Sashe 120
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kamar ance dubi can ta hangi mahmoud zaune saman motarsu yana jajjefa qafa yana murmushi,bisa dukkan alamu yana jin dadin yanayin,haka sauyin waje zuwa unguwar da bai santa ba bai taba zuwanta ba hakan yayi masa dai dai,idanu ta zuba sosai wai ko idanuwanta ke mata gizo,ta sake matsawa wajen,tabbas shine,daidai sanda ya waiwayo shima,baki ya bude yana mamaki
"Wa nake gani haka?,me ya kawoki unguwarnan?" Ya fada yana murmushi tare da saukowa daga saman motar
"Da gaske kai ne?,to me kake yi a kano kuma a unguwarmu a qofar gidanmu?"
"Kina nufin nam shine gidanku?" Ya fada yana nuna gidansu da yatsa
"Qwarai kuwa,nan aka haifeni"
"Malam shine aminin baabaa dama,sulen muntari?" Wannan magana ce kawai ta kasa gane me yake nufi,sai ta dubeshi tana neman qarin bayani,baisan ta yadda zai fasaara maga zancan ba sai ya dora da cewa
"Tare da baabaa prof muke fa sumayya,babanku shine tsohom aminin nan masa da yake yawan ambata,wanda ba yadda zakuyi magana da shi ta awa daya bai sako zancansa ba" ya fada yana murmushi har cikin zuciyarsa yana jim dadin yadda a yau burin mahaifinsu na tsahon shekaru ya cika,mamaki ya kamata qwarai,tabbas babu shakka zata iya tunawa ko ita yana sako mata zancansa lokaci lokaci idan hira ta dan hadasu
"Malam dinmu?,baaba yanzu yana ciki?" Duka tayi tambayar a tare lokaci guda cike da dimbin mamaki,wai babanta shine tsohon aminin baabaa prof,bugu da qari kuma wai baban ne yau a gidansu
"Qwarai kuwa,mun fito mun nasu guri ne din kinsan tsaffin abokai idan aka hadu ba dama,kada a tuno wata quruciyar aji kunya a gabanmu" ya fada cikin irin salonshi na tsokana,dariya ya basu baki daya
"Allah mai iko" sumayyan ta fada har yanzu abun nata na bata mamaki
"Bari naje na gaida babanmu" ta fada tana yunqurin wucewa
"Wannan qani na ne,shike bi mini,mus'ab dake thailand,gashi nan ku gaisa" ya fada yana dukan kafadarsa,a mutunce suka gaisa sannan ta sanya kai zuwa cikin gidan cike da zumudi da mamaki.
Sai da tayi sallama biyu aka bata izini sannan suka sanya kai cikin dakin,suna zaune irin zaman da kama dubansu kasan muhimmiyar ganawa suke,ganawa kuma mai dauke da qauna da fahimtar juna,duk da ruwa dake lemukan gaban baabaa prof babu wanda ya taba,ganin sulenshi da sauraron labaranshi ya fiye masa komai,daga kai baaban yayi cikin mamaki yana dubanta
"A'ah,mama na,daga ina haka" kanta a qasa cikin murmushi ta qarasa gabanshi ta duqa
"Baabaa,yau kaine a gidanmu?" Sai ya maida dubanshi ga sule yana fadin
"Kada dai kace min sumayya diyarka ce?" Cikin murmushi ya daga kai
"Tabbas,ita ce diya ta tabiyu,ita ce kuma ta haifamin babban jika na" kai baabaan ke dagawa,wani madaukakin farinciki na mamayarsa,tabbas Allah na sonshi,Allah na duba ga zukatan bayinsa ya musu taimako cikin ayyukan alkhairin da suka sanya gaba,a ladabce sumayya ke gaidashi da su zainab ya amsa cikin farinciki yana sanya musu albarka.
