Sashe 43
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 7 min read
Abinda bata sani ba malam din na sane da komai,bata san da hakan ba sai ranar da aka kai kudin auren abubakar da saka rana wanda baki daya aka tsaida watanni biyu,washegarin ranar malam din yayi kiranta falonsa,bayan ya kammala duka abubuwan da yake ya dubeta
"Am sumayya,nasan cewa kinsan tsarina da al'ada ta gidan nan,sannan alhamdulillah kin san mutuncin mace dakin mijinta,baki da inda yafi nan daraja,dukkan wani abu da ya faru a baya mu ajjiyeshi gefe haka Allah ya tsarama rayuwarki,cikin KUNDIN QADDARARKI yake,babu wanda ya isa ya goge miki ko ya kautar miki da shi"
"Haka ne malam" ta fada kanta na duqe zuciyarta ba bugawa kamar zata bullo,addu'a take kada Allah yasa malam ya bullo mata da zancan da bata da buqatar jinsa a yanzu
"Sumayya,yaron nan abdur rahman yazo guna ya gabatar min da kansa a matsayin manenin aurenki,to amma kasancewarki bazawara a yanzu addini ya baki damar zabawa kanki mijin aure ya sanya nace sai na tambayeki naji mene ne ra'ayinki,kada ki zalunci kanki a yanzu kina da dama,sannan zaman aure zama ne bana yau ko gobe kawai ba,zama ne na har abada". Wani tashin hankali ne ya rikito mata,abubuwan da suka dinga faruwa da ita zamanin tana auren mukhtar tsaf suka dinga dawo mata,a hankali ta bude bakinta muryarta na rawa
"Kayi haquri malam,abdur rahman dan uwa ne ga mukhtar dan wan babansa ne nasan kasan haka malam" murmushi ya saki
"Sumayya,sumayya kenan,wannan duka ba abun damuwa bane tunda dai aure ya halasta a tsakaninku ba haramun bane" tashin hankali ta fada cikin zuciyarta,'yan uwan mukhtar fa sune dai 'yan uwan abdur rahman,ba'a canzawa tuwo suna
"Malam,ina tsoron sake kasancewa da ahalin su mukhtar...." Sai tayi shiru ta kasa qarasawa,shima shirun yayi yana nazarin maganarta,tabbas sumayya yarinya ce mai matuqar zurfin ciki,a iya zamanta na aure bazai iya fadar ranar data kawo matsalarta ba,saidai idan an fahimta a maganta mata.
"Ke kike da zabi a hannunki ai,ba zan miki auren dole ba"
"Malam,ina so abdur rahman ya janye daga qudurinsa,bana son sake shiga ahalinsu" ta fada zuciyarta na raurawa muryarta na rawa
"Shikenan zancansa ya wuce,sai ki fidda miji ina son hada aurenki da na yayanki abubakar idan ta kama har da su halima baki daya"
"Amma malam ba......."
"Sumayya,bana son qorafi ko wata magana,kinsan ba zaiyiwu kici gaba da zama a gida ba,shekara nawa,shekara daya ana gab da cika ta biyu" shuru tayi don tafi kowa sanin waye malam,amma ina mafita meye mafitarta?,
"Sumayyan luqman fa?" Taji ya jefo mata tambayar wadda ta sanya dago kanta ta dubeshi,murmushi ya kuma yi yana dubanta
"Mamaki kike yadda na sanshi?,ya fara zuwa gunki ba da izini ba ya karya doka ta,hakan ya sanya nayi bincike a kansa,na samu gamsassun bayanai a kansa,mutumin kirki ne bakin gwargwado" sai ya dan ja fasali yana dubanta kafin yaci gaba da cewa.
_yauma dai amin uziri_
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
3⃣7⃣
_____________________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wa'iza sa'a laka ibady anny fa inni qarib,ujibu da'a watad da'i iza da'aan*
*_idan bayina suka tambayeka game da ni kace ni makusanci ne(ina kusa da bayi na),ina amsa addu'ar mai addu'a idan ya roqeni_*
_______________________________
Har ta idar sallahr isha'i babu abdallah ba mukhtar,sai ta rushe sa kika ganin qarfe takwas na neman gotawa,komawa tayi ta jingina da jikin katifa tana maida numfashi tare da sakin ajiyar zuciya.
