Sashe 58
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kafin su qarasa gun hajiyan sumayya ta dubeta
"Me yasa kinsan kina fitsarin kwance da kika tashi baki sauya kayanki ba nuwaira?,kinsan fa ba'a son mace da qazanta" sai yarinyar ta fara qwalla ta soma sharewa tana cewa
"Wallahi anty tunda bana fitsarin kwance,saddiqa keyi sai a hadamu kwanciya gado daya,idan tayi duk sai ya jiqani,idan ta tashi ita sai nuratu ta sauya mata kaya,ni kuma ba zan canza ba har sai umma ta gama bacci tayi wanka ta fito sannan zata nunan wadanda zan sauya din,koda asuba bana samu nayi sallah sai rana ta fito" ta fada da alamu abun na ci mata tuwo a qwarya,shiru sumayya tayi tausayin yarinyar na kamata,wannan wanne irin zalunci ne,tun kallon farko da ta yiwa yarinyar ya nuna tana jin jiki a gidan,amma tana tunanin kamar ita ce yarinyar nan daya da karima jiya ta gaya mata uwarta daban,don ta tabbatar sai ta tambayeta
"Ina mamarki to?"
"Mama na tayi aure a wani gidan,tun kafin a yayeni aka karboni aka bawa hajiya ni,to da abbanmu ya sake aure ya auro umma sai umman ta karbeni nake gunta"take tsanar karima ta darsu a zuciyar sumayya,lallai ba shakka bayan shirkar tsafi ma harda azabtar da yarinyar da bata ji ba bata gani ba,wai me mutane suka dauki duniya ne?,kowacce mace son kanta ya mata yawa?,burinta ta mallaki miji ta rabashi da kowa nasa?,ta rabashi da 'yan uwansa da tazo ta samesu tare,'yan uwa da suka zamar masa bango marufar asiri tun yana zanin tsumma har kawo yau,ta rabashi da duk wani alkhairi uwa uba ta rabashi da mahaliccinsa,ta sakashi a musibar da ranar gobe qiyama bazai iya tsallaketa ba,ta rabashi da hankalinsa bare ya kula da addininsa,wanda ya cancanci a bashi haqqinsa ta hana ya basu yanzu duka wannan qauna ce?,sai tace sonshi take shi yasa ta aikata haka,wannan ko babban maqiyinka ba shakka iya cutarwar da zai maka kenan,da irin wannan tunani suka isa bangaren hajiyan.
A duqe suka sameta tana share falon nata dake malale da carfet,kallo daya sumayya tayi mata ta fuskanci shekarunta basukai ace tayi tsufar da tayi a yanzu ba,da sallama suka shiga ta dago tana amsa musu riqe da qugunta wanda bisa dukkan alamu ciwo yake mata,nuwaira ce ta gaisheta ta amsa babu yabo ba fallasa yayin da sumayya ta qarasa tana amsar tsintsiyar hannunta tana gaidata,amsawa tayi tana dubanta yayin da sumayya ke qarasa mata sharar har ta kammala sannanbta dawo inda hajiyar ke zaune tana yiwa nuwaira masifar sai zuba zarni take taje bandakinta ta wanke jikinta,mamaki ya cika sumayyar,to ko batasan meke wakana bane cikin gidan?,batasan ba laifin nuwairan bane karima ce ta cancanci fada idan da duka ma ayi mata?,tashi yarinyar tayi ya shige bandakin hajiyar sannan hajiyar ta maido kallonta ga sumayyan
"Ban gane fuskar ba wace ce ne?" Murmushi kawai tayi ta dan sad da kai
"Oho,ko amaryar lukman ce" kai sumayyan ta gyada.
