Sashe 21
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin kwanakin gaba daya mukhtar ya fita harkar fa'izan duk da cewa daman can ba shiga yake yi ba,saidai duk wani abu da yake haqqinta ne kansa yana sauke mata bakin gwargwado.
Zaman yaya yahanasu a gidan ya dauki sabon salo,wani irin zama ake a gidan,sosai yaya yahanasun kejin haushin fa'izan gami da ganin baikenta tun farko data daure gindin dan uwanta ya zama miji gareta,sai dai kuma duk da wannan bai hanata jin haushin sumayya ba,gani taje tamkar itace ta shiga tsakaninsu.
Duk kwanan duniya gari na wayewa da zarar mukhtar din ya sanya qafa ya fice itama fa'izan ke ficewa,ba zata dawo ba sai yaba gab da dawowa koda kuwa ranakun girkinta ne,sai a sannan zata tsiri girkin dare shima tsoron hukuncin mukhtar din ya hau kanta take,ba qaramin horata yayi ba lokacin da ya amshi maqullin locker din abincinsa daga hannunta ba,da rana kuwa saidai kowa tashi ta fishsheshi,shiga su jamila suke kitchen kansu tsaye su girka duk abinda suka ga dama,su din ma ba baya bane wajen iya barnar abinci da ta'adi,sam ko sau daya sumayyan bata taba daga kai ta dubesu ba bare ta gwadawa mukhtar abinda sukeyi cikin gidan,dakinta kam tuni ta sallama musu shi,ta dauke kai baki daya da shi saboda yadda suke abinda suka ga dama cikinsa,wani abun da gayya da gadara suke mata,koda bata tankasu ba sukan bude baki suce "kayan dakin da kudin dan uwansu aka sauya su" sau tari dariya abun yake bata,ta kuma godewa Allah da ya sanya iyayenta masu rufin asiri da zuciyar yiwa iyalinsu ne,suma sun san da haka,babu shakka da Allah kadai ne yasan halin da zata tsinci kanta ciki,hatta da kayan sawarta sai suka fara dauka dai dai da dai dai suna sanyawa idan zasu fita wata unguwa ko biki,ranar da mukhtar ya soma gani ransa ya baci matuqa,bai iya jurewa ba sai da ya kirasu ya musu jan kunne.
Ganin haka ya sanya mukhtar yace ta debe duk wani abu nata mai amfani ta dawo da shi dakinsa,ya bude ma'ajiyarsa ya adana mata ciki.
Fa'iza kuwa tsakaninsu da yaya yahanasun da yaran ma baki daya sai harare harare da baqar magana,wanda yawanci ma sunfi yi da jamilan ko sayyada,bata san me mukhtar ya gaya musu ba amma da alama shi ya kawo wannan dan qaramin sauyin da aka samu.
Cikin wata d'aya kacal mukhtar ya kammala musu gyaran suka tattara suka koma nasu gidan,ko a ranar da zasu tafi din ma sai da ka kusa kwata ta ranar da suka zo din,da zagi suka rabu,ba qaramin qona ran yaya yahanasun abun yayi ba ganin mukhtar din ya gaza daukar kowanne irin mataki,abinda bata sani ba shine ya fita jin takaicin abinda ke faruwar,saidai ya riga da ya tsarama ransa sai sun gama d'aukar darasin rayuwa tukunna.
*********************
Qarfe takwas na dare ya iso gida tun bayan fitar da yayi da safe sakamakon aiki da suke a shagon sa na kasuwa,sosai yake a gajiye tiqis,saidai yasan cewa abu mafi muhimmanci shine ya adana gajiyarsa,matuqar fa'iza ke da girki babu wani abu da yake iya tsinta ko ya dorar a wunin ranar baki daya,qarin gajiyarsa machine dinsa yau da ya masa tsiya ya baroshi gun bakinike ya tari adaidaita ya iso gida.
Babu wutar nepa a unguwar tasu hakan shi ya sabba ba duhun da gidan yayi,sai hasken fitila daga dakin sumayya dakin fa'iza da kuma kitchen din gidan.