Kamar daga sama taji muryar mukhtar din kamar daga can soro suna magana da yaya abubakar,sai ta miqe zumbur ta zauna tana saurare har zuwa sanda abubakar din ya daga labulen qofar dakinta ya leqo
"Kije ki karbi abdallah,wai yau ni zaiwa rashin m yaga babansa yaqi yarda na karboshi" ya qarashe zancan yana sakin labulen,tana ji yana ma mama qorafi tana musu dariya,zumbur ta miqe kamar mai jira,dama tun hijabin da tayi sallah shine a jikinta bata cireshi ba.
A soron ta tadda su tsaye yana rungume da abdallan,tana zuwa ta miqa hannu alamar ya bata shi,banza yayi kamar bai gane me take nufi ba,ya dubeta fuskar nan a dinke tsaf
"Duk randa kika sake gigin fitowa gun bazawarinki da yaro na,idan har na tafi da shi ya tafi kenan har abada" ya qare maganan sannan ya miqa mata shi wanda tuni bacci ya fara dibansa,hannu tasa cikin azaba ta karbeshi,cikin hanzarin ta shige gida kamar wanda zaice mata dawo da shi,binsu yayi da kallo har suka shige,ya jima tsaye cikin soron ba tare da ya iya tafiya na a haka abubakar ya cimmasa sannan sukayi sallama ya tagi,har yanzu bai cimma burinsa na ganin wanda ke zuwa gun sumayyan ba,amma babu shakka ba zai guahe ba har sai ya gano waye.
Dare ya fara miqawa amma tana kwance idanunta biyu,abdallah na jikinta yana ta barcinsa,a haka halima ta daga labulen dakin ta shigo
"Yaya sumayya wani ne keta kira tun dazu yana cewa sumayya yake nema,nace masa ba ita bace amma yace ita ta bashi number din "
"Wani?" Ta tambaya cikin mamaki,don har ga Allah ta mance shaf da luqman.
"Eh,yace dazu da yamma" sai a lakacin ta tuna da shi,don baki daya abdur rahman ya hargitsa tunaninta,maganar sa ta mata girma,ga mukhtar shima da yaso hautsina ta,kafin tace komai wayar ta sake ruri,haliman ta kalleta
"Yaya gashi,shi ya sake kira" tsaki ta dan ja tana ganin baiken kanta tun farko da bata bashi lambar bogi ba,kanta ta maida kan filo sannan tace
"Kice da shi nayi bacci"
"Amma yaya....." Haliman taso yin qorafi saboda ba sabonsu bane yin qarya
"Don Allah ki fita ki bani guri ki gaya masa yadda nace din ko kisan me zaki gaya masa" ganin sumayyan ta harzuqa har haka wanda basu saba ganin hakan tattare da ita ba ya sanya ta juya ya fice ba tare data amsa wayar dake ta faman kururuwa ba.
***** ****** *******
Cikin kwanakin da suka biyo baya gaba daya haka take wuni sukuku,ga maganar abdur rahman dake mata amsa kuwwa a kai,gefe guda kuma ga luqman daya matsanta da kiran waya ba dare ba rana,duk da ko daya bata taba amsa wayarsa ba amma hakan bai sanya ta gajiya ba.
Gani take baki daya abdur rahman ta shigo da maganar ne don ya dagula lissafinta,domin shi kansa yasan yana magana ne kan abinda bashi yiwuwa,ta yaya zata aure shi bayan ta auri dan uwansa?,ta yaya zata yadda ta sake maida kanta cikin ahalin da bata da farinjini ko sau daya a gunsu?,ahalin da tasha wahala tasha jinyar zuciyarta duk a kansu,ahalin da basu ganin alkhairi tattare da ita?,duk a ture ta wannan ma yaushe zata aure musu abdur rahman?,matashin saurayin da ko auren fari baiyi ba?,sam bata jin zata iya wannan abu koda a mafarki ne ballanta na kuma a gaske.
