Sashe 135
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummee na tsaye falon tana kintsa shi kasancewar su ke masa gyaran da kansu,sanye take da doguwar riga da hijabinta wanda sallah ta idar ta fito falon
"Bata hijabi kilishi ta sanya" cewar baabaa yana wuce bedroom dinsa,waiwayowa tayi cikin mamaki tana duban su'ad,mamakin irin ciwukan dake jikin su'ad din wanda duka kusan yanka ne,itama idanun su'ad din qyar cikin nata,wata tsanar ummen take ji,tana jin laifinta ma yafi na baabaan yawa,tunda uwarta ta gaya mata tun usuli ummeen dama bata qaunarta,bata furta komai ba kamar yadda su'ad din bata ce ba ta juya daki ta fiddo hijabin ta kawo mata,kamar wadda aka bawa kashi haka ta sanya hannu ta amsa,bata tunanin kaf rayuwarta ta taba sanya hijabi,amma ya zata yi da wannam tsohon dole ta saka don cikar burinta,yanayinta kawai da ummee ta gani ya sanya ta sake tsare gida taci gaba da aikace aikacenta,ta tabbatar akwai wata a qasa,don dama can macace da bata daukar raini a hakan baabaan ya fito.
Cikin sheshsheqar kuka bayan ya sake tambayarta ta soma magana
"Yanzu an kyauta min kenan baabaa an yimin adalci,haka akeyi bada sani na ko yarda ta ba kawai a yimin kishiya(nace hmmmm ko ta dauka a america take)?" Murmushi ya dan sake kafin yace
"Banda abinki su'ad ai ita kishiya lokaci ce,idan lokacinta yayi sai tazo ko ka yarda ko baka yarda ba,zancan sani kuma mai gidanki shine a haqqu da ya sanar da ke"
"Amma ai bakinku daya shi yasa shima bai gaya min ba,gaskiya baabaa ni dai idan ana son zaman lafiya tofa a raba auren nan,ka duba jikina baki daya daga jiya zuwa yau,nan gaba abun sai yafi haka" a nutse baabaa ya soma yi mata bayani da kwantar mata da hankali tare da bata kyawawan misalai na kishiyoyin dake zaune lafiya,ciki kuwa harda su ummee,ga zatonshi tana saurarenshi ne amma kafin ya kai qarshe sai kawai ta saki ihun kuka,miqewa ummee tayi tana tabe baki sabida baabaa ya hanata magana,ficewa tayi don ba zata iya ganin wannan iskancin ba,itama miqewar tayi
"Wallahi ni bazan zauna da shi ba" ta fada tana yage hijabin jikinta ta wurgar ta fice,miqewa baabaan yayi cikin nutsuwa ya taka a hankali yabi bayanta zuwa sashen nasu,karo na farko da ya soma zuwa sashen.
Yanayin tafiyar tasu ba daya ba,hakan ya sanya ya cimmata a falo sanda take yunqurin haurawa sama,kiran sunanta yayi tare da bata umarnin tazo ta samu waje ta zauna,kwarjini yayi mata amma da niyyarta ko 'yar harara ta banka masa,sai ta kasa haka ta dawo ta zauna din tana rusa kuka.
A hankali cikin nutsuwa ta bude qofar dakin nata ta fito,gama tilawarta kenan tana rufe alqur'anin da niyyar sake kashingida kasancewar lokacin bakwai na safe tayi sai taji kamar muryan baabaan,fuskarta qunshe da murmushi kunya da girmamawa ta qaraso inda yake tsaye,ta rusuna har qasa tana gaidashi,shi din ma fuskarsa sake take,farinciki na ratsashi ya amsa gaisuwan nata
"Yaya kwanan baqunta?" Ya tambayeta,kunya ta kamata ta sadda kanta qasa
"Maza kiramin almustapha" cewar baabaa,miqewa tayi cikin ranta tana taraddadin inda zata nufa,shahada kawai tayi ta nufi saman yayin da su'ad ta bita da kallo mai dauke da harara zuciyarta na zugi
"Banza kawai 'yar qauye" take ambatan hakan cikin zuciyarta,fata take barazanarta ta kafu cikin zukatansu,addu'a take Allah yasa almustaphan na saukowa baabaa ya sanyashi ya sallameta ta huta.