Bashi da sha'awar yin tozali da fa'izar ko kadan,saboda haka ya bude dakinsa ya shige da zummar zuwa ya rage kayan jikinsa ya koma bayi ya tanadi ruwan wanka,hular kansa ya cire ya jefata saman gadonsa,ya balle maballan rigarsa ya zareta ya ajjiye sannan ya nufi window dinsa ya yaye labulen don ya bawa iska damar shigowa.
Kamar wanda aka kira idanunsa suka sauka kan kitchen,fa'iza ya hango,da farko yayi niyyar dauke kansa,saidai wani abu da ya hango shi ya ja hankalinsa,idanu ya zuba sosai don yana son ya tabbatar da abinda idanunsa ke gane masa,baiso yayi hukunci bisa kuskure zato ko tsammani.
Sakin labulen yayi sannan a hankali ya fita izuwa kitchen din cikin takun sanda,bakin window ya isa sannan ya lafe daga jikin bangon yana kallon komai tar kamar yadda idanunsa suka soma nuna masa daga cikin dakinsa,yana tsaye harta sheqe da dariya sannan tace..............
*mrs muhammad ce*
📚📚📚📚✍✍✍✍
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
1⃣9⃣
_________________________
*Bismillahir rahmamir rahim*
*ala bi zikrillahi tad'ma innul quluub*
______________________
Mamaki fal zuciyar sumayya,kanta ya daure tamau,ta kasa furta ma komai sai kallon mukhtar da takeyi,ta tabbata ba qarya ya yiwa fa'iza ba domin ba halinsa bane,amma halayyar fa'iza har ta kai haka?.
"Ina naki abincin?" Mukhtar ya tambayeta,ta katse tunaninta ta dago ta dubeshi
"Ya d'aki"
"Ki dauko,ban amince kema. a yau kici ba,ki zuba a leda ki saka a shara a zubar,shiga kitchen ki samar mana abinda zamu ci koda indomie ce sai ki hada mana da qwai" ya fada yana kashingida gami da lumshe idanunsa,tsam ta miqe ta fice don aiwatar da abinda ya umarceta.
************************
Cikin kwanakin ta dage sosai da addu'ar neman tsari,ta san tabbas shartin mutum girma gareshi,zuwa yanzu ta kuma sallama kaidin fa'iza,ta fahimci irinsu matan da suka dauki kishi ko a mutu ko ayi rai,irinsu wadanda zash iya aikata komai saboda kishi,sosai take takatsantsan kan duk wani motsi da kai kawo nata a gidan,ba ruwanta da sabgar fa'izan bare wani abu ya shiga tsakaninsu,koda fa'izan zata shekara tana takalar tashin hankali bata bi ta kanta,don ta riga ta tabbatar cewa akwai banbancin gida da kowaccensu ta fito,bai kyautu ta biye mata su zamana kamar wadanda suka fito daga gurbi guda ba.
********************
Tun da asubahin ranar suka dinga jiyo kakarin amai a tsakar gidan nasu,sumayya ta dubi mukhtar dake gefanta wanda basu jima da kammala sallar asubahin ba kasancewar sun makara basu tashi da wuri ba
"Ya mukhtar,kamar kakarin amai nake ji fa a tsakar gida" shi din ma taji amma sam bai da muradin fita,tamkar bazai tanka ba sai ya daure yace
"Eh nima naji" yaci gaba da jan carbinsa,ganin yayi shiru ya sanya ta sake cewa
"Ya mukhtar ka duba mana,inajin kamar fa'iza ce fa" shiru ya sake mata ganin hakan ya sanya itama ta tsuke bakinta tayi shiru tana ci gaba da sauraran kakarin wanda yake fita tamkar da kayan cikinta,ya kammala azkar dinsa ya haye gado abinsa ya kashingida.
