Sashe 203
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 7 min read
Jakarta kawai ta ajjiye suka fito ita da mommyn nata,ta riga data siya musu tikitin jirgin qasa har ya zuwa unguwar da sibitin yake da zama,tafiya ce ta kusan awanni daya,wanda cikin awa daya da rabi suka isa ga ofishin ainihin likitan da suke nema,doctor james,haifaffan qasar america,mutum da ya tashi da tsantsar aqidar yahudawa ta aihini,sannan ya ginu kan qiyayyar musulunci da musulmai,ko kadan baya qaunar musulmi a zuciyarsa,qwararren likitane na gyni wanda ya qware ya kuma shahara wajen saida sperm yin dashe d'a dana qwayayen haihuwa,shahararsa ta sanya mummu kashe kudade masu yawa domin su ganshi don samun biyan buqatarsu,da idanu yake kallonsu bayan ya gama jin abinda ya kawosu,uasan tabbas ba mai yiwuwa bane,haihuwa ga macen da babu mahaifa tattare da ita kwata kwata,saidai kuma tunda aka masa transfer na sunayensi cikin system dinshi ya tabbatar da musulmai ne,baya jin kuwa zai barsu su fita a office dinsa salin alin ba tare da ya zaluncesu ba,wanda wannan shine babban burinsa,agender dake gabanshi tsakaninsa da wani shahararren mai kudi dake garin nasu ya fado masa,hakan ya sanyashi sakin murmushi,ba shakka zuwansu yayi daidai,haka faduwa tazo dai dai da zama,murmushinsa ya jefa musu zaton cewa nasara ce qarara ya hango,sai ya karkace ya zuba musu bayanin cewa zata haihu kamar kowacce mace,zasuyi mata aikin da bazata farka ba sai da juna biyu,nan da kwanaki uku ta taho asibitin zasu soma aikin nasu,kudi kadan ya yanka musu ahakan ma ya karba ne kawai don kada ya darsa zargi cikin zuciyarsu saboda yasan cewa kudaden da zaya samu zasu mai dashi cikin jerin sahun masu kudin garin,zuciyarsu fes suka bar asibitin,tun a sannan su'ad din ta fara hasashen irin abubuwan da zata shuka bayan bayyanar ciki a jikinta,bata jin zata dagawa wani cikinsu qafa,kowa sai ta takashi dai dai da abinda yayi mata.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[3/20, 12:57 PM] Bilki M. Rabiu: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
1⃣0⃣6⃣
*KADA KI WUCE BAKI KARANTA BA*
*SHIMFIDA MAI MUHIMMANCI*
*bismillahir rahmanir rahim*
*Allah S W T yana fada cikin qur'aninsa mai girma*
*ku koma izuwa ubangijinku ku tsarkake aiki dominsa,tun kafin azaba tazo muku,sannan ba za'a taimakeku ba(da hana saukar azabar idan baku tuba ba*
*kubi kyakkyawan abinda aka saukar izuwa gareku daga ubangiji tun gabanin azaba bata zo muku bagatatan bakuyi hasashen zuwanta ba*
*tun kafin rai bata ce ba "ya asarata/tabewa ta bisa sakacim da nayi a janibin Allah,haqiqa na kasance cikin masu wasa*
*ko tace "da Allah ya shiryeni da na kasance daga cikin masu tsoron Allah*
*ko tace lokacin da taga azaba " da ace ina da damar komawa izuwa duniya izuwa duniya dana kasance daga cikikin mash kyakkyawan aiki*
______________________________________
*WANNAN SHAFIN SADAUKARWA NE GA MEELA ADEEL DA SAURAN DUKA MASOYAN SU'AD*
Kallo daya zaka yi masa ka tabbatar da cewa ba cikin nutsuwa walwala da kwanciyar hankali yake ba,tunda ya diro qasar bayan kira da ya samu na gaggawa daga hajiya khaulat kwana ashirin da tafiyar su'ad din bai sake samun isashen bacci ba cikin nutsuwa,me ya sameta haka har ta fice hayyacinta bata gane kowa?,me ya kawota asibiti cikin wani gari wanda ba nasu ba bayan gidansu suka yi da shi zata je?,me ya sameta haka meye dalili?,babban abinda ya daga masa hankali shine doctor james,wanda a cewar hajiya khaulat shike duba su'ad,tare sukayi karatu da shi,dalibi me cikin jami'ar da yayi karatu,ajinsu daya course dinsu daya,hasalima yana daya daga cikin mutaben da basa shiri sam,saboda aqidarsa ta qin jinin musulunci da musulmai,uwa uwa yana matuqar adawa da qoqarin da almustapha ke da shi,yana daga cikin gungun dalibai 'yan adawarshi,kusan ma shine shugaba,jamea baida kirki ko kadan,bai da tausayi kuma bashi da imani,dalilin wai laifi da suka aikata shi ya sanya aka koreshi yana shekarar warshe a makarantar,saidai sunji labarin ya sauya qasa ya qarashe karatunshi har ma ya bude asibiti,tunda yaje basu hadu da james ba,duk sanda zaije asibitin suna sabani ne,randa suka hadu ya jima yana kallon almustapha,irin kallon da ya sake sanya shakku cikin zuciyar almustapha,bugu da qari daya buqaci bayani kan meye damuwar su'ad bayanin da yayi masa sam bai gamsheshi ba hakan ya sanya ya quduri shiga aikin da kanshi a matsayinsa na likita.