Sosai wani irin farin ciki ke shigar shi,ji yake tamkar babu wanda ya kaishi farinciki yau a duniya,mamanshi cikin zuriyyar sulenshi?,babu ko tantama Allah yana nufinsa da alkhairi,sosai yake jansu da hira abinshi,tun su zainab na dari dari na rashin sabo har suka saki jiki
"Ba don bikin da za'a yi ba shakka sai na daukeku baki daya,dama ita mama na 'yar gida ce" baabaa ya fada yana murmushi,dariya suka sa baki daya suna sake jinjina girman qaunar dake tsakanin iyayensu,sumayya ce ta janyesu tace bari su shiga ciki suma don su sake basu waje sosai,murmushi ne dauke a fuskar baabaa prof har suka fice sannan ya maida idanunsa kan malam.
"Sule,dama sumayya diyarka ce?,wannan abu ya faranta min fiye da yadda kake zato,tun sanda naga yarinyar naji ta kwanta min,na yaba da halayyarta,haka naji ina qaunarta kwatankwacin yadda nake qaunar amira,ashe jininmu ce,jinin sulenmu ce" murmushi malam keyi sannan yace
"Mai sunan inna daban take muntari cikin 'ya'yana,Allah ya yi mata baiwar ilimi hankali haquri da nutsuwa,zakayi mamaki odan na baka labarin irin rayuwar data fuskanta,da irin qaddarorin da suka fuskanceta,cikin ikon Allah ta cinye jarrabawarta,dubeta,yanzh waye zai ce ta taba fuskantar matsi da qunci makamancin haka,waye zai ce harda maraya gareta?" Dubanshi kawai baabaa keyi,don shi bai san sumayyan ta taba aure ba
"Kana nufin kace mama na ta taba aure?" Kai malam ke kadawa don tabbatar masa
"Qwarai kuwa,har da yaro" gaban baabaa na faduwa cike da faata yace
"Ina fata amma a yanzu bata da aure ko maganar wani kanta?" Cikin mamakin gambayar da muntarinsa ya masa ya amsa masa da eh,sauke ajiyar zuciya baabaa yayi yana furta
"Alhamdulillahi,sule,ko zaka iya taimakamin ka bani auren mama na?" Dubanshi yake alamun bai fahimta ba
"Ina nufin ka bani auren mama na na karbawa d'aana mustapha?" Murmushi ya subucewa malam din,amma sai ya gaza cewa komai,baaba ya dora da bayani
"Mustapha na cikin yara mafi soyuwa a wajena kamar yadda mamana take,tabbas da dan adam keda ikon tsarawa dan uwanshu rayuwa bazan zabawa almustapha rayuwan da yake yi ba a yanzu,taimako nake da buqata ka yiwa yaronka mustapha,don Allah kada a hanashi,bari na gaya maka wanne irin rayuwa mustapha keyi da iyalinshi" hankali kwance baabaan ya zayyanewa malam komai,kai kawai malam ke kadawa,shi kam bai ma tabajin rayuwar aure ta tsantsar nasaranci ba irin wannan,baiyi yawon duniya ba bare ya santa,wadda tazo cikin qur'ani da sunna da wadda akeyi cikin kowanne gida a society dinmu kawai ya sani,shi da ko karatun boko bai bari anyi a gidansa ba banda zamani daya tilastashi ya bar halima da zainab sukayi candy,
"tabbas wannan wani taimako da jihadi zakayi sule,saboda yau da gobe tafi qarfin wasa,almustapha lafiyayye ne,yana da tarin dukiya wadda tafi tawa,kai duka cikin zuriyata babu mai dukiyarshi,'yammata na qasashe daban daban na sonshi koda ba soyayyar aure ba,yana da iko da 'yancin yin komai,WA YASAN GOBE?,wa yasan gobe mai zata haifar,gwara tunda ina da ikon kawo gyara na kawowa rayuwarsa gyara ta hanya halastacciya" mamaki ke ci gaba da ratsa malam wamda ya haddasa masa kasa magana,wannan wace iriyar mace?,ita zata iya daga hannu tayi tutiyar ita din matar aure ce?,murmushi ya saki ganin yadda muntarin ya zuba mishi idanu yana jiran amsarsa,irin kallon wanda ke tsoron jin fitowar amsa mara dadi daga bakin wani