Zuciyar musulunci ya sanyata ta kasa daurewa,sai ta miqe ta fidda hijabin jikinga ta nufi qofa,sanya baki yayi ya kirata tare da tambayarta ina zata
"Zanje na duba ne,bai kyautu da mutane cikin gidan ba kuma aqi fita a dubata ba,bamu san meke damunta ba" kai ya girgiza
"Dawo tausa nake so kimin"
"Kayi haquri naje na dubata din minti biyu kawai zan dawo sai na maka tausar"
"Idan ban isa da ke ba shikenan kina iya hakan" ya fada yana maida kansa ya kwantar kan pillow,sai jikinta yayi sanyi bata son saba masa ko kadan,saboda haka ta juyo a sanyaye tahaye gadon.
A tausashe take masa tausar tana leqen fuskarsa ganin yaqi kulata,har ta soma tara qwalla bata iya jure fushinsa,sai taji kawai ya birkitota ya danneta da rabin jikinsa yana dariya qasa qasa
"Raguwa kawai sarkin kuka" ya fada yana lakuce mata hanci,dariya ta saki ya shiga mata cakulkuli daga haka suja shige duniyar ma'aurata wanda hakan shi ya hanasu fitowa da wuri.
Qarfe goma ya gama shirinsa zaya fita,a tsakar gida daga can bakin qofar dakin fa'izan suka ganta zaune dirshan a qasa,ta wani wargaje can qafa can qafa tana numfashi da qyar,da sauri sumayya ta qarasa inda take tana fadin
"Hasbunallahu lafiya fa'iza?"
"Bani da lafiya" ta fada qasa qasa da qyar,ta daga kai ta kalli mukhtar da bai qaraso gun ba,yana tsaye abunsa bakin qofar dakin sumayyan yana daura agogo
"Yaya mukhtar,ko asibiti zamu?" Baice komai ba sai hannunsa da ya sanya cikin aljihun wandonsa ya zaro naira dubu biyu ya miqa mata
"Gashi sai kun dawo Allah ya kiyaye hanya" ya sanya kansa soro ya tada machine dinsa ya fice.
Tana jin rufe qofar gidan nashi ta miqe tamkar ba itace hajaran majaran ba,duk da yanayin jikinta ya nuna bata da qwari sosai,ta sakarwa sumayya harara sannan ta wafce kudin dake hannunta
"Babu inda zaki rakani munafuka" ta fada tana shigewa dakinta,kada kai sumayya tayi cikin zuciyarta tana fadin
"Allah ka shirya,wato hali zanan dutse".
Tana daki tana shafa mai bayan ta kammala wanka ta jiyo fitar fa'izan.
Suna zaune zasu ci abincin dare bayan ya kammala komai,tana gabansa tayi kyau cikin kwalliyar lace ja mai adon baqi tana zuba masa abincin data shirya musamman saboda shi fa'iza tayi sallama ta shigo dakin fuskarta qunshe da murmushi hannubta riqe da farar takarda,daya daga cikin kujerun dakin sumayyan ta samu ta zauna,fuskarsa a hade ya dubeta
" daga ina kike takwas na dare?"sai ta rausayar da ido
"Haba mana muntari,ka tsaya kaji ji da nazo maka da daddadan labari"
"Ba wannan ba ki fara amsa min tambayar da na miki tukunna"
"Kash,labarin da zan baka yanzun duka yafi wannan muhimmanci,amma tunda ka nace sai kaji to daga asibiti jikina ya rikice sai na wuce gida na kwanta acan,sai da magariba na danji dama dama" shiru yayi ya soma cin abincinsa,ganin haka ya sanya tace
"Ka godewa Allah muntari,Allah ya kusa cika maka burinka da ka dade kana fata,ka kusa zama baba,an auna ni ina da juna biyu har na wata biyu".
Qwarewa yayi da lomar abincin da ya kai bakinsa,sai ya soma tari babu qaqqautawa,cikin hanzari sumayya ta miqa masa ruwan tana jujjuya maganar cikin ranta,indai hakan gaskiya ne to ya tabbata ITACE BATA HAIHUWA?.
Sai da ya sha ruwan sosai sannan ya ajjiye cup din,hannu kawai ya miqawa fa'iza wadda keta doka murmushi tana tunanin farinciki ya sanya mukhtar qwarewa,tabbas burinta ya kusa cika,zaman sumayya cikin gidan ya kusa zuwa qarshe,ta kusa raba mukhtar da kowa sai ita.