Idanu ta shiga rarrabawa tsakanin qofofin,ta tsaida idonta kan qofar da tafi kowacce fadi cikin qofofin dakunan dake saman,nan ta nufa ta sanya hannunta cikin fargaba da runtse ido ta tura qofar,tashin farko ta taka daya daga cikin kwalaben dake dakin,zafin ya ratsata har qwaqwalwarta
"Wash" ta furta wanda hakan yayi sanadiyyar dago da kanshi daga kallon dan qaramin qur'anin dake hannunshi,wanda tun bayan daya kammala sallar asubah yake tilawa duk don nemawa kanshi sauqin zugi da radadin da zuciyarsa keyi,babu shakka sai ya hukunta su'ad din hukunci mafi tsanani don gayara mata zamanta,ba'a taba nuna masa raini irin wannan ba,ya fuskanci ya sakar mata mara ne da yawa,bai fuskanci illar sakar mata din ua yayi ba kamar yadda su hamza ke nusasheshi ba sai yanzu,to ba zaya lamunci wannan iskancin ba,idan taga zata iya zama bisa doka da tsarinsa ta zauna,idan kuma ba zata iya ba tana iya yanke duk hukuncin da take so,amma tilas idan tana son zama da shi tabi dokarsa,idanunshi ya maida kan qafarta data dage sannan ya sake maidawa kan fuskarta,yaso ya share sabida yana ganin duk sune silar damuwarsa cikin satin musamman tsakanin daren jiya zuwa yau,sai kuma ya gaza daurewa kasancewarsa mutum mai tausayi,uwa uba kuma kulawar data bashi daren jiya har yau tana yawo tsakanin idanunshi
"Tsaya a nan" ya fada yana ajjiye alqur'anin hannun nashi,a hankali ya tako zuwa inda take tsaye ya duqa,yana son kama qafar saidai ya rasa ta inda zaya fara,yayin da ta runtse ido sabida zafin da take ji,a hankali ya sanya hannun shi dai fai idon sahun ta,ya sanya yatsunsa uku ya zaro ragowar kwalbar ya cillar gefe,mitsa qafar tayi da alama taji zafin haka,a hankali ya saki qafar sannan ya miqe tsaye,wanda hakan ya zamanto suna tsaye dab da juna,idamunsu suka hadu da sauri ta janye idanunta tana ja da baya saboda yadda taga yayi dab da ita,caraf taji ya kama hannunta cikin daga sauti yace
"Kula!" Ta dan tsorata,ta waiwaya baya sai taga madubi ne fasashshe dab da qafar tata saura kadan ta taka,hannun ya saki tayi qoqari tsayawa daidai
"Baabaa yana kiranka,yana jiranka a qasa" idanuwanta na qasa bashi take duba ba,sai ya gewayeta zai fice,har ya murda qofar cikin sanyin murya tace
"Ya hannun naka?" Waiwayowa yayi cikin sa suka sake hada idamu,wannan karon shi ya fara kauda kanshi,a gajarce yace
"Alhamdulillah",ya ambata yana qarasa ficewa daga dakin,maida idanunta tayi cikin dakin,mamaki ya kamata na ganin yadda dakin ya zama kamar wata bola ta gilasai,komawa tayi ta lalubi tsintsiya da paka ta soma tattare kwalaban cikin taka tsantsan da tsantseni.