A ranar yayi waya da wani farar fata abokinsa,wanda yake da asibiti shima hafin gwiwa da gwamnati,almustaphan ya sanya aka hada masa daki guda da dukkan abinda yake buqata,wanda a yau ya shirya yin bincike a kanta.
Kaman ko yaushe tana kwance iskar oxcygen na taimakawa numfashinta,yayin da hajiya khaulat ke gefe cikin fita hayyaci,tunda take bata taba fuskantar tashin hankali tsahon rayuwarta ba irin wannan karon,idanuna sun yi luhu luhu,tayi kuka har ta gaji,batasan wanne irin aiki ne haka doctor james ya yiwa diyar tata qwaya daya tilo ba wanda ya sanyata shiga wannan matsanancin halin,sanda taga almustapha ya shigo dakin jikinta har rawa yake,kwarjini yake mata sosai irin wanda ada can baya baiyi mata ba,a mutunce ya gaidata yana maida kallonshi ga su'ad tare da tambayarta jikin nata,ba amsa sai kuka data sanya,ranshi a jagule yake qwarai,ya qagu ya duba abinda ke faruwa,shigowar ma'aikatan jinyar ya katse duk abinda haj khaulat din keson gaya masa,sai data ga suna daukar su'ad daga gadon da take zuwa wanda suka shigo da shi mai taya da alama zasu fita da ita ne sannan ra magantu cikin rawar baki
"Mustapha...ina..ina zaku da ita"
"Zanje nayi nawa binciken ne,saboda bayanin da james yayimin bai gamsheni ba,nasanshi ya sanni tun ba yau ba" ya fada yana ciro wayoyinshi ya ajjiye gefe guda,ita dinma tana shanshano wani abu,din bata yarda da cewa aikin da suka buqata din kadai yayi mata ba
"Amma yau professor da alhaji zasu iso,inaga a bari su iso din ko?"
"Ina so kafin suzo din in san amsar da zan basu kan me ya sameta,tunda ku da kuke tare sanda abun ya sameta baku san meye sababi ba" ya fadi haka sanda yake takawa ya fice yana bin bayan masu turatan.
Sanda ya haska fitilar nan mai tsananin haske abu na farko da idanunahi suka fara masa karo da shi hudar dake qasan cibiyarta da kuma wadda ke gefan hannun hagunta,saidai daya ta warke daya kuma danya ce,gabanshi yayi mummunan faduwa,addu'a yake Allah kada ya tabbatar da abinda yake tsammani,a hankali cikim qwarewa da hikima ya jona duk wata cumputer da yake da buqata wadda zata taimakawa bincikensa cikin sauqi ya soma aikinsa cikin lura da taka tsantsan.
Cikin awa guda qwaqwalwarsa ta soma yamutsewa,ba abinda yake ambata sai innalillahi wa inna ilaihi raji'un,gumi ya hada sharkaf,sai ya saki duk abinda yake ya koma saman kujera ya zauna,nanya manyan lamura biyu kowanne yana sukuwa cikin qwaqwalwarsa,kowanne buqata yake ya soma sarrafashi,su'ad babu mahaifa tattare da ita?,babu qodarta ta hannu hagu an illata mata ta dama?,duka aikin waye wannan?,aikin waye?,ta shiga nanatawa kanshi tambayar,cikin wasu qalilan sakanni idanunshi suka kada suka koma jazur,ya dinga fidda huci kaman kumurcin maciji,wani bala'in tausayin su'ad din ya mamayeshi,me ta yiwa wani har ya mata haka?,waye ya aikata mata haka?"