Zaman yaya yahanasu a gidan ya dauki sabon salo,wani irin zama ake a gidan,sosai yaya yahanasun kejin haushin fa'izan gami da ganin baikenta tun farko data daure gindin dan uwanta ya zama miji gareta,sai dai kuma duk da wannan bai hanata jin haushin sumayya ba,gani taje tamkar itace ta shiga tsakaninsu.
Duk kwanan duniya gari na wayewa da zarar mukhtar din ya sanya qafa ya fice itama fa'izan ke ficewa,ba zata dawo ba sai yaba gab da dawowa koda kuwa ranakun girkinta ne,sai a sannan zata tsiri girkin dare shima tsoron hukuncin mukhtar din ya hau kanta take,ba qaramin horata yayi ba lokacin da ya amshi maqullin locker din abincinsa daga hannunta ba,da rana kuwa saidai kowa tashi ta fishsheshi,shiga su jamila suke kitchen kansu tsaye su girka duk abinda suka ga dama,su din ma ba baya bane wajen iya barnar abinci da ta'adi,sam ko sau daya sumayyan bata taba daga kai ta dubesu ba bare ta gwadawa mukhtar abinda sukeyi cikin gidan,dakinta kam tuni ta sallama musu shi,ta dauke kai baki daya da shi saboda yadda suke abinda suka ga dama cikinsa,wani abun da gayya da gadara suke mata,koda bata tankasu ba sukan bude baki suce "kayan dakin da kudin dan uwansu aka sauya su" sau tari dariya abun yake bata,ta kuma godewa Allah da ya sanya iyayenta masu rufin asiri da zuciyar yiwa iyalinsu ne,suma sun san da haka,babu shakka da Allah kadai ne yasan halin da zata tsinci kanta ciki,hatta da kayan sawarta sai suka fara dauka dai dai da dai dai suna sanyawa idan zasu fita wata unguwa ko biki,ranar da mukhtar ya soma gani ransa ya baci matuqa,bai iya jurewa ba sai da ya kirasu ya musu jan kunne.
Ganin haka ya sanya mukhtar yace ta debe duk wani abu nata mai amfani ta dawo da shi dakinsa,ya bude ma'ajiyarsa ya adana mata ciki.
Fa'iza kuwa tsakaninsu da yaya yahanasun da yaran ma baki daya sai harare harare da baqar magana,wanda yawanci ma sunfi yi da jamilan ko sayyada,bata san me mukhtar ya gaya musu ba amma da alama shi ya kawo wannan dan qaramin sauyin da aka samu.
Cikin wata d'aya kacal mukhtar ya kammala musu gyaran suka tattara suka koma nasu gidan,ko a ranar da zasu tafi din ma sai da ka kusa kwata ta ranar da suka zo din,da zagi suka rabu,ba qaramin qona ran yaya yahanasun abun yayi ba ganin mukhtar din ya gaza daukar kowanne irin mataki,abinda bata sani ba shine ya fita jin takaicin abinda ke faruwar,saidai ya riga da ya tsarama ransa sai sun gama d'aukar darasin rayuwa tukunna.
*********************
Qarfe takwas na dare ya iso gida tun bayan fitar da yayi da safe sakamakon aiki da suke a shagon sa na kasuwa,sosai yake a gajiye tiqis,saidai yasan cewa abu mafi muhimmanci shine ya adana gajiyarsa,matuqar fa'iza ke da girki babu wani abu da yake iya tsinta ko ya dorar a wunin ranar baki daya,qarin gajiyarsa machine dinsa yau da ya masa tsiya ya baroshi gun bakinike ya tari adaidaita ya iso gida.
Babu wutar nepa a unguwar tasu hakan shi ya sabba ba duhun da gidan yayi,sai hasken fitila daga dakin sumayya dakin fa'iza da kuma kitchen din gidan.