Shiru ne ya biyo baya,hajiyan na dan satar kallon sumayyan,sai taji ta dan sake da yarinyar duk da ba hira suke ba zaman kurame ne,a haka har nuwaira ta fito daga bandakin sanye da jiqaqqun kayanta wadanda ta wanke bayan ta dauraye jikinta ta maida su a haka
"Wani nuwaira nikam bakuyu abin kari bane yau,gashi har sha daya na shirin gotawa yau ba'a kawo kin komai ba,ko luba mai aikin bata zo bane?"cike da madaukakin mamaki sumayya ke sauraron zancan
"Tazo hajiya,bansan ba'a kawo miki ba,don ko nima yau ban karya ba,naga dai su nuratu na karyawa ni ma ba'a bani nawa ba"ta fadi babu alamun damuwa tattare da ita bisa dukkan alamu ta riga da ta saba da hakan,yamutsa fuska hajiyan tayi
"gaskiya na fara jin yunwa wlh,wannan abu Allah kayi mana maganinsa"
"Amma hajiya ai naga kina da sauran kayan abincinki da kika ce bazaki iya ci gaba da girki ba ai abba bai debe su ba ko?"
"To idan banda abinki ina fama da lalura ina zan iya,sharar ma don bazan iya zama cikin qazanta bane nake daburtawa nake yinta" ta fada ta muskutawa da alamu yunwa na sakadarta,tausayinta duka sai ya kama sumayya ta dubeta
"To hajiya idan ba damuwa sai na shiga na girka miki ai ko?"haba ta riqe
" a'a,har kya fara shiga madafi ta sanadina?,ki barshi babu komai idan da sabo ai mun saba da irin wannan gashin,ke dai kawai Allah yayi mana magani"murmushi tayi kawai ta miqe tana tambayar nuwaira inda kitchen din yake.
Sallamar karima a gadarance ita ta maida hankalinsu bakin qofar,ita ke gaba gogan na binta a baya riqe da wani dan qaramin flask wanda bako shakka abun karin hajiyan ne a ciki,idanunsa na kan sumayya yana faman sakar mata murmushi ,wani takaici da haushinsa suka qumeta saita dauke kai tana jin kamar taje ta shaqeshi,haka nan kawai taji jarumin namiji yana burgeta,sai ta tuna sanda zainab ta fara murza kambunta lokacin tana gidan mukhtar,tabbas ko a lokacin mukhtar din kan tauna tsakuwa wani lokaci.
Hajiyan da za'a yiwa sannu a gaisheta ita ke faman yiwa kariman sannu tare da gaisheta,lukman ya koma gefan hajiyan yana gaidata cikin dari dari suke gaisawar kamar suruki da suruka duk don kada su batawa karima rai,baki sumayya ta saki tana kallon abun mamaki bayan hajiya ta bude flask din da aka kawo mata,wani gantalallen soyayyen dankali ne da rabin wainar qwai babu ko tea amma hajiyan sai godiya da sannu take mata
"Saidai yau kici haka hajiya don kafin na fito jikokin naki sun shanye shayin"
"Ai babu komai,idan baka yiwa jikanka ba wa zaka yiwa" ta fada fara'a kamar gonar auduga.
Kallon sumayya karima tayi bayan sumayyan ta gaida lukman wanda ke faman binta da kallo kamar tsohon maye
"Ke baki iya gaida mutane ba" ta fada fuska a tsuke kamar wata uwarta,waigawa sumayyan tayi ta watsa mata kallo
"Su waye mutanen?" Ta tambayeta bayan ta tsareta da ido,sai kawai taji sumayyan ta mata kwarjini da irin kallon da take mata,janye idonta tayi ta dubi hajiya
"Hajiya kina gani dai a gabanki ko?" Ta fada cikin zafin rai,lukman yayi saurin karbewa
"Bana son rashin zaman lafiya fa sumayya a gida na kinji ko?" Kallon da wa kazo ta watsa masa sannan ta dauke kai,hajiya cikin rawar jiki tace
"Ke yarinya,farincikinmu shine farincikin karima,saboda haka dole ki mata biyayya ki kiyaye" girman hajiyan take gani,saboda haka ta dan rusuna
"Insha Allahu hajiya kiyi haquri" ta fadi da sauri tana shigewa kitchen din hajiyan don bata son ma ta sake kallon fuskar lukman bare ta karima.