Ranar da ta fara amsa wayarsa suna zaune ne baki dayasu a falon maman suna cin tuwon dare wayar haliman ta sake tsuwwa karo na wajen uku kenan,mama ce da ringing din wayar ya soma damu ta dubi halima
"Wai halima idan ba zaki daga wayar nan ba ki kashe ta mana haba"
"Mama bani ake kira ba yaya ake kira,yau kusan kwana hudu kenan wlh taqi ta daga ko sau daya" sai maman ta juya tana suban aumayya wadda ta cika tayi fam sabida halima ta gayawa maman
"Ke sumayya wake kiranki" cikin murya mai kama da shagwaba wanda sau tari idan ranta na bace bata aon magana haka yanayin muryarta ke komawa tace
"Wani ne nima mama ban sanshi ba"hade rai maman tayi sannan tace
"Ha'aa,baki sanshi ba kamar yaya?,ina cewa ke kika bashi lambar ko?" Dan jim tayi sannan ta gyada kai
"To maza bana son shashanci karbi ki amsa kirab,na gane take takenki sarai,kuma kinfi kowa sani malam ya fara maganar baiga kina magana da wani ba,kinsan halinshi sarai tun da can baya ma shi ba mai barin yara su girme a gabanshi bane,su kansu su halima rashin tsayayye ye ne ya sanya har suke gida iwar haka" gabanta ya fadi fargaba ta lullubeta,wani irin aure kuma?,duka duka mutuwar auren nata da bai wuce shekara biyu ba?,tilas ta karbi wayar ta miqe ta shige daki.
Sun dan dauki lokaci kan wayar yana qoqarin shigar da kansa a gunta,ba yabo ba fallasa ta amsa masa duk wata magana da yayi mata,da qyar ya shawo kanta ta bashi lambarta,yayi murna da godiya sosai tare da alqawarin zai kirata gobe,tabe baki tayi tana bin wayar da kallo bayan sun gama wayar,sai ta miqe nan saman katifa tayi kwanciyarta taqi komawa falon don koda ma mama ta sake baro wata maganar.
***** ****** ******
Kullum ta Allah baya fashin kiranta,koda kuwa bata dauka ba zai mata tex,qoqarin kafa kanshi yake sosai da gaske,duk da gaya masa ita din fa ba budurwa bace har da yaronta,yace babu komai shi hakan ma yake so,a haka har sati dayan da abdur rahman ya diba mata ya cika,satin guda cif bai sake nemanta ko takowa gidan ba har cikar wa'adin kwanakin.
Tun safe take addu'ar kada Allah ya dawo da shi,a haka har lokacin tafiya makaranta yayi ta shirya ta tafi tare da abdallah wanda yau ya tubure sai ya bita.
"Am sumayya,nasan cewa kinsan tsarina da al'ada ta gidan nan,sannan alhamdulillah kin san mutuncin mace dakin mijinta,baki da inda yafi nan daraja,dukkan wani abu da ya faru a baya mu ajjiyeshi gefe haka Allah ya tsarama rayuwarki,cikin KUNDIN QADDARARKI yake,babu wanda ya isa ya goge miki ko ya kautar miki da shi"
"Haka ne malam" ta fada kanta na duqe zuciyarta ba bugawa kamar zata bullo,addu'a take kada Allah yasa malam ya bullo mata da zancan da bata da buqatar jinsa a yanzu
"Sumayya,yaron nan abdur rahman yazo guna ya gabatar min da kansa a matsayin manenin aurenki,to amma kasancewarki bazawara a yanzu addini ya baki damar zabawa kanki mijin aure ya sanya nace sai na tambayeki naji mene ne ra'ayinki,kada ki zalunci kanki a yanzu kina da dama,sannan zaman aure zama ne bana yau ko gobe kawai ba,zama ne na har abada". Wani tashin hankali ne ya rikito mata,abubuwan da suka dinga faruwa da ita zamanin tana auren mukhtar tsaf suka dinga dawo mata,a hankali ta bude bakinta muryarta na rawa
"Kayi haquri malam,abdur rahman dan uwa ne ga mukhtar dan wan babansa ne nasan kasan haka malam" murmushi ya saki
"Sumayya,sumayya kenan,wannan duka ba abun damuwa bane tunda dai aure ya halasta a tsakaninku ba haramun bane" tashin hankali ta fada cikin zuciyarta,'yan uwan mukhtar fa sune dai 'yan uwan abdur rahman,ba'a canzawa tuwo suna
"Malam,ina tsoron sake kasancewa da ahalin su mukhtar...." Sai tayi shiru ta kasa qarasawa,shima shirun yayi yana nazarin maganarta,tabbas sumayya yarinya ce mai matuqar zurfin ciki,a iya zamanta na aure bazai iya fadar ranar data kawo matsalarta ba,saidai idan an fahimta a maganta mata.