"Ba qaramar kunya ka sanya naji ha muhtari,yanzu don Allah ka cancanci ka roqeni kan neman auren mai sunan inna?,ashe ma ba daya muke ba,ashe ma yadda ka daukeni ban kai nan ba,sannan baka amince da yadda matsayinka yake a guna ba,har kwanan gobe muntarim ban sake aboki ko amini wanda nake jinsa kamar ni da shi tagwaye muke ba tunda muka rabu da kai,muhtari,ba almustapha ba,ko kai keson sumayya na baka ita halak malak bare tsatsonka,kai,ko moqocin maqocinka kesom sumayya wlh yaci albarkacinka,kana iya aurar da ita ma ba tare da na sani ba,NA BAWA ALMUSTAPHA SUMAYYA HALAK MALAK,amma wani hanzari ba gudu ba,sumayyan tayi aure ba guda daya ba har biyu harda yaro,kana ganin hakan ba matsala bace?" Kai yake kadawa
"Naji dadi sule,na gode da wannan karamcin naka,sumayya ko aure dubu tayi matuqar nace wa mustapha ina so ya aureta babu musu sai ya aureta,baaga auren budurqar ba anyi meye ne a ciki?,bazawara nada tata baiwar ta musamman kuma ta daban matuqar ta tsare mutuncin kanta tasan ciwon kanta,hankalinta da na budurwa ma kadai akwai banbanci,nasan mustapha cikin 'ya'yana,ni inda nake kokwanto mamana,kada muyi abinda zai sabawa ra'ayinta" dariya malam yayi
"Muhtari kenan,wacce maman namu?,yadda kake da tabbas kan danmu almustapha haka nake baka tabbas kan maman taka" cikin farinciki suka saki dariya dukansu,hannayensu damqe cikin juna farinciki na shawagi da su cikin duniyarshi,tamkar baabaa ya tashi ya taka rawa haka yake ji,yau Allah yayi mishi baiwa manya manya guda biyu,ko yau Allah ya dauki ranshi tabbas ya cika masa burikansa,a hankali malam ya warwarewa baabaa labarin sumayyan da irin gwagwarmayar da tasha,tausayi da qaunarta ta sake yawa a ranshi,qimarta ta dadu,tabbas wannan itace macen aure,ba shakka irin wannan matar ita ta dace da a nema,ya godewa Allah data kusa zama halak malak din familynsa,wannan shi ya sake motsa baabaa ya dubi malam
"Sule,idan zai yiwu ina son a hada auren nan da na 'yar uwarta,idan yaso bayan an daura a nutse sai ta tare ko bayan kwanaki nawa ne,ji nake kamar wannan damar zata subucewa mustapha" dariya ta subucewa malam
"Haba muhtari,tunda na bada sumayya wa almustapha duk duniya banga wanda ya isa ya maida wannan alqawarin ba,kawai ina ganin shi kansa yaron bai sani ba tunda naji kace yana can dubai wajen aikinshi,amma tunda sai kafi nutsuwa da hakan hakan za'ayi,za'a hada da zainab din in sha Allah,ubangiji ya tabbatar mana da dukkan alkhairi yasa wannan hadin ya zamo abun alfahari da farinciki wa zuri'ar ta da taka"
"Amin ya rahmanud dunya wal'aakhira" cikin madaukakin farinciki baabaa ke amsawa,shigowar mus'ab sitting room din shi ya katse sauran maganar da sukeyi,ya dan rusuna yana fadin
"Afuwa,baabaa sha daya na dare,nace ko nan zaka kwana mu mu wuce?"ya fada cikin salon tsokana,daquwa baabaan ya watsa masa
" baka gama fahimtar waye sule a gurina bane,da da hali kwanan zanyi,amma na tabbatar idan na kwana din kwanan zaune zamuyi ni da shi,don hira tsakaminmu ba mai qarewa bace,ni sai naga ma kamar daren yana gudu"dariya ya basu don babu wani gudu da dare keyi,idanuwanshi ne kawai,har bakin motarsu malam ya takowa aminin nashi masoyinshi,gab da baabaa zai shiga motar ya dubeshi
"Gobe ya kama saura sati guda kenan daurin auren ko?"
