← Book details Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 82 OF 210

Sashe 82

Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 7 min read

Suna shiga motar laila tace
"Lah,wallahi anty sumayya kinga har ya biyo mu ya koma,ta fada tana qyalqyala dariya"
"Waye ya biyo mu" anty dije ta tambaya tana qoqarin maida atm dinta jaka
"Ba kowa" sumayya ta fada da sauri sannan ta juya tana kallon laila,harararta tayi sannan tace
"Bana son surutu komai kika gani kiyi magana kai,idan ba haka ba bazamu shirya ba"
"Sorry anty sumayya" ta fada tana narke fuska don ta cikawa su hafiz baki ita ce ta gaban goshin anty sumayya bata son su gansu a rana
"Shikenan" ta fada tana gyara zamanta,sai da suka sake daukar hanya sosai sannan ta lalubi wayarta da niyyar kiran yaya yahanasu,sai taci karo da misscall din abdur rahman,sai kuma saqon SMS
_garin masoyi baya nisa,ina miki fatan alkhairi_ abinda kawai ya rubuta kenan,bata fahimci zaurencen nasa ba saboda haka ta share ta lalubi lambar yaya yahanasun ta danna kira,ringing biyu ta daga,cikin mutunci suka gaisa sannan aka nemo mata abdallah aka hadata da shi,hira ya dinga mata wani shirme wani abun dariya haka ta dunga dariya,daga bisani su laila suka amshe wayar suka yita shirmensu su da shi sai da suka cinye nata credit dinta tatas sannan suka haqura,bayanta ta maida makarin kujerar ta lumshe idanuwa zuciyarta fes tana jin dadi da jin muryar abdallah da tayi,tabbas d'a ba wasa bane,ababe ne masu wanke zukatan mahaifansu koda da shirme da quruciyarsu kadai,tunanin mukhtar shi ya ratso cikin farincikinta ya gusar da shi cikin yab sakanni qalilan,taje fuskarta ta sauya,damuwa ta lullube zuciyarta,taso abdallah ya rayu da mahaifinsa,yaci gaba da cin gajiyar gata da mahaifinsa ya tanadarwa rayuwarsa saidai ina,tsarin ubangiji shine daidai,tana jin hayaniyar su laila amma tayi fakare kamar mai bacci,bata sake bude idanuwanta ba har suka shiga garin abuja.

Qarfe biyar da rabi suka isa garin,bata mance yadda unguwar tasu take ba saidai an sake samun sauye sauye,sabbin gine gine da kuma sabunta tsoffin.

A falo suka zube baki dayansu wanda basu tashi ba sai da lokacin sallar magariba yayi sannan kowa ya debi kayansa zuwa daki,a dakin laila da minal ta zabi zama,kasancewar gado uku ne a dakin,daki ne madaidaici wanda ke shimfide da tiles da labulaye sai fenti dukkansu kala daya,wardrobe ce irin ta jikin bango wadda ta cinye bango guda,sai madubi a wani bangon daban,daya bangaren kuma gun ajitar takalma ne zuwa su jakankunan makarantarsu,daura da nan kuma qofar bandaki ne,sallah ta sanyasu suka fara yi sannan suka bude kayansu suka koma maidasu muhallinsu,a wanke a goge suke dawo da kayansu kamar yadda suka tafi da su.

Anty dije ce ta turo qofar dakin ta shigo,wannan karon ta sauya kayan jikinta da alamu ma wanka tayi don sai qamshi take zubawa ta dubesu tana zama gefan daya cikin gadajen dakin
"Sannunku da himma,hala ma ko wanka ba wanda yayi a cikinku ko?"
"Ummi sai mun gama gyaran kaya"inji laila
"eh kam bakwajin yunwa ne" anty dije ta sake fada,murmushi sumayya tayi din itakam ba yunwa tattare da ita,miqewa anty dije tayi
"Idan kun gama ga takeaway can da abban laila ya shigo da shi sai ku dauka kuci,nikam ina ga sai da safe zamu sake haduwa da ku"
Minal ce ta miqe da sauri
"Ummi zani gun abba"
"A'ah,ya shiga daki shima a gajiye ya dawo,abba sai da safe ki kwanta ga anty sumayya nan sumayya sai da safe,ayi kwanan baqunta lafiya" dariya duka sukayi sumayya tace
"Allah ya bamu alkhairi anty"
"Amin" ta amsa tana ficewa.