Tana kitchen tana hada girkin duk da wasu kayan buqatun babu,mamaki da tunani fal ranta,a haka taji sallamar hajiyan,ta juya tana amsa mata,qarasowa hajiyan tayi ta kama hannun sumayya kamar zata saki kuka
"Kiyi haquri sumayya da abinda nayi miki dazu,yarinyar nan idan ta umarcemu da abu daga ni har lukman bama iya musa mata,amma nasan alhakin yaran jama'a ne yake bibiyata,haka kawai naji kin kwanta min sumayya zan gaya miki wace ni me na aikata ga rayuwata da rayuwar yarona"
Kafin sumayyan tace wani abu tuni hajiya ta fara bata labarin dukka aure auren da lukman yayi wanda ita ce sila,da fari haushin hajiyan ta dinga ji,amma daga bisani sai tausayinta ita da lukman ya baibayeta baki daya,tabbas abu na farko data fuskanta ya janyo wannan matsalar sakaci da rashin riqe ubangiji hannu bibbiyu,har qwalla sai data yiwa hajiya da lukman din saboda aikin kariman ya shallake hankali.
Cikin sanyin jiki ta riqe hannun hajiyan ganin tana zubda qwalla
"Kiyi haquri hajiya ki fawwalawa Allah lamarinki,ba shakka inna idan ma alhakin ne ba mamaki,Allah na sonki shi yasa zai hukunta ki tun a duniya,din hukuncin lahira da shi gwara na duniya sau babu adadi,in sha Allahu ni zanyi iya bakin qoqarina wajen ganin na daidaita lamarin iya abinda Allah ya huwace min,ina so daga yau kisa a ranki ba zaki qara jin tsoron karima ba,ba zaki sake bin umarninta ba sai abinda ya dace shi zakiyi,a duk sanda kika ganta idan kika ji faduwar gaba ko tsoro ki karanta ALLAHUMMAKH FINIHIM BIMA SHI'ITA matakin farko kenan,sannan daga yau kada ki sake cin duk abinda ya fito daga hannunta,ki umarci lukman ya kawo miki kayan abincinki a zuwan zaki ci gaba da girki,ni kuma in sha Allahi zanci gaba da dafa miki" kai take gyadawa cike da gamsuwa tana jin tamkar damuwarta na gab da yayewa
"Sannan lukman danki ne hajiya,bakin uwa kaifi gareshi,ki dage da yi masa addu'a,Allah ya yaye masa bala'in da ya fada ta sanadin abinda ke kika aikata shi,bashi kadai ba,har ke dinma saikin dage da addu'a wa kanki na neman tsari"
Kai ta sake jinjinawa
"Har na manta rabon da na sashi a addu'a ta,na gode da tunatar da ni da kikayi,na gode sosai"
"Sannan hajiya,kinsan rayuwar da nuwaira take cikin gida kuwa?" Ta tabo inda yafi mata qaiqayi
"Na sani sumayya na sani,saidai bani da ikon magana bani da ikon gyarawa" ta fada cikin jimami,don har ga Allah duk cikin jikokinta tafi qaubarta,din ta fita daban a cikinsu,nutsuwarta da komai da komai,shiru sumayyan tayi sannan tace
"Babu komai,zanyi iya bakin qoqarina itama akanta kafin Allah ya kawo qarshen lamarin"
"Na gode sumayya na gode,haqiqa kin zamo *HASKE* cikin gidan d'ana cikin kwana daya tal,ina miki fatan alheri sannan kuma ina miki fatan samun nasara,Allah ya albarkaci rayuwarki da alkhairi masu tarin yawa,ya tsareki" amin sumayya ta dinga cewa tana jin dadin addu'ar har cikin ranta,ko da can ita din mai son wani na gaba da ita ne ya albarkaceta,kusan tare suka gama aikin ta kammalewa hajiyan cikin kula yadda tasan zai ishesu ita da nuwaira,tace zata turo mata ita taci na rana dana dare,don ta lura bata samu albarakacin cin na safe ba,sai na hajiyan da suka yayyafita.
Nan tayi zamanta gun hajiya,ita kanta hajiyan sai ta dinga jin dadi cikin ranta,nuwaira ma ta dinga sato jiki tana leqowa har sanda sumayyan ta koma bangarensu.