Cikin lokaci qanqanin ta kwashe duka kwalaban tsakar dakin wanda ta gani,ta zuba cikin wani dan kyakkyawan kondon shara dake bayan qofa,ta dago kenan aka banko qofar wanda hakan ya sanya goshinta bugewa duk da bata wani buge sosai ba amma taji zafi,dafe wajen tayi tana dubanshi,ko baka sanshi ba kana duban fuskarshi kasan ya kai qarshe wajen fushi da bacin rai,su'ad ce biye da shi wadda dukkan hudubar da baabaan yayi musu ta bayan kunne tabi,wanda badon tsoro da tsinin idon almustapha ba saita gaggaya masa magana,biye take da shi tana ambatar sunanshi wanda ya wuce kai tsaye zuwa ma'ajiyar kayanshi ya fidda suit ash and pink ya ajjiye yana lalubar tie din da zai daura,bayanshi ta tsaya cikin kuka da masifa tace
" wallahi almustapha sai na tafi ko baka so,ba kuma zaka sake gani na ba"a wani fusace ya waiwayo yana mata kallon banza,cikin masifa tamkar wanda zai fidda garwashin wuta daga bakinsa yace
"Wa ya riqe qafafunki?,kina mafarkin ni mustapha zan tsaidaki na hanaki tafiya?,idan kinso kifi iska ko guguwa gudu,amma ina son kisan abu daya,ni muhammad almustapha kada ki damo zaton cewa zan biyo sahunki,kada ki soma mafarkin zan taka qafata muhallinku da sunan biko,zaki gane cewa ni din cikakken dan halak ne,jinin......." Da hanzari ta ajjiye fakar da tsintsiyar ta fice zuwa falon,don bata da hurumin sauraran wannan case din,yana kammala fadin haka ya ci gaba da abinda yakeyi,cikin zafi zafi ya soma shiryawa,juyawa tayi da wani irin sauri ta fice tana sakin kuka,bata taba zaton cewa ita din ba kowa bace bata kai matsayin kowa ba wajen almustaphan sai yau,ta tabbatarwa kanta sai tayi nisan da zai mance wace su'ad,ta hakanne kadai take ganin zata iya hukuntashi,yadda idanunta suka rufe ya sanya bata kula sam da sumayya ba har ta sauka qasan a gurguje tana kuka.
A gaggauce ya fito daga cikin dakim zuwa falon,jeat da shi ba qaramin kyau shigar tayi masa ba,saidai zuciyarsa a hargitse take sabanin yadda shigarshi take a tsare,inda take din ya qaraso a gaggauce,hannunshi ya sanya ya daga nata hannun wanda take dafe da goshinta saboda dan zugi zugin da yake maga,kalla yayi sannan ya saki hannun nata,hannunshi ya zura aljihunsa ya fiddo takarda da kudi ya ajjiye mata yayi gaba yana cewa
"Kada ki damu da cewa sai kin gyara dakin,ga number nan da zaki kira wanda zai kawo miki dukan abinda kike buqata,if kinason kiyi breakfast a wani waje ki kira duka za'a kaiki" ya qarashe maganar yana ficewa yayin data bishi da kallo,cikin qanqanim lokaci ta fuskanci tabbas akwai wata hargitsatstsiyar rayuwa da dangantaka cikin duniyarshi,har ga Allah taji tausayinshi ya tsarga mata,ta jima kafin ta miqa hannunta ta dauki takardar,rubutu ne a tsare wanda kana kallo kasan gwanin iya rubutu ne ya tsarashi sabanin rubutun likitoci da mafi yawa bai da kyau,ajjiye takardar tayi saman kudin ba tare data damu taga ko nawa bane,dakin ta sake komawa cikin nutsuwa ta kintsa komai ta goge ko ina,cikin qanqanin lokaci ya dawo hayyacinsa,sai rashin kayan qawa kawai da yayi.
Qarfe goma saura ra sauko,falon babu kowa,saidai tana iya jiyo motsi mai qarfi wanda yake tabbatar mata daga sashen su'ad ne,dakinta ta koma tayi wanka ta shirya cikin dinkin atamfa riga da zani plain,mai powder lipstic su kadai ta buqata,sannan ta feshe jikinta da turare,mayafi ta samu wadatacce ta yafa saman kanta wanda ya dace da shigarta ta fito matar bahaushe zam,plat din takalmi tayi amfani da shi sannan ta rufe dakin ta fice baki daga sashen.
Bangaren ummee ta nufa kai tsaye,tana gab da zata shiga ta jiyoshi
"Matar yayanmu" waiwayowa tayi fuskarta qunshe da murmushi,mahmoud ne shima dariya yake ya qaraso inda take
"Allah ya taimaki matar yaya,an tashi lpy,ni qi bansan da isowarku da gurinku zanci abincin dare" dariya yaso bata,wanne gu zaici abinci,gidan da tunda suka shigoshi zuwa yau babu cikakken nutsuwa da kwanciyar hankali,koshi mai gidan bata tsammani yasanya wani abu cikinsa daga jiya zuwa yau din,tare suka jera suka taka zuwa ciki tana amsa masa yana zolayarta.