"In sha Allahu"
"To madalla,ina zaton gobe zan koma gida na sanarwa da mutanen gida muma mu fara shiri,don wancan auren da yayi ba'a qasar nan aka daura ba,hakan yasanya daidaiku ne suka je masu ikon zuwa,amma wannan karon d'aana zai auri diyata sai inda kati ya qare" dariya sukayi a tare,malam ya rufe mishi murfin motar yana mausu fatan alkhairi da fatan wayewar gari lafiya.
"Wa nake gani haka?,me ya kawoki unguwarnan?" Ya fada yana murmushi tare da saukowa daga saman motar
"Da gaske kai ne?,to me kake yi a kano kuma a unguwarmu a qofar gidanmu?"
"Kina nufin nam shine gidanku?" Ya fada yana nuna gidansu da yatsa
"Qwarai kuwa,nan aka haifeni"
"Malam shine aminin baabaa dama,sulen muntari?" Wannan magana ce kawai ta kasa gane me yake nufi,sai ta dubeshi tana neman qarin bayani,baisan ta yadda zai fasaara maga zancan ba sai ya dora da cewa
"Tare da baabaa prof muke fa sumayya,babanku shine tsohom aminin nan masa da yake yawan ambata,wanda ba yadda zakuyi magana da shi ta awa daya bai sako zancansa ba" ya fada yana murmushi har cikin zuciyarsa yana jim dadin yadda a yau burin mahaifinsu na tsahon shekaru ya cika,mamaki ya kamata qwarai,tabbas babu shakka zata iya tunawa ko ita yana sako mata zancansa lokaci lokaci idan hira ta dan hadasu
"Malam dinmu?,baaba yanzu yana ciki?" Duka tayi tambayar a tare lokaci guda cike da dimbin mamaki,wai babanta shine tsohon aminin baabaa prof,bugu da qari kuma wai baban ne yau a gidansu
"Qwarai kuwa,mun fito mun nasu guri ne din kinsan tsaffin abokai idan aka hadu ba dama,kada a tuno wata quruciyar aji kunya a gabanmu" ya fada cikin irin salonshi na tsokana,dariya ya basu baki daya
"Allah mai iko" sumayyan ta fada har yanzu abun nata na bata mamaki
"Bari naje na gaida babanmu" ta fada tana yunqurin wucewa
"Wannan qani na ne,shike bi mini,mus'ab dake thailand,gashi nan ku gaisa" ya fada yana dukan kafadarsa,a mutunce suka gaisa sannan ta sanya kai zuwa cikin gidan cike da zumudi da mamaki.
Sai da tayi sallama biyu aka bata izini sannan suka sanya kai cikin dakin,suna zaune irin zaman da kama dubansu kasan muhimmiyar ganawa suke,ganawa kuma mai dauke da qauna da fahimtar juna,duk da ruwa dake lemukan gaban baabaa prof babu wanda ya taba,ganin sulenshi da sauraron labaranshi ya fiye masa komai,daga kai baaban yayi cikin mamaki yana dubanta
"A'ah,mama na,daga ina haka" kanta a qasa cikin murmushi ta qarasa gabanshi ta duqa
"Baabaa,yau kaine a gidanmu?" Sai ya maida dubanshi ga sule yana fadin
"Kada dai kace min sumayya diyarka ce?" Cikin murmushi ya daga kai
"Tabbas,ita ce diya ta tabiyu,ita ce kuma ta haifamin babban jika na" kai baabaan ke dagawa,wani madaukakin farinciki na mamayarsa,tabbas Allah na sonshi,Allah na duba ga zukatan bayinsa ya musu taimako cikin ayyukan alkhairin da suka sanya gaba,a ladabce sumayya ke gaidashi da su zainab ya amsa cikin farinciki yana sanya musu albarka.
Sosai wani irin farin ciki ke shigar shi,ji yake tamkar babu wanda ya kaishi farinciki yau a duniya,mamanshi cikin zuriyyar sulenshi?,babu ko tantama Allah yana nufinsa da alkhairi,sosai yake jansu da hira abinshi,tun su zainab na dari dari na rashin sabo har suka saki jiki
"Ba don bikin da za'a yi ba shakka sai na daukeku baki daya,dama ita mama na 'yar gida ce" baabaa ya fada yana murmushi,dariya suka sa baki daya suna sake jinjina girman qaunar dake tsakanin iyayensu,sumayya ce ta janyesu tace bari su shiga ciki suma don su sake basu waje sosai,murmushi ne dauke a fuskar baabaa prof har suka fice sannan ya maida idanunsa kan malam.