"Ke kike da zabi a hannunki ai,ba zan miki auren dole ba"
"Malam,ina so abdur rahman ya janye daga qudurinsa,bana son sake shiga ahalinsu" ta fada zuciyarta na raurawa muryarta na rawa
"Shikenan zancansa ya wuce,sai ki fidda miji ina son hada aurenki da na yayanki abubakar idan ta kama har da su halima baki daya"
"Amma malam ba......."
"Sumayya,bana son qorafi ko wata magana,kinsan ba zaiyiwu kici gaba da zama a gida ba,shekara nawa,shekara daya ana gab da cika ta biyu" shuru tayi don tafi kowa sanin waye malam,amma ina mafita meye mafitarta?,
"Sumayyan luqman fa?" Taji ya jefo mata tambayar wadda ta sanya dago kanta ta dubeshi,murmushi ya kuma yi yana dubanta
"Mamaki kike yadda na sanshi?,ya fara zuwa gunki ba da izini ba ya karya doka ta,hakan ya sanya nayi bincike a kansa,na samu gamsassun bayanai a kansa,mutumin kirki ne bakin gwargwado" sai ya dan ja fasali yana dubanta kafin yaci gaba da cewa.
_yauma dai amin uziri_
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
3⃣7⃣
_____________________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wa'iza sa'a laka ibady anny fa inni qarib,ujibu da'a watad da'i iza da'aan*
*_idan bayina suka tambayeka game da ni kace ni makusanci ne(ina kusa da bayi na),ina amsa addu'ar mai addu'a idan ya roqeni_*
_______________________________
Har ta idar sallahr isha'i babu abdallah ba mukhtar,sai ta rushe sa kika ganin qarfe takwas na neman gotawa,komawa tayi ta jingina da jikin katifa tana maida numfashi tare da sakin ajiyar zuciya.
Kamar daga sama taji muryar mukhtar din kamar daga can soro suna magana da yaya abubakar,sai ta miqe zumbur ta zauna tana saurare har zuwa sanda abubakar din ya daga labulen qofar dakinta ya leqo
"Kije ki karbi abdallah,wai yau ni zaiwa rashin m yaga babansa yaqi yarda na karboshi" ya qarashe zancan yana sakin labulen,tana ji yana ma mama qorafi tana musu dariya,zumbur ta miqe kamar mai jira,dama tun hijabin da tayi sallah shine a jikinta bata cireshi ba.
A soron ta tadda su tsaye yana rungume da abdallan,tana zuwa ta miqa hannu alamar ya bata shi,banza yayi kamar bai gane me take nufi ba,ya dubeta fuskar nan a dinke tsaf
"Duk randa kika sake gigin fitowa gun bazawarinki da yaro na,idan har na tafi da shi ya tafi kenan har abada" ya qare maganan sannan ya miqa mata shi wanda tuni bacci ya fara dibansa,hannu tasa cikin azaba ta karbeshi,cikin hanzarin ta shige gida kamar wanda zaice mata dawo da shi,binsu yayi da kallo har suka shige,ya jima tsaye cikin soron ba tare da ya iya tafiya na a haka abubakar ya cimmasa sannan sukayi sallama ya tagi,har yanzu bai cimma burinsa na ganin wanda ke zuwa gun sumayyan ba,amma babu shakka ba zai guahe ba har sai ya gano waye.
Dare ya fara miqawa amma tana kwance idanunta biyu,abdallah na jikinta yana ta barcinsa,a haka halima ta daga labulen dakin ta shigo
"Yaya sumayya wani ne keta kira tun dazu yana cewa sumayya yake nema,nace masa ba ita bace amma yace ita ta bashi number din "
"Wani?" Ta tambaya cikin mamaki,don har ga Allah ta mance shaf da luqman.