"Bata hijabi kilishi ta sanya" cewar baabaa yana wuce bedroom dinsa,waiwayowa tayi cikin mamaki tana duban su'ad,mamakin irin ciwukan dake jikin su'ad din wanda duka kusan yanka ne,itama idanun su'ad din qyar cikin nata,wata tsanar ummen take ji,tana jin laifinta ma yafi na baabaan yawa,tunda uwarta ta gaya mata tun usuli ummeen dama bata qaunarta,bata furta komai ba kamar yadda su'ad din bata ce ba ta juya daki ta fiddo hijabin ta kawo mata,kamar wadda aka bawa kashi haka ta sanya hannu ta amsa,bata tunanin kaf rayuwarta ta taba sanya hijabi,amma ya zata yi da wannam tsohon dole ta saka don cikar burinta,yanayinta kawai da ummee ta gani ya sanya ta sake tsare gida taci gaba da aikace aikacenta,ta tabbatar akwai wata a qasa,don dama can macace da bata daukar raini a hakan baabaan ya fito.
Cikin sheshsheqar kuka bayan ya sake tambayarta ta soma magana
"Yanzu an kyauta min kenan baabaa an yimin adalci,haka akeyi bada sani na ko yarda ta ba kawai a yimin kishiya(nace hmmmm ko ta dauka a america take)?" Murmushi ya dan sake kafin yace
"Banda abinki su'ad ai ita kishiya lokaci ce,idan lokacinta yayi sai tazo ko ka yarda ko baka yarda ba,zancan sani kuma mai gidanki shine a haqqu da ya sanar da ke"
"Amma ai bakinku daya shi yasa shima bai gaya min ba,gaskiya baabaa ni dai idan ana son zaman lafiya tofa a raba auren nan,ka duba jikina baki daya daga jiya zuwa yau,nan gaba abun sai yafi haka" a nutse baabaa ya soma yi mata bayani da kwantar mata da hankali tare da bata kyawawan misalai na kishiyoyin dake zaune lafiya,ciki kuwa harda su ummee,ga zatonshi tana saurarenshi ne amma kafin ya kai qarshe sai kawai ta saki ihun kuka,miqewa ummee tayi tana tabe baki sabida baabaa ya hanata magana,ficewa tayi don ba zata iya ganin wannan iskancin ba,itama miqewar tayi
"Wallahi ni bazan zauna da shi ba" ta fada tana yage hijabin jikinta ta wurgar ta fice,miqewa baabaan yayi cikin nutsuwa ya taka a hankali yabi bayanta zuwa sashen nasu,karo na farko da ya soma zuwa sashen.
Yanayin tafiyar tasu ba daya ba,hakan ya sanya ya cimmata a falo sanda take yunqurin haurawa sama,kiran sunanta yayi tare da bata umarnin tazo ta samu waje ta zauna,kwarjini yayi mata amma da niyyarta ko 'yar harara ta banka masa,sai ta kasa haka ta dawo ta zauna din tana rusa kuka.
A hankali cikin nutsuwa ta bude qofar dakin nata ta fito,gama tilawarta kenan tana rufe alqur'anin da niyyar sake kashingida kasancewar lokacin bakwai na safe tayi sai taji kamar muryan baabaan,fuskarta qunshe da murmushi kunya da girmamawa ta qaraso inda yake tsaye,ta rusuna har qasa tana gaidashi,shi din ma fuskarsa sake take,farinciki na ratsashi ya amsa gaisuwan nata
"Yaya kwanan baqunta?" Ya tambayeta,kunya ta kamata ta sadda kanta qasa
"Maza kiramin almustapha" cewar baabaa,miqewa tayi cikin ranta tana taraddadin inda zata nufa,shahada kawai tayi ta nufi saman yayin da su'ad ta bita da kallo mai dauke da harara zuciyarta na zugi
"Banza kawai 'yar qauye" take ambatan hakan cikin zuciyarta,fata take barazanarta ta kafu cikin zukatansu,addu'a take Allah yasa almustaphan na saukowa baabaa ya sanyashi ya sallameta ta huta.