"Zai wuce doctor james" wami bangare na zuciyarshi ya bashi amsa,a fusace ya miqe cikin tsananin fushi
"To amma me ya hadasu da shi?,me ya kawosu wajenshi?" Cak ya tsaya sanda wani sashe na zuciyarshi ya jefo masa wannan tambayar,a hankali ya koma ya zauna yana kiran sunayen Allah dafe da kanshi.
Ya jima kafin ya samu ya yiwa kansa control,tabbas sai ya saka nutsuwa indai yana son komai ya dai daita,a hankali kaman wanda aka yiwa dukan tsiya ya miqe ya hada mata qarin ruwa ya zuba magungunan da yasan zasu taimaka mata sannan ya sanya ma'aikatan suka maidata dakinta,kai tsaye ya fice daga asibitin shida drivansa.
Bai koma gida ba sai daya samu dukkan bayanan da yake so cikin kwana daya tal,abinda yaji kan doctor james yayi matuqar girgizashi,saidai ya hada dukkan wasu hujjoji da bayanai waje daya,banu nutsuwa ko ta qwayar zarra tattare da shi haka yayi wanka ya sauya kaya,yana ganin tarin misscal na sumayya da saqonni saidai ya kasa karantawa ko yabi kiran haka ya sake ficewa.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[3/20, 12:57 PM] Bilki M. Rabiu: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
1⃣0⃣6⃣
*KADA KI WUCE BAKI KARANTA BA*
*SHIMFIDA MAI MUHIMMANCI*
*bismillahir rahmanir rahim*
*Allah S W T yana fada cikin qur'aninsa mai girma*
*ku koma izuwa ubangijinku ku tsarkake aiki dominsa,tun kafin azaba tazo muku,sannan ba za'a taimakeku ba(da hana saukar azabar idan baku tuba ba*
*kubi kyakkyawan abinda aka saukar izuwa gareku daga ubangiji tun gabanin azaba bata zo muku bagatatan bakuyi hasashen zuwanta ba*
*tun kafin rai bata ce ba "ya asarata/tabewa ta bisa sakacim da nayi a janibin Allah,haqiqa na kasance cikin masu wasa*
*ko tace "da Allah ya shiryeni da na kasance daga cikin masu tsoron Allah*
*ko tace lokacin da taga azaba " da ace ina da damar komawa izuwa duniya izuwa duniya dana kasance daga cikikin mash kyakkyawan aiki*
______________________________________
*WANNAN SHAFIN SADAUKARWA NE GA MEELA ADEEL DA SAURAN DUKA MASOYAN SU'AD*
Kallo daya zaka yi masa ka tabbatar da cewa ba cikin nutsuwa walwala da kwanciyar hankali yake ba,tunda ya diro qasar bayan kira da ya samu na gaggawa daga hajiya khaulat kwana ashirin da tafiyar su'ad din bai sake samun isashen bacci ba cikin nutsuwa,me ya sameta haka har ta fice hayyacinta bata gane kowa?,me ya kawota asibiti cikin wani gari wanda ba nasu ba bayan gidansu suka yi da shi zata je?,me ya sameta haka meye dalili?,babban abinda ya daga masa hankali shine doctor james,wanda a cewar hajiya khaulat shike duba su'ad,tare sukayi karatu da shi,dalibi me cikin jami'ar da yayi karatu,ajinsu daya course dinsu daya,hasalima yana daya daga cikin mutaben da basa shiri sam,saboda aqidarsa ta qin jinin musulunci da musulmai,uwa uwa yana matuqar adawa da qoqarin da almustapha ke da shi,yana daga cikin gungun dalibai 'yan adawarshi,kusan ma shine shugaba,jamea baida kirki ko kadan,bai da tausayi kuma bashi da imani,dalilin wai laifi da suka aikata shi ya sanya aka koreshi yana shekarar warshe a makarantar,saidai sunji labarin ya sauya qasa ya qarashe karatunshi har ma ya bude asibiti,tunda yaje basu hadu da james ba,duk sanda zaije asibitin suna sabani ne,randa suka hadu ya jima yana kallon almustapha,irin kallon da ya sake sanya shakku cikin zuciyar almustapha,bugu da qari daya buqaci bayani kan meye damuwar su'ad bayanin da yayi masa sam bai gamsheshi ba hakan ya sanya ya quduri shiga aikin da kanshi a matsayinsa na likita.
A ranar yayi waya da wani farar fata abokinsa,wanda yake da asibiti shima hafin gwiwa da gwamnati,almustaphan ya sanya aka hada masa daki guda da dukkan abinda yake buqata,wanda a yau ya shirya yin bincike a kanta.