"Eh,yace dazu da yamma" sai a lakacin ta tuna da shi,don baki daya abdur rahman ya hargitsa tunaninta,maganar sa ta mata girma,ga mukhtar shima da yaso hautsina ta,kafin tace komai wayar ta sake ruri,haliman ta kalleta
"Yaya gashi,shi ya sake kira" tsaki ta dan ja tana ganin baiken kanta tun farko da bata bashi lambar bogi ba,kanta ta maida kan filo sannan tace
"Kice da shi nayi bacci"
"Amma yaya....." Haliman taso yin qorafi saboda ba sabonsu bane yin qarya
"Don Allah ki fita ki bani guri ki gaya masa yadda nace din ko kisan me zaki gaya masa" ganin sumayyan ta harzuqa har haka wanda basu saba ganin hakan tattare da ita ba ya sanya ta juya ya fice ba tare data amsa wayar dake ta faman kururuwa ba.
***** ****** *******
Cikin kwanakin da suka biyo baya gaba daya haka take wuni sukuku,ga maganar abdur rahman dake mata amsa kuwwa a kai,gefe guda kuma ga luqman daya matsanta da kiran waya ba dare ba rana,duk da ko daya bata taba amsa wayarsa ba amma hakan bai sanya ta gajiya ba.
Gani take baki daya abdur rahman ta shigo da maganar ne don ya dagula lissafinta,domin shi kansa yasan yana magana ne kan abinda bashi yiwuwa,ta yaya zata aure shi bayan ta auri dan uwansa?,ta yaya zata yadda ta sake maida kanta cikin ahalin da bata da farinjini ko sau daya a gunsu?,ahalin da tasha wahala tasha jinyar zuciyarta duk a kansu,ahalin da basu ganin alkhairi tattare da ita?,duk a ture ta wannan ma yaushe zata aure musu abdur rahman?,matashin saurayin da ko auren fari baiyi ba?,sam bata jin zata iya wannan abu koda a mafarki ne ballanta na kuma a gaske.
Ranar da ta fara amsa wayarsa suna zaune ne baki dayasu a falon maman suna cin tuwon dare wayar haliman ta sake tsuwwa karo na wajen uku kenan,mama ce da ringing din wayar ya soma damu ta dubi halima
"Wai halima idan ba zaki daga wayar nan ba ki kashe ta mana haba"
"Mama bani ake kira ba yaya ake kira,yau kusan kwana hudu kenan wlh taqi ta daga ko sau daya" sai maman ta juya tana suban aumayya wadda ta cika tayi fam sabida halima ta gayawa maman
"Ke sumayya wake kiranki" cikin murya mai kama da shagwaba wanda sau tari idan ranta na bace bata aon magana haka yanayin muryarta ke komawa tace
"Wani ne nima mama ban sanshi ba"hade rai maman tayi sannan tace
"Ha'aa,baki sanshi ba kamar yaya?,ina cewa ke kika bashi lambar ko?" Dan jim tayi sannan ta gyada kai
"To maza bana son shashanci karbi ki amsa kirab,na gane take takenki sarai,kuma kinfi kowa sani malam ya fara maganar baiga kina magana da wani ba,kinsan halinshi sarai tun da can baya ma shi ba mai barin yara su girme a gabanshi bane,su kansu su halima rashin tsayayye ye ne ya sanya har suke gida iwar haka" gabanta ya fadi fargaba ta lullubeta,wani irin aure kuma?,duka duka mutuwar auren nata da bai wuce shekara biyu ba?,tilas ta karbi wayar ta miqe ta shige daki.
Sun dan dauki lokaci kan wayar yana qoqarin shigar da kansa a gunta,ba yabo ba fallasa ta amsa masa duk wata magana da yayi mata,da qyar ya shawo kanta ta bashi lambarta,yayi murna da godiya sosai tare da alqawarin zai kirata gobe,tabe baki tayi tana bin wayar da kallo bayan sun gama wayar,sai ta miqe nan saman katifa tayi kwanciyarta taqi komawa falon don koda ma mama ta sake baro wata maganar.
***** ****** ******
Kullum ta Allah baya fashin kiranta,koda kuwa bata dauka ba zai mata tex,qoqarin kafa kanshi yake sosai da gaske,duk da gaya masa ita din fa ba budurwa bace har da yaronta,yace babu komai shi hakan ma yake so,a haka har sati dayan da abdur rahman ya diba mata ya cika,satin guda cif bai sake nemanta ko takowa gidan ba har cikar wa'adin kwanakin.
Tun safe take addu'ar kada Allah ya dawo da shi,a haka har lokacin tafiya makaranta yayi ta shirya ta tafi tare da abdallah wanda yau ya tubure sai ya bita.