Bashi da sha'awar yin tozali da fa'izar ko kadan,saboda haka ya bude dakinsa ya shige da zummar zuwa ya rage kayan jikinsa ya koma bayi ya tanadi ruwan wanka,hular kansa ya cire ya jefata saman gadonsa,ya balle maballan rigarsa ya zareta ya ajjiye sannan ya nufi window dinsa ya yaye labulen don ya bawa iska damar shigowa.
Kamar wanda aka kira idanunsa suka sauka kan kitchen,fa'iza ya hango,da farko yayi niyyar dauke kansa,saidai wani abu da ya hango shi ya ja hankalinsa,idanu ya zuba sosai don yana son ya tabbatar da abinda idanunsa ke gane masa,baiso yayi hukunci bisa kuskure zato ko tsammani.
Sakin labulen yayi sannan a hankali ya fita izuwa kitchen din cikin takun sanda,bakin window ya isa sannan ya lafe daga jikin bangon yana kallon komai tar kamar yadda idanunsa suka soma nuna masa daga cikin dakinsa,yana tsaye harta sheqe da dariya sannan tace..............
*mrs muhammad ce*
📚📚📚📚✍✍✍✍
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
1⃣9⃣
_________________________
*Bismillahir rahmamir rahim*
*ala bi zikrillahi tad'ma innul quluub*
______________________
Mamaki fal zuciyar sumayya,kanta ya daure tamau,ta kasa furta ma komai sai kallon mukhtar da takeyi,ta tabbata ba qarya ya yiwa fa'iza ba domin ba halinsa bane,amma halayyar fa'iza har ta kai haka?.
"Ina naki abincin?" Mukhtar ya tambayeta,ta katse tunaninta ta dago ta dubeshi
"Ya d'aki"
"Ki dauko,ban amince kema. a yau kici ba,ki zuba a leda ki saka a shara a zubar,shiga kitchen ki samar mana abinda zamu ci koda indomie ce sai ki hada mana da qwai" ya fada yana kashingida gami da lumshe idanunsa,tsam ta miqe ta fice don aiwatar da abinda ya umarceta.
************************
Cikin kwanakin ta dage sosai da addu'ar neman tsari,ta san tabbas shartin mutum girma gareshi,zuwa yanzu ta kuma sallama kaidin fa'iza,ta fahimci irinsu matan da suka dauki kishi ko a mutu ko ayi rai,irinsu wadanda zash iya aikata komai saboda kishi,sosai take takatsantsan kan duk wani motsi da kai kawo nata a gidan,ba ruwanta da sabgar fa'izan bare wani abu ya shiga tsakaninsu,koda fa'izan zata shekara tana takalar tashin hankali bata bi ta kanta,don ta riga ta tabbatar cewa akwai banbancin gida da kowaccensu ta fito,bai kyautu ta biye mata su zamana kamar wadanda suka fito daga gurbi guda ba.
********************
Tun da asubahin ranar suka dinga jiyo kakarin amai a tsakar gidan nasu,sumayya ta dubi mukhtar dake gefanta wanda basu jima da kammala sallar asubahin ba kasancewar sun makara basu tashi da wuri ba
"Ya mukhtar,kamar kakarin amai nake ji fa a tsakar gida" shi din ma taji amma sam bai da muradin fita,tamkar bazai tanka ba sai ya daure yace
"Eh nima naji" yaci gaba da jan carbinsa,ganin yayi shiru ya sanya ta sake cewa
"Ya mukhtar ka duba mana,inajin kamar fa'iza ce fa" shiru ya sake mata ganin hakan ya sanya itama ta tsuke bakinta tayi shiru tana ci gaba da sauraran kakarin wanda yake fita tamkar da kayan cikinta,ya kammala azkar dinsa ya haye gado abinsa ya kashingida.
Zuciyar musulunci ya sanyata ta kasa daurewa,sai ta miqe ta fidda hijabin jikinga ta nufi qofa,sanya baki yayi ya kirata tare da tambayarta ina zata
"Zanje na duba ne,bai kyautu da mutane cikin gidan ba kuma aqi fita a dubata ba,bamu san meke damunta ba" kai ya girgiza
"Dawo tausa nake so kimin"
"Kayi haquri naje na dubata din minti biyu kawai zan dawo sai na maka tausar"
"Idan ban isa da ke ba shikenan kina iya hakan" ya fada yana maida kansa ya kwantar kan pillow,sai jikinta yayi sanyi bata son saba masa ko kadan,saboda haka ta juyo a sanyaye tahaye gadon.