Kaman ko yaushe tana kwance iskar oxcygen na taimakawa numfashinta,yayin da hajiya khaulat ke gefe cikin fita hayyaci,tunda take bata taba fuskantar tashin hankali tsahon rayuwarta ba irin wannan karon,idanuna sun yi luhu luhu,tayi kuka har ta gaji,batasan wanne irin aiki ne haka doctor james ya yiwa diyar tata qwaya daya tilo ba wanda ya sanyata shiga wannan matsanancin halin,sanda taga almustapha ya shigo dakin jikinta har rawa yake,kwarjini yake mata sosai irin wanda ada can baya baiyi mata ba,a mutunce ya gaidata yana maida kallonshi ga su'ad tare da tambayarta jikin nata,ba amsa sai kuka data sanya,ranshi a jagule yake qwarai,ya qagu ya duba abinda ke faruwa,shigowar ma'aikatan jinyar ya katse duk abinda haj khaulat din keson gaya masa,sai data ga suna daukar su'ad daga gadon da take zuwa wanda suka shigo da shi mai taya da alama zasu fita da ita ne sannan ra magantu cikin rawar baki
"Mustapha...ina..ina zaku da ita"
"Zanje nayi nawa binciken ne,saboda bayanin da james yayimin bai gamsheni ba,nasanshi ya sanni tun ba yau ba" ya fada yana ciro wayoyinshi ya ajjiye gefe guda,ita dinma tana shanshano wani abu,din bata yarda da cewa aikin da suka buqata din kadai yayi mata ba
"Amma yau professor da alhaji zasu iso,inaga a bari su iso din ko?"
"Ina so kafin suzo din in san amsar da zan basu kan me ya sameta,tunda ku da kuke tare sanda abun ya sameta baku san meye sababi ba" ya fadi haka sanda yake takawa ya fice yana bin bayan masu turatan.
Sanda ya haska fitilar nan mai tsananin haske abu na farko da idanunahi suka fara masa karo da shi hudar dake qasan cibiyarta da kuma wadda ke gefan hannun hagunta,saidai daya ta warke daya kuma danya ce,gabanshi yayi mummunan faduwa,addu'a yake Allah kada ya tabbatar da abinda yake tsammani,a hankali cikim qwarewa da hikima ya jona duk wata cumputer da yake da buqata wadda zata taimakawa bincikensa cikin sauqi ya soma aikinsa cikin lura da taka tsantsan.
Cikin awa guda qwaqwalwarsa ta soma yamutsewa,ba abinda yake ambata sai innalillahi wa inna ilaihi raji'un,gumi ya hada sharkaf,sai ya saki duk abinda yake ya koma saman kujera ya zauna,nanya manyan lamura biyu kowanne yana sukuwa cikin qwaqwalwarsa,kowanne buqata yake ya soma sarrafashi,su'ad babu mahaifa tattare da ita?,babu qodarta ta hannu hagu an illata mata ta dama?,duka aikin waye wannan?,aikin waye?,ta shiga nanatawa kanshi tambayar,cikin wasu qalilan sakanni idanunshi suka kada suka koma jazur,ya dinga fidda huci kaman kumurcin maciji,wani bala'in tausayin su'ad din ya mamayeshi,me ta yiwa wani har ya mata haka?,waye ya aikata mata haka?"
"Zai wuce doctor james" wami bangare na zuciyarshi ya bashi amsa,a fusace ya miqe cikin tsananin fushi
"To amma me ya hadasu da shi?,me ya kawosu wajenshi?" Cak ya tsaya sanda wani sashe na zuciyarshi ya jefo masa wannan tambayar,a hankali ya koma ya zauna yana kiran sunayen Allah dafe da kanshi.
Ya jima kafin ya samu ya yiwa kansa control,tabbas sai ya saka nutsuwa indai yana son komai ya dai daita,a hankali kaman wanda aka yiwa dukan tsiya ya miqe ya hada mata qarin ruwa ya zuba magungunan da yasan zasu taimaka mata sannan ya sanya ma'aikatan suka maidata dakinta,kai tsaye ya fice daga asibitin shida drivansa.
Bai koma gida ba sai daya samu dukkan bayanan da yake so cikin kwana daya tal,abinda yaji kan doctor james yayi matuqar girgizashi,saidai ya hada dukkan wasu hujjoji da bayanai waje daya,banu nutsuwa ko ta qwayar zarra tattare da shi haka yayi wanka ya sauya kaya,yana ganin tarin misscal na sumayya da saqonni saidai ya kasa karantawa ko yabi kiran haka ya sake ficewa.