Idanu ta shiga rarrabawa tsakanin qofofin,ta tsaida idonta kan qofar da tafi kowacce fadi cikin qofofin dakunan dake saman,nan ta nufa ta sanya hannunta cikin fargaba da runtse ido ta tura qofar,tashin farko ta taka daya daga cikin kwalaben dake dakin,zafin ya ratsata har qwaqwalwarta
"Wash" ta furta wanda hakan yayi sanadiyyar dago da kanshi daga kallon dan qaramin qur'anin dake hannunshi,wanda tun bayan daya kammala sallar asubah yake tilawa duk don nemawa kanshi sauqin zugi da radadin da zuciyarsa keyi,babu shakka sai ya hukunta su'ad din hukunci mafi tsanani don gayara mata zamanta,ba'a taba nuna masa raini irin wannan ba,ya fuskanci ya sakar mata mara ne da yawa,bai fuskanci illar sakar mata din ua yayi ba kamar yadda su hamza ke nusasheshi ba sai yanzu,to ba zaya lamunci wannan iskancin ba,idan taga zata iya zama bisa doka da tsarinsa ta zauna,idan kuma ba zata iya ba tana iya yanke duk hukuncin da take so,amma tilas idan tana son zama da shi tabi dokarsa,idanunshi ya maida kan qafarta data dage sannan ya sake maidawa kan fuskarta,yaso ya share sabida yana ganin duk sune silar damuwarsa cikin satin musamman tsakanin daren jiya zuwa yau,sai kuma ya gaza daurewa kasancewarsa mutum mai tausayi,uwa uba kuma kulawar data bashi daren jiya har yau tana yawo tsakanin idanunshi
"Tsaya a nan" ya fada yana ajjiye alqur'anin hannun nashi,a hankali ya tako zuwa inda take tsaye ya duqa,yana son kama qafar saidai ya rasa ta inda zaya fara,yayin da ta runtse ido sabida zafin da take ji,a hankali ya sanya hannun shi dai fai idon sahun ta,ya sanya yatsunsa uku ya zaro ragowar kwalbar ya cillar gefe,mitsa qafar tayi da alama taji zafin haka,a hankali ya saki qafar sannan ya miqe tsaye,wanda hakan ya zamanto suna tsaye dab da juna,idamunsu suka hadu da sauri ta janye idanunta tana ja da baya saboda yadda taga yayi dab da ita,caraf taji ya kama hannunta cikin daga sauti yace
"Kula!" Ta dan tsorata,ta waiwaya baya sai taga madubi ne fasashshe dab da qafar tata saura kadan ta taka,hannun ya saki tayi qoqari tsayawa daidai
"Baabaa yana kiranka,yana jiranka a qasa" idanuwanta na qasa bashi take duba ba,sai ya gewayeta zai fice,har ya murda qofar cikin sanyin murya tace
"Ya hannun naka?" Waiwayowa yayi cikin sa suka sake hada idamu,wannan karon shi ya fara kauda kanshi,a gajarce yace
"Alhamdulillah",ya ambata yana qarasa ficewa daga dakin,maida idanunta tayi cikin dakin,mamaki ya kamata na ganin yadda dakin ya zama kamar wata bola ta gilasai,komawa tayi ta lalubi tsintsiya da paka ta soma tattare kwalaban cikin taka tsantsan da tsantseni.