***** ****** ******
"Me yasa kinsan kina fitsarin kwance da kika tashi baki sauya kayanki ba nuwaira?,kinsan fa ba'a son mace da qazanta" sai yarinyar ta fara qwalla ta soma sharewa tana cewa
"Wallahi anty tunda bana fitsarin kwance,saddiqa keyi sai a hadamu kwanciya gado daya,idan tayi duk sai ya jiqani,idan ta tashi ita sai nuratu ta sauya mata kaya,ni kuma ba zan canza ba har sai umma ta gama bacci tayi wanka ta fito sannan zata nunan wadanda zan sauya din,koda asuba bana samu nayi sallah sai rana ta fito" ta fada da alamu abun na ci mata tuwo a qwarya,shiru sumayya tayi tausayin yarinyar na kamata,wannan wanne irin zalunci ne,tun kallon farko da ta yiwa yarinyar ya nuna tana jin jiki a gidan,amma tana tunanin kamar ita ce yarinyar nan daya da karima jiya ta gaya mata uwarta daban,don ta tabbatar sai ta tambayeta
"Ina mamarki to?"
"Mama na tayi aure a wani gidan,tun kafin a yayeni aka karboni aka bawa hajiya ni,to da abbanmu ya sake aure ya auro umma sai umman ta karbeni nake gunta"take tsanar karima ta darsu a zuciyar sumayya,lallai ba shakka bayan shirkar tsafi ma harda azabtar da yarinyar da bata ji ba bata gani ba,wai me mutane suka dauki duniya ne?,kowacce mace son kanta ya mata yawa?,burinta ta mallaki miji ta rabashi da kowa nasa?,ta rabashi da 'yan uwansa da tazo ta samesu tare,'yan uwa da suka zamar masa bango marufar asiri tun yana zanin tsumma har kawo yau,ta rabashi da duk wani alkhairi uwa uba ta rabashi da mahaliccinsa,ta sakashi a musibar da ranar gobe qiyama bazai iya tsallaketa ba,ta rabashi da hankalinsa bare ya kula da addininsa,wanda ya cancanci a bashi haqqinsa ta hana ya basu yanzu duka wannan qauna ce?,sai tace sonshi take shi yasa ta aikata haka,wannan ko babban maqiyinka ba shakka iya cutarwar da zai maka kenan,da irin wannan tunani suka isa bangaren hajiyan.
A duqe suka sameta tana share falon nata dake malale da carfet,kallo daya sumayya tayi mata ta fuskanci shekarunta basukai ace tayi tsufar da tayi a yanzu ba,da sallama suka shiga ta dago tana amsa musu riqe da qugunta wanda bisa dukkan alamu ciwo yake mata,nuwaira ce ta gaisheta ta amsa babu yabo ba fallasa yayin da sumayya ta qarasa tana amsar tsintsiyar hannunta tana gaidata,amsawa tayi tana dubanta yayin da sumayya ke qarasa mata sharar har ta kammala sannanbta dawo inda hajiyar ke zaune tana yiwa nuwaira masifar sai zuba zarni take taje bandakinta ta wanke jikinta,mamaki ya cika sumayyar,to ko batasan meke wakana bane cikin gidan?,batasan ba laifin nuwairan bane karima ce ta cancanci fada idan da duka ma ayi mata?,tashi yarinyar tayi ya shige bandakin hajiyar sannan hajiyar ta maido kallonta ga sumayyan
"Ban gane fuskar ba wace ce ne?" Murmushi kawai tayi ta dan sad da kai
"Oho,ko amaryar lukman ce" kai sumayyan ta gyada.