Kamin wani lokaci sun gama kintsa komai,sai da suka ci abincin sannan suka yi wanka kowacce tayi shirin kwanciya,tana saman gadonta lullube da bargo saboda ac da laila ta kunna wayarta ta soma haske sabida ta maidata silent,abdur rahman ne kamar ba zata daga ba saboda bacci take da buqatar yi,amma sai taga hakan bai dace ba,a mutunce ta gaida shi ya shaida mata ya kirata dazun kiran bai shiga,ta sanar masa,mai yiwuwa lokacin suna kan hanya ne ba service,qorafi ya shiga yi mata kan dalilin tafiyarta bata sanar masa yace
"A qalla ko addu'a sumayya na miki ko?,har yau kinqi gayan dalilin da ya sanya baki sona" baki ta bude kamar yana ganinta
"Ni bance ma bana sonka ba abdur rahman,kawai dai ina da buqatar hutu ne cikin rayuwata,har yau zuciyata da qwaqwalwata basu zama fresh ba,kuma ko baya ga haka ma banson na zalunceka,don banajin akwau mahaluqin da zanso kwatankwacin mukhtar,zanfi so na qarashe rayuwata a haka naje na tadda shi a inda yake" shiru ya ratsa wayoyin nasu kafin daga bisani ya sauke ajiyar zuciya
"Wannan ba hujja bace,amma har zuwa yaushe kike ganin qwaqwalwarki zata zama fresh din na daga miki qafa zuwa wannan lokacin?"
"Ban sani ba nima abdur rahman,ban da masaniya" ta fada da alamun ta fara karaya,shuru ya sakeyi,ta tabbata sumayya abar tausayi ce,hakanaj dole ayi mata uziri,amma ya ya iya bazai iya rabuwa da ita ba,tsakanin jiya da yau kawai lissafinsa ya dagule,aikin da ya tafi sokoto domin shi ya gaza aiwatar da komai
"Zan bar miki maganar da baki so har zuwa sanda zaki buqaci haka,saidai ina son don Allah mu maida dangantakar mu ta baya ta wa da qanwa,idan na kiraki ki amsamin kamar dan uwanki kin yarda?"
"Anya hakan ma zai yiwu?"
"Mai zai hana kin manta abdur rahman ne dan zaman dakinki?" Dariya ya sanyata wadda ta taho da hawaye,ya tuna mata wani abu can baya,wani abu da bazai taba goguwa cikin KUNDIN tarihin rayuwarta ba,dadi yaji cikin ransa da ya fuskanci ta sake,bai wani cikata da surutu ba sosai yace ta kwanta tayi bacci zaya kirata gobe yaji yaya kwanan abuja.

*WAI INA ZAINAB NE?*

Tun sanda aka kaita asibitin ta soma gane Allah da girma yake,ga cutar qanjamau dake cin kowane sashi na jikinta,ga qafa wadda ta tasamma rubewa koma ace ta rube,ga hannu daya kullum daurw da ankwa jikin qarfen gado,gwajin farko aka gano cancer ta shiga ciwon saboda haka tilas a yanke qafar kada dayar ma ta harbu,kuka ta dinga yi wiwi da idanuwanta sanda aka nemi kudin da za'a biya ma a samu a yanke qafar aka rasa,ita ta shawarci mamarta da cewa
"Mama,ko kadarorina dake cikin dakina za'a diba a saida a biya tunda ku kun kasa biyamin,bakusan bala'in da nake kwana nake tashi a cikinsa ba" kallon banza maman tayi mata ganin cewa har yanzu bakin zainab din bai gama rusuna ba,duk da halin da take ciki
"Wadanne kadarori kuma kike da su,bayan wadanda kika aiko zinatu ta diba ta saida miki ta kaiwa alqali kudin don ki samu nasara kan shari'arki,da yake Allah ba azzalumin bawa bane gashinan abinda kika aikata yana bibiyarki" ihu ta kwarara wanda ya janyo hankalin jami'an tsaron dake gadinta,wadanda basa rabuwa da ita koda tayi bacci,rantse rantse ta shiga yi kan cewa ba ita ta aiko zinatu ba,maman taje ta nemota duk inda take damfararta tayi,kudin da take sa ran za'a dinga juya mata ana aiko mata da su don tayi rayuwa mai kyau da'yanci cikin kurkuku(kujifa,ita da aka yankewa hukuncin daurin rai da rai amma zuciyar da sauran buri har wata rayuwa mai kyau take hangowa kanta),rirriqeta ta jami'an tsaron sukayi sannan suka sanya likita yazo ya danna mata allurar bacci maman na kallo,a hankali jikinta ya saki har bacci ya dauketa,kuka maman ta sanya bayan 'yan sanda sun aikata waje don basa bari ma a ga zainab din,tausayin 'yar tata kuma sai ya kamata,duk da irin tsiyar da zainab din ta shuka tun tana budurwa kawo yanzu,asirin data yiwa maman ma kusan sai da aka daureta gidan yari ya saketa, ta sani cewa maiyiwuwa zaluncin da itama ta tafka tsakanin kishiyoyi zamanin mijinsu na raye shine alhakin ke bibiyarta Allah ya sauko mata da wannan jarabawar,wato shi sharri kare ne maishi yake ba,hakana sharri dan aike ne,duk inda yaje gun wanda ya aikeshin yake dawowa.

******* ******** *******

Washegari da gyaran gidan suka tashi kasancewar 'yar aikin anty dijen itama ta tafi garinsu,babu tabbacin dawowarta ma don suna tsammani aure za'a yi mata,basu samu kansu ba sai la'sar sannan suka kammala komai,daki sumayya ta shiga tayi wanka sannan ta fito ta shirya cikin riga da zani na atamfa,ta zura hijabinta kenan zata tayar da sallah wayarta ta dauki ruri,mama ce sai ta koma bakin gado suka gaisa,sannan daga bisani ta buqaci ta kaiwa dije zasuyi magana ta kira nata layin a kashe,kiran ta katse sannan tayo falo don ta haura sama ta miqawa anty dijen wayar.
Chapter 82 · 0% Book details