Sashe 65
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 7 min read
Cikin sassanyar murya tayi sallama a falon nasa,da abdallah idanunta suka soma tozali,ko kadan batayi tsammanin ganinsa a lokacin ba shi ko mahaifinsa,ai da gudu ya baro jikin mukhtar din ya iso inda take tsaye ya riqeta yana kiran amma na,jikinta da zuciyarta baki daya a raunane suke,hakan ya sanyata zubewa shima ya fado jikinta,sai ta rungumeshi a jikinta tayi qas da kanta hawaye ya balle mata a boye,cikin dabara take shareshi.
"Sumayya" taji malam ya kirata
"Na'am" ta amsa murya a sarqe
"Ga mukhtar nan yazo neman gafararki kan abunda ya faru tsakaninki da shi a baya,wanda mu nasan ya riga da ya wuce a gunmu saidai tsakaninku dai" ya fada yana miqe ya fice ya turo halima ta zauna da su tunda ya sani a lokacin bai halatta ya barsu su kebe ba,har a sannan tana matsayin matar lukman har zuwa sanda ta kammala idda.
Dauke idanunsa yayi da sauri daga kanta saboda tunawa da yayi matar wani ce,rabonsa da ya sanyata a idanunsa ya mance,tun kafin aurenta.
"Sumayya,nazo gareki a matsayina na mutum mai tarin laifi,a matsayina na mutumin da yafi kowa laifi duk duniya a gurinki,nasan cewa kalmomina basu isa su haqurqurtar da ke kan abinda na aikata a gareki ba cikin jahilci,gaggawa da yanke hukunci cikin rashin bincike,tun ranar da na san gaskiyar lamarin naso neman gafararki amma hakan bazai yiwu ba saboda kina gidan wani,yanzun ma mama da malam mazo sanarwa ya gayan kina kusa,don girman Allah sumayya na roqeki ki yafemin,koda kuwa wannan ne alfarma na qarshe da zakiyimin,babu shakka zainab ta zalunce ni ta zalunceki ta kuma zalunci danmu,kimin afuwa don Allah" tsam ta miqe ba tare da tace komai ba ta dauki abdallah ta fice daga falon,sai yayi qasa da kansa zuciyarsa na masa zafi,yayin da nauyi ya kama halima,sai ta miqe tabi bayan sumayya itama.
Ranar bacci barawo ne kawai ya dauketa,zafi goma da ashirin ke bugun zuciyarta,ta duba ta laluba kaf rayuwar aurenta babu wanda ya ruguza farincikinta sai mata 'yan uwanta,babu abinda ta aikata musu don kawai sun hada miji?,me yasa kishiya ta zame mata qalubale cikin rayuwarta baki daya?.
Sannu kwanaki suka dinga hada satittika,satittika suka hadu suka bada watanni,ta miqawa Allah dukkan lamarinta baki daya,ta yadda babu bawan da ya isa ya gujewa qaddararsa,watanni uku cif cif iddarta ta cika,ta godewa Allah bisa baiwa da ni'inar lafiya da ya bata,ta watsar da dukkan wani abu ta rungumi rayuwarta,riqon Abdallah ya dawo wajenta,hakanan taci gaba da makarantarta na koyon sana'o'i,wanda zuwa lokacin ta qware sosai wajen iya humra kwalakca da turaren daki na kaya da na tsuguno,ya abbakar shi ya bata jari ta soma gwadawa,Allah kuwa ya sanyawa abun albarka don ciniki take sosai,don kana shigowa gidansu zakasan ana saida humra balle kuma jikinta,nutsuwa sosai ta sake zuwa mata,wani girma da hankali na musamman ya soma gameta,mukhtar kuwa har yau bata yarda ta sake ganinsa ba ma bare ya dagula mata lissafi.
**** ***** ****** *****
Qarfe bakwai na bayan sallar magariba ta gangaro cikin layinsu abdallah na sabe a kafadarta,tun daga makaranta ta wuce gidan anty maryam qanwar mama sai gab da magariba ta fito.