Shiru ne ya biyo baya,hajiyan na dan satar kallon sumayyan,sai taji ta dan sake da yarinyar duk da ba hira suke ba zaman kurame ne,a haka har nuwaira ta fito daga bandakin sanye da jiqaqqun kayanta wadanda ta wanke bayan ta dauraye jikinta ta maida su a haka
"Wani nuwaira nikam bakuyu abin kari bane yau,gashi har sha daya na shirin gotawa yau ba'a kawo kin komai ba,ko luba mai aikin bata zo bane?"cike da madaukakin mamaki sumayya ke sauraron zancan
"Tazo hajiya,bansan ba'a kawo miki ba,don ko nima yau ban karya ba,naga dai su nuratu na karyawa ni ma ba'a bani nawa ba"ta fadi babu alamun damuwa tattare da ita bisa dukkan alamu ta riga da ta saba da hakan,yamutsa fuska hajiyan tayi
"gaskiya na fara jin yunwa wlh,wannan abu Allah kayi mana maganinsa"
"Amma hajiya ai naga kina da sauran kayan abincinki da kika ce bazaki iya ci gaba da girki ba ai abba bai debe su ba ko?"
"To idan banda abinki ina fama da lalura ina zan iya,sharar ma don bazan iya zama cikin qazanta bane nake daburtawa nake yinta" ta fada ta muskutawa da alamu yunwa na sakadarta,tausayinta duka sai ya kama sumayya ta dubeta
"To hajiya idan ba damuwa sai na shiga na girka miki ai ko?"haba ta riqe
" a'a,har kya fara shiga madafi ta sanadina?,ki barshi babu komai idan da sabo ai mun saba da irin wannan gashin,ke dai kawai Allah yayi mana magani"murmushi tayi kawai ta miqe tana tambayar nuwaira inda kitchen din yake.
Sallamar karima a gadarance ita ta maida hankalinsu bakin qofar,ita ke gaba gogan na binta a baya riqe da wani dan qaramin flask wanda bako shakka abun karin hajiyan ne a ciki,idanunsa na kan sumayya yana faman sakar mata murmushi ,wani takaici da haushinsa suka qumeta saita dauke kai tana jin kamar taje ta shaqeshi,haka nan kawai taji jarumin namiji yana burgeta,sai ta tuna sanda zainab ta fara murza kambunta lokacin tana gidan mukhtar,tabbas ko a lokacin mukhtar din kan tauna tsakuwa wani lokaci.
Hajiyan da za'a yiwa sannu a gaisheta ita ke faman yiwa kariman sannu tare da gaisheta,lukman ya koma gefan hajiyan yana gaidata cikin dari dari suke gaisawar kamar suruki da suruka duk don kada su batawa karima rai,baki sumayya ta saki tana kallon abun mamaki bayan hajiya ta bude flask din da aka kawo mata,wani gantalallen soyayyen dankali ne da rabin wainar qwai babu ko tea amma hajiyan sai godiya da sannu take mata
"Saidai yau kici haka hajiya don kafin na fito jikokin naki sun shanye shayin"
"Ai babu komai,idan baka yiwa jikanka ba wa zaka yiwa" ta fada fara'a kamar gonar auduga.
Kallon sumayya karima tayi bayan sumayyan ta gaida lukman wanda ke faman binta da kallo kamar tsohon maye
"Ke baki iya gaida mutane ba" ta fada fuska a tsuke kamar wata uwarta,waigawa sumayyan tayi ta watsa mata kallo
"Su waye mutanen?" Ta tambayeta bayan ta tsareta da ido,sai kawai taji sumayyan ta mata kwarjini da irin kallon da take mata,janye idonta tayi ta dubi hajiya
"Hajiya kina gani dai a gabanki ko?" Ta fada cikin zafin rai,lukman yayi saurin karbewa
"Bana son rashin zaman lafiya fa sumayya a gida na kinji ko?" Kallon da wa kazo ta watsa masa sannan ta dauke kai,hajiya cikin rawar jiki tace
"Ke yarinya,farincikinmu shine farincikin karima,saboda haka dole ki mata biyayya ki kiyaye" girman hajiyan take gani,saboda haka ta dan rusuna
"Insha Allahu hajiya kiyi haquri" ta fadi da sauri tana shigewa kitchen din hajiyan don bata son ma ta sake kallon fuskar lukman bare ta karima.