"Sule,dama sumayya diyarka ce?,wannan abu ya faranta min fiye da yadda kake zato,tun sanda naga yarinyar naji ta kwanta min,na yaba da halayyarta,haka naji ina qaunarta kwatankwacin yadda nake qaunar amira,ashe jininmu ce,jinin sulenmu ce" murmushi malam keyi sannan yace
"Mai sunan inna daban take muntari cikin 'ya'yana,Allah ya yi mata baiwar ilimi hankali haquri da nutsuwa,zakayi mamaki odan na baka labarin irin rayuwar data fuskanta,da irin qaddarorin da suka fuskanceta,cikin ikon Allah ta cinye jarrabawarta,dubeta,yanzh waye zai ce ta taba fuskantar matsi da qunci makamancin haka,waye zai ce harda maraya gareta?" Dubanshi kawai baabaa keyi,don shi bai san sumayyan ta taba aure ba
"Kana nufin kace mama na ta taba aure?" Kai malam ke kadawa don tabbatar masa
"Qwarai kuwa,har da yaro" gaban baabaa na faduwa cike da faata yace
"Ina fata amma a yanzu bata da aure ko maganar wani kanta?" Cikin mamakin gambayar da muntarinsa ya masa ya amsa masa da eh,sauke ajiyar zuciya baabaa yayi yana furta
"Alhamdulillahi,sule,ko zaka iya taimakamin ka bani auren mama na?" Dubanshi yake alamun bai fahimta ba
"Ina nufin ka bani auren mama na na karbawa d'aana mustapha?" Murmushi ya subucewa malam din,amma sai ya gaza cewa komai,baaba ya dora da bayani
"Mustapha na cikin yara mafi soyuwa a wajena kamar yadda mamana take,tabbas da dan adam keda ikon tsarawa dan uwanshu rayuwa bazan zabawa almustapha rayuwan da yake yi ba a yanzu,taimako nake da buqata ka yiwa yaronka mustapha,don Allah kada a hanashi,bari na gaya maka wanne irin rayuwa mustapha keyi da iyalinshi" hankali kwance baabaan ya zayyanewa malam komai,kai kawai malam ke kadawa,shi kam bai ma tabajin rayuwar aure ta tsantsar nasaranci ba irin wannan,baiyi yawon duniya ba bare ya santa,wadda tazo cikin qur'ani da sunna da wadda akeyi cikin kowanne gida a society dinmu kawai ya sani,shi da ko karatun boko bai bari anyi a gidansa ba banda zamani daya tilastashi ya bar halima da zainab sukayi candy,
"tabbas wannan wani taimako da jihadi zakayi sule,saboda yau da gobe tafi qarfin wasa,almustapha lafiyayye ne,yana da tarin dukiya wadda tafi tawa,kai duka cikin zuriyata babu mai dukiyarshi,'yammata na qasashe daban daban na sonshi koda ba soyayyar aure ba,yana da iko da 'yancin yin komai,WA YASAN GOBE?,wa yasan gobe mai zata haifar,gwara tunda ina da ikon kawo gyara na kawowa rayuwarsa gyara ta hanya halastacciya" mamaki ke ci gaba da ratsa malam wamda ya haddasa masa kasa magana,wannan wace iriyar mace?,ita zata iya daga hannu tayi tutiyar ita din matar aure ce?,murmushi ya saki ganin yadda muntarin ya zuba mishi idanu yana jiran amsarsa,irin kallon wanda ke tsoron jin fitowar amsa mara dadi daga bakin wani
"Ba qaramar kunya ka sanya naji ha muhtari,yanzu don Allah ka cancanci ka roqeni kan neman auren mai sunan inna?,ashe ma ba daya muke ba,ashe ma yadda ka daukeni ban kai nan ba,sannan baka amince da yadda matsayinka yake a guna ba,har kwanan gobe muntarim ban sake aboki ko amini wanda nake jinsa kamar ni da shi tagwaye muke ba tunda muka rabu da kai,muhtari,ba almustapha ba,ko kai keson sumayya na baka ita halak malak bare tsatsonka,kai,ko moqocin maqocinka kesom sumayya wlh yaci albarkacinka,kana iya aurar da ita ma ba tare da na sani ba,NA BAWA ALMUSTAPHA SUMAYYA HALAK MALAK,amma wani hanzari ba gudu ba,sumayyan tayi aure ba guda daya ba har biyu harda yaro,kana ganin hakan ba matsala bace?" Kai yake kadawa