A tausashe take masa tausar tana leqen fuskarsa ganin yaqi kulata,har ta soma tara qwalla bata iya jure fushinsa,sai taji kawai ya birkitota ya danneta da rabin jikinsa yana dariya qasa qasa
"Raguwa kawai sarkin kuka" ya fada yana lakuce mata hanci,dariya ta saki ya shiga mata cakulkuli daga haka suja shige duniyar ma'aurata wanda hakan shi ya hanasu fitowa da wuri.
Qarfe goma ya gama shirinsa zaya fita,a tsakar gida daga can bakin qofar dakin fa'izan suka ganta zaune dirshan a qasa,ta wani wargaje can qafa can qafa tana numfashi da qyar,da sauri sumayya ta qarasa inda take tana fadin
"Hasbunallahu lafiya fa'iza?"
"Bani da lafiya" ta fada qasa qasa da qyar,ta daga kai ta kalli mukhtar da bai qaraso gun ba,yana tsaye abunsa bakin qofar dakin sumayyan yana daura agogo
"Yaya mukhtar,ko asibiti zamu?" Baice komai ba sai hannunsa da ya sanya cikin aljihun wandonsa ya zaro naira dubu biyu ya miqa mata
"Gashi sai kun dawo Allah ya kiyaye hanya" ya sanya kansa soro ya tada machine dinsa ya fice.
Tana jin rufe qofar gidan nashi ta miqe tamkar ba itace hajaran majaran ba,duk da yanayin jikinta ya nuna bata da qwari sosai,ta sakarwa sumayya harara sannan ta wafce kudin dake hannunta
"Babu inda zaki rakani munafuka" ta fada tana shigewa dakinta,kada kai sumayya tayi cikin zuciyarta tana fadin
"Allah ka shirya,wato hali zanan dutse".
Tana daki tana shafa mai bayan ta kammala wanka ta jiyo fitar fa'izan.
Suna zaune zasu ci abincin dare bayan ya kammala komai,tana gabansa tayi kyau cikin kwalliyar lace ja mai adon baqi tana zuba masa abincin data shirya musamman saboda shi fa'iza tayi sallama ta shigo dakin fuskarta qunshe da murmushi hannubta riqe da farar takarda,daya daga cikin kujerun dakin sumayyan ta samu ta zauna,fuskarsa a hade ya dubeta
" daga ina kike takwas na dare?"sai ta rausayar da ido
"Haba mana muntari,ka tsaya kaji ji da nazo maka da daddadan labari"
"Ba wannan ba ki fara amsa min tambayar da na miki tukunna"
"Kash,labarin da zan baka yanzun duka yafi wannan muhimmanci,amma tunda ka nace sai kaji to daga asibiti jikina ya rikice sai na wuce gida na kwanta acan,sai da magariba na danji dama dama" shiru yayi ya soma cin abincinsa,ganin haka ya sanya tace
"Ka godewa Allah muntari,Allah ya kusa cika maka burinka da ka dade kana fata,ka kusa zama baba,an auna ni ina da juna biyu har na wata biyu".
Qwarewa yayi da lomar abincin da ya kai bakinsa,sai ya soma tari babu qaqqautawa,cikin hanzari sumayya ta miqa masa ruwan tana jujjuya maganar cikin ranta,indai hakan gaskiya ne to ya tabbata ITACE BATA HAIHUWA?.
Sai da ya sha ruwan sosai sannan ya ajjiye cup din,hannu kawai ya miqawa fa'iza wadda keta doka murmushi tana tunanin farinciki ya sanya mukhtar qwarewa,tabbas burinta ya kusa cika,zaman sumayya cikin gidan ya kusa zuwa qarshe,ta kusa raba mukhtar da kowa sai ita.