Tana kitchen tana hada girkin duk da wasu kayan buqatun babu,mamaki da tunani fal ranta,a haka taji sallamar hajiyan,ta juya tana amsa mata,qarasowa hajiyan tayi ta kama hannun sumayya kamar zata saki kuka
"Kiyi haquri sumayya da abinda nayi miki dazu,yarinyar nan idan ta umarcemu da abu daga ni har lukman bama iya musa mata,amma nasan alhakin yaran jama'a ne yake bibiyata,haka kawai naji kin kwanta min sumayya zan gaya miki wace ni me na aikata ga rayuwata da rayuwar yarona"
Kafin sumayyan tace wani abu tuni hajiya ta fara bata labarin dukka aure auren da lukman yayi wanda ita ce sila,da fari haushin hajiyan ta dinga ji,amma daga bisani sai tausayinta ita da lukman ya baibayeta baki daya,tabbas abu na farko data fuskanta ya janyo wannan matsalar sakaci da rashin riqe ubangiji hannu bibbiyu,har qwalla sai data yiwa hajiya da lukman din saboda aikin kariman ya shallake hankali.
Cikin sanyin jiki ta riqe hannun hajiyan ganin tana zubda qwalla
"Kiyi haquri hajiya ki fawwalawa Allah lamarinki,ba shakka inna idan ma alhakin ne ba mamaki,Allah na sonki shi yasa zai hukunta ki tun a duniya,din hukuncin lahira da shi gwara na duniya sau babu adadi,in sha Allahu ni zanyi iya bakin qoqarina wajen ganin na daidaita lamarin iya abinda Allah ya huwace min,ina so daga yau kisa a ranki ba zaki qara jin tsoron karima ba,ba zaki sake bin umarninta ba sai abinda ya dace shi zakiyi,a duk sanda kika ganta idan kika ji faduwar gaba ko tsoro ki karanta ALLAHUMMAKH FINIHIM BIMA SHI'ITA matakin farko kenan,sannan daga yau kada ki sake cin duk abinda ya fito daga hannunta,ki umarci lukman ya kawo miki kayan abincinki a zuwan zaki ci gaba da girki,ni kuma in sha Allahi zanci gaba da dafa miki" kai take gyadawa cike da gamsuwa tana jin tamkar damuwarta na gab da yayewa
"Sannan lukman danki ne hajiya,bakin uwa kaifi gareshi,ki dage da yi masa addu'a,Allah ya yaye masa bala'in da ya fada ta sanadin abinda ke kika aikata shi,bashi kadai ba,har ke dinma saikin dage da addu'a wa kanki na neman tsari"
Kai ta sake jinjinawa
"Har na manta rabon da na sashi a addu'a ta,na gode da tunatar da ni da kikayi,na gode sosai"
"Sannan hajiya,kinsan rayuwar da nuwaira take cikin gida kuwa?" Ta tabo inda yafi mata qaiqayi
"Na sani sumayya na sani,saidai bani da ikon magana bani da ikon gyarawa" ta fada cikin jimami,don har ga Allah duk cikin jikokinta tafi qaubarta,din ta fita daban a cikinsu,nutsuwarta da komai da komai,shiru sumayyan tayi sannan tace
"Babu komai,zanyi iya bakin qoqarina itama akanta kafin Allah ya kawo qarshen lamarin"
"Na gode sumayya na gode,haqiqa kin zamo *HASKE* cikin gidan d'ana cikin kwana daya tal,ina miki fatan alheri sannan kuma ina miki fatan samun nasara,Allah ya albarkaci rayuwarki da alkhairi masu tarin yawa,ya tsareki" amin sumayya ta dinga cewa tana jin dadin addu'ar har cikin ranta,ko da can ita din mai son wani na gaba da ita ne ya albarkaceta,kusan tare suka gama aikin ta kammalewa hajiyan cikin kula yadda tasan zai ishesu ita da nuwaira,tace zata turo mata ita taci na rana dana dare,don ta lura bata samu albarakacin cin na safe ba,sai na hajiyan da suka yayyafita.
Nan tayi zamanta gun hajiya,ita kanta hajiyan sai ta dinga jin dadi cikin ranta,nuwaira ma ta dinga sato jiki tana leqowa har sanda sumayyan ta koma bangarensu.
***** ****** ******