"Naji dadi sule,na gode da wannan karamcin naka,sumayya ko aure dubu tayi matuqar nace wa mustapha ina so ya aureta babu musu sai ya aureta,baaga auren budurqar ba anyi meye ne a ciki?,bazawara nada tata baiwar ta musamman kuma ta daban matuqar ta tsare mutuncin kanta tasan ciwon kanta,hankalinta da na budurwa ma kadai akwai banbanci,nasan mustapha cikin 'ya'yana,ni inda nake kokwanto mamana,kada muyi abinda zai sabawa ra'ayinta" dariya malam yayi
"Muhtari kenan,wacce maman namu?,yadda kake da tabbas kan danmu almustapha haka nake baka tabbas kan maman taka" cikin farinciki suka saki dariya dukansu,hannayensu damqe cikin juna farinciki na shawagi da su cikin duniyarshi,tamkar baabaa ya tashi ya taka rawa haka yake ji,yau Allah yayi mishi baiwa manya manya guda biyu,ko yau Allah ya dauki ranshi tabbas ya cika masa burikansa,a hankali malam ya warwarewa baabaa labarin sumayyan da irin gwagwarmayar da tasha,tausayi da qaunarta ta sake yawa a ranshi,qimarta ta dadu,tabbas wannan itace macen aure,ba shakka irin wannan matar ita ta dace da a nema,ya godewa Allah data kusa zama halak malak din familynsa,wannan shi ya sake motsa baabaa ya dubi malam
"Sule,idan zai yiwu ina son a hada auren nan da na 'yar uwarta,idan yaso bayan an daura a nutse sai ta tare ko bayan kwanaki nawa ne,ji nake kamar wannan damar zata subucewa mustapha" dariya ta subucewa malam
"Haba muhtari,tunda na bada sumayya wa almustapha duk duniya banga wanda ya isa ya maida wannan alqawarin ba,kawai ina ganin shi kansa yaron bai sani ba tunda naji kace yana can dubai wajen aikinshi,amma tunda sai kafi nutsuwa da hakan hakan za'ayi,za'a hada da zainab din in sha Allah,ubangiji ya tabbatar mana da dukkan alkhairi yasa wannan hadin ya zamo abun alfahari da farinciki wa zuri'ar ta da taka"
"Amin ya rahmanud dunya wal'aakhira" cikin madaukakin farinciki baabaa ke amsawa,shigowar mus'ab sitting room din shi ya katse sauran maganar da sukeyi,ya dan rusuna yana fadin
"Afuwa,baabaa sha daya na dare,nace ko nan zaka kwana mu mu wuce?"ya fada cikin salon tsokana,daquwa baabaan ya watsa masa
" baka gama fahimtar waye sule a gurina bane,da da hali kwanan zanyi,amma na tabbatar idan na kwana din kwanan zaune zamuyi ni da shi,don hira tsakaminmu ba mai qarewa bace,ni sai naga ma kamar daren yana gudu"dariya ya basu don babu wani gudu da dare keyi,idanuwanshi ne kawai,har bakin motarsu malam ya takowa aminin nashi masoyinshi,gab da baabaa zai shiga motar ya dubeshi
"Gobe ya kama saura sati guda kenan daurin auren ko?"
"In sha Allahu"
"To madalla,ina zaton gobe zan koma gida na sanarwa da mutanen gida muma mu fara shiri,don wancan auren da yayi ba'a qasar nan aka daura ba,hakan yasanya daidaiku ne suka je masu ikon zuwa,amma wannan karon d'aana zai auri diyata sai inda kati ya qare" dariya sukayi a tare,malam ya rufe mishi murfin motar yana mausu fatan alkhairi da fatan wayewar gari lafiya.