Cikin lokaci qanqanin ta kwashe duka kwalaban tsakar dakin wanda ta gani,ta zuba cikin wani dan kyakkyawan kondon shara dake bayan qofa,ta dago kenan aka banko qofar wanda hakan ya sanya goshinta bugewa duk da bata wani buge sosai ba amma taji zafi,dafe wajen tayi tana dubanshi,ko baka sanshi ba kana duban fuskarshi kasan ya kai qarshe wajen fushi da bacin rai,su'ad ce biye da shi wadda dukkan hudubar da baabaan yayi musu ta bayan kunne tabi,wanda badon tsoro da tsinin idon almustapha ba saita gaggaya masa magana,biye take da shi tana ambatar sunanshi wanda ya wuce kai tsaye zuwa ma'ajiyar kayanshi ya fidda suit ash and pink ya ajjiye yana lalubar tie din da zai daura,bayanshi ta tsaya cikin kuka da masifa tace
" wallahi almustapha sai na tafi ko baka so,ba kuma zaka sake gani na ba"a wani fusace ya waiwayo yana mata kallon banza,cikin masifa tamkar wanda zai fidda garwashin wuta daga bakinsa yace
"Wa ya riqe qafafunki?,kina mafarkin ni mustapha zan tsaidaki na hanaki tafiya?,idan kinso kifi iska ko guguwa gudu,amma ina son kisan abu daya,ni muhammad almustapha kada ki damo zaton cewa zan biyo sahunki,kada ki soma mafarkin zan taka qafata muhallinku da sunan biko,zaki gane cewa ni din cikakken dan halak ne,jinin......." Da hanzari ta ajjiye fakar da tsintsiyar ta fice zuwa falon,don bata da hurumin sauraran wannan case din,yana kammala fadin haka ya ci gaba da abinda yakeyi,cikin zafi zafi ya soma shiryawa,juyawa tayi da wani irin sauri ta fice tana sakin kuka,bata taba zaton cewa ita din ba kowa bace bata kai matsayin kowa ba wajen almustaphan sai yau,ta tabbatarwa kanta sai tayi nisan da zai mance wace su'ad,ta hakanne kadai take ganin zata iya hukuntashi,yadda idanunta suka rufe ya sanya bata kula sam da sumayya ba har ta sauka qasan a gurguje tana kuka.
A gaggauce ya fito daga cikin dakim zuwa falon,jeat da shi ba qaramin kyau shigar tayi masa ba,saidai zuciyarsa a hargitse take sabanin yadda shigarshi take a tsare,inda take din ya qaraso a gaggauce,hannunshi ya sanya ya daga nata hannun wanda take dafe da goshinta saboda dan zugi zugin da yake maga,kalla yayi sannan ya saki hannun nata,hannunshi ya zura aljihunsa ya fiddo takarda da kudi ya ajjiye mata yayi gaba yana cewa
"Kada ki damu da cewa sai kin gyara dakin,ga number nan da zaki kira wanda zai kawo miki dukan abinda kike buqata,if kinason kiyi breakfast a wani waje ki kira duka za'a kaiki" ya qarashe maganar yana ficewa yayin data bishi da kallo,cikin qanqanim lokaci ta fuskanci tabbas akwai wata hargitsatstsiyar rayuwa da dangantaka cikin duniyarshi,har ga Allah taji tausayinshi ya tsarga mata,ta jima kafin ta miqa hannunta ta dauki takardar,rubutu ne a tsare wanda kana kallo kasan gwanin iya rubutu ne ya tsarashi sabanin rubutun likitoci da mafi yawa bai da kyau,ajjiye takardar tayi saman kudin ba tare data damu taga ko nawa bane,dakin ta sake komawa cikin nutsuwa ta kintsa komai ta goge ko ina,cikin qanqanin lokaci ya dawo hayyacinsa,sai rashin kayan qawa kawai da yayi.
Qarfe goma saura ra sauko,falon babu kowa,saidai tana iya jiyo motsi mai qarfi wanda yake tabbatar mata daga sashen su'ad ne,dakinta ta koma tayi wanka ta shirya cikin dinkin atamfa riga da zani plain,mai powder lipstic su kadai ta buqata,sannan ta feshe jikinta da turare,mayafi ta samu wadatacce ta yafa saman kanta wanda ya dace da shigarta ta fito matar bahaushe zam,plat din takalmi tayi amfani da shi sannan ta rufe dakin ta fice baki daga sashen.
Bangaren ummee ta nufa kai tsaye,tana gab da zata shiga ta jiyoshi
"Matar yayanmu" waiwayowa tayi fuskarta qunshe da murmushi,mahmoud ne shima dariya yake ya qaraso inda take
"Allah ya taimaki matar yaya,an tashi lpy,ni qi bansan da isowarku da gurinku zanci abincin dare" dariya yaso bata,wanne gu zaici abinci,gidan da tunda suka shigoshi zuwa yau babu cikakken nutsuwa da kwanciyar hankali,koshi mai gidan bata tsammani yasanya wani abu cikinsa daga jiya zuwa yau din,tare suka jera suka taka zuwa ciki tana amsa masa yana zolayarta.