na zafi.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
3⃣5⃣
_______________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wallazi yumutuni summa yuhyi,wallazi adma'u ay yagfirali khadi aty yau maddin*
______________________________
A makare ya tashi yau wanda hakan ya sabba ba masa yin sallar asubahi cikin gida,tunda ya idar da sallar yake zaune saman daddumar bai tashi ba kamar yadda bai aiwatar da komai ba,tunanin sumayya ne fal zuciyarsa yau ya wayi gari da shi,hakanan yake jin wunin yau ba zai iya qarewa ba ba tare da yaje ya ganta da lafiyar abinda ke cikinta ba,kusan tunda ta shiga watan haihuwarta da ita yaje kwana yake tashi.
Qarar wayarsa ce ta katse masa hanzari,ya juya bangaren da take ya jawota ya duba,baquwar lamba ce,ya latsa sannan ya kara a kunnensa,runtse idanunsa yayi zuciyarsa ta soma quna saboda muryar wadda yaji,bai taba jin ya tsani wani abu tsana mai tsanani ba irin na mamallakiyar muryar,zainab ce take magana cikin maqale murya da wani irin salo nason tafiyar da hankali,tun a daren jiya bokanta wanda take kira da malam ya bata wannan sa'ar ya kuma tabbatar mata bayan sallar asubahi ne zata sameshi,sanda ya daga wayar zuciyarta sai ta cika da farincikin samun nasara,don dama ya sanar mata bayan sallar asubar a gobe bazai koma bacci ba,jin tana ta magana ya mata shiru ya sanya ta fashewa da wani makirin kuka
"Habaa my mukhtar,dama laifin wani kan iya shafar wani?,mene laifina ni a ciki?,duk iya yina nayi don inga abinda ke cikin yarinyar nan ya kubuta,duk tarin hidima dana dinga yi da ita rana daya duk ka mance ka watsar da alkhairi na a gareku ka sakeni,kuma ma tunda an samu cikin na nan ba shikenan ba komai ya wuce sai ka maidani daki na ko?".
Kamar garwashin wuta haka yaji kalaman nata,cikin harzuqa ya dakatar da ita
" ke wacce iriyar jahila ce wai?,shin kin manta zama ni dake a yanzu ya haramta ne sau nawa zan nana ta miki,ke koda kuwa ma zamanmu ya halatta bazan iya zama da kowacce mace ba a yanzu,tunda sumayya da na raina da kaina ta iya min haka babu wata diya mace da ba zata iya aikata min makamancin haka koma fiye da shi ba,saboda haka gargadina dake na qarshe,kada ki sake gigin kiran layi na ko tarar hanyar da kika san zan bi,idan kuma kinqi ji ba zaki qi gani ba"daga haka ya katse kiran ya ajjiye wayar a fusace.
Daga daya bangaren nata itama ajjiye wayar tayi tana huci sannan ta dubi qawar tata
"Wannan wanne irin mutum ne haka?,duk zama da wuyar da muka sha wajen malam ta tashi kenan a banza,kinji maganganun banzan da yake gaya min?,to wallahi wannan karon babban aikin zan saka a masa koda duniya zata zageni,ko zanyi yawo babu zanin daurawa" kafada ta daga tana fadin
"Au ho sai yanzu kika gane kenan?,tuntuni ai malam din ya gaya miki ki saki naira kiga aikin da ko uwarsa dake kabari ba zai ganta a gabansa ba sai ke" miqewa tayi ta fice daga dakin fuuu tana fadin
"Ai anzo gurin kuma".
A hasale ya kuma waiwayowa ga wayar tasa jin ta sake tsuwwa a karo na biyu yana zaton ita din ce ta sake kiransa,sai jikinsa yayi sanyi gabansa ya fara faduwa ganin sunan abubakar kan screen din,cikin sanyi da sallama ya amsa wayar,lumshe idanuwa yayi wata rahama na sauka cikin zuciyarsa lokacin da abubakar ke furta masa albishir mafi dadi da ya taba sauraro tsawon rayuwarsa,sumayya ta haihu ta haifa masa yaro,baisan adadin lokacin da ya dauka ba cikin duniyar madaukakin farinciki shidai ya farka yaga har kiran na abubakar ya katse.
Faduwa yayi saman a bin sallar yayi sujudush shukur yana mai tasbihi ga ubangiji,bai wani jinkiri ba ya miqe ya fada makewayi ya shiga wanka,cikin mintina talatin ya fito,kai tsaye gaban sif dinsa ya isa bayan ya tsane jikinsa,ya bude yana kallon kayan,a sanyaye ya sauke hannayensa yana duban kayan kala bakwai da suke sababbi dukkansu,ba zai manta randa ya bada dinkinsu ba,tun cikin sumayya na da wata uku a lokacin tana gidan,musamman ya tanadesu ya dinkasu saboda ya sanyasu tun daga rana ta farko da aka haifa masa yaronsa har ranar suna,baya iya manta lokacin da take dariya tana tsokanarsa da cewa gandoki,sai ya koma bakin gadon ya zauna yana yarfa hannu,yana jin yadda bacin rai ke taso masa yana son danne farincikin da yake ciki,baisan mai yasa har yau zuciyarsa ta kasa daina jin ciwon abinda tayi masa ba duk da cewa an cimma nasarar tsallakewar cikin gashi har yau Allah ya nufa ya iso duniya.
Da qyar ya samu ya hadiye wani dunqulen abu mai daci sannan ya miqe ya shirya cikin wani yadi mai kyau na maza fari sol wanda ya masa kyau sosai,ko abinda zai sawa cikinsa bai nema ba ya fito don dama ba ko yaushe yake samun damar karyawar safe ba,yana shirin tada motarsa ya kira ya yahansu ya shaida mata,hamdala ta dinga yi matiqa da gaske tana jin dadi a zuciyarta,ta kuma shaida masa lalle ya biyo gidan nata kafin ya wuce.
Kafin sha daya na safe tuni gidan ya cika da jama'a 'yan uwa da abokan arzuqi,kowa barka yake mata tare da tayata farincikin wannan rana da aka jima ana saka ran zuwanta,sam ita bata san me ake ba ma,bacci take sosai ita daya a dakinsu,yaron shima nashi baccin yake,sai da ya farka ya fara kuka alamar yunwa sannan mama ta baro dakinta wanda suke zaune da mutane ta shigo dakin ta tasheta,sai data sake hada mata shayi mai kauri ta sake sha sannan ta dora mata shi saman cinyarta ta fara koya mata yadda zata shayar da shi,runtse tayi sannan ta fara qorafin zafi maman tace
"A haka zaki daure har ki saba".