Tana gab da gidan nasu ta kula da motar wadda ko daga bacci ta tashi zata iya ganeta,motar mukhtar ce,sai ta dauke kai tana qoqarin wucewa cikin gidan,saidai abdallah dake kafadarta wanda ya soma zillo ganin babansa yaqi bada hadin kai,tilas taja tunga ta saukeshi da niyyar ta wuce ta barshi a gun,saidai tana dagowa daga durquson da tayi ta tsinci mukhtar din tsaye a gabanta
"Zan wuce malam" ta fada ranta a hade
"Kiyi haquri malama" ya fada da irin salon muryarta,kicin kicin tayi ganin yadda yake son maida lamarin wasa
"Ka bani hanya da Allah kana batamin lokaci bana son shirme" tsit yayi yana kallonta,ita kanta sai taji kalma ta mata nauyi,don haka ta basar ta hanyar gyara hannun hijabinta
"Sumayya" ya kirata da wani irin salo wanda ada can yake kiranta da shi,kira ke da idan yayi mata take jinsa har cikin jikinta
"Ki yafemim sumayya,a kullum tsahon wata biyar kenan cikin neman yafiyarki nake,idan na kira baki dauka,idan nayi miki saqo baki reply,kiyi haquri ki yafemin,na yadda nayi babban kuskure a rayuwata amma na girbe abinda na shuka ai,na rasaki na tsahon wasu shekaru,ban taba tunani a baya akwai abin zai rabani da ke ba idan ba mutuwa ba,tunda na rabu da ke sumayya ban taba samun nutsuwa ta minti guda ba,Allah ya hukuntani tunda har kin shiga gidan wani sumayya,ki zama mai afuwa da yafiya kamar yadda na sanki nasam halinki a baya,mukhtar dinki ne sumayya bazan daina neman yafiyarki ba matuqar baki yafemim ba har sai ranar da numfashina ya bar gangar jikina...."da sauri ta katseshi don yana neman karya mata zuciya
" don Allah ka bani hanya,na gaji da jin kalaman bakinka"murmushi ya saka yana kada kai
"Shikenam sumayya,idan kinso ma ba zaki sake gani na ba tunda haka kika buqata,amma bazan daina neman afuwarki ba,na barki lafiya"ya fada yana juyawa ya danqawa Abdallah wani dan madaidaicin kwali ya wuce motarsa,sai ta samu kanta da tsayawa cak a gun ta kasa tafiya har ya bar layin,tausayinsa nason rinjayar zuciyarta,tuna wahalhalun da tasha shi ya bijiro mata ya taurarar da zuciyarta,kama hannun abdallah tayi suka shige ciki.
***** ****** ******
Tunda ya bar gidan yaso tilastawa kansa cireta daga zuciyarsa saidai ya gaza hakan,wata sabuwar soyayya da qaunarta ke yawo ko ina cikin jinin jikinsa fiye da irin qaunarta da yake ji a da,sai ya soma komawa wani iri,ko da yaushe cikin tunani,ga wani matsanancin ciwon kai dake matsanta masa wanda ke kwantar da shi,yana mamakin yadda ya kasa haqura da ita,ji yake tamkar idan ya haqura da ita din zai rasa numfashinsa,hakan ya sanya ya shirya da kansa wani dare bayan ya yiwa abbakar waya ya sanar masa ya gayawa malam zaizo zasu tattauna,idan da hali abubakar din ma ya zauna.
Qarfe takwas yana sitring room din malam din dake qofar gidansu,hakan ne ya sanya babu wanda yasan da zuwansa a cikin gidan
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:45] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
4⃣6⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wa yuhazzirikumul lahu nafsah*
*_Allah yana tsoratar da ku game da kansa_*
_______________________________
Duk yadda ta kai ga tunanin duniyar gidanta zata sameta yadda takeso ba haka abun yazo mata ba,komai na neman lalace mata bayan ta tabbatar da cewa tayi nasarar tuge sumayya daga gidan,gaba daya yaranta yadda ta sansu a yanzu ba haka suke ba,baki dayansu kansu a hade yake,qarami na girmama babba,haka babba na tausayin qarami,nuwaira na cikinsu tamkar cikinsu daya da ita,ita ke jagorancin ragamar sauran a matsayinta na babba,duk yadda taso ga sake raba kansu abun yaci tura,duka ne a yanzu basa tsoron dukanta,da tayi abu zasu ce mama babu kyau fa abu kaza,ko daya daga cikin tarbiyyar da sumayya ta dorasu babu wadda suka watsar,a yanzu haka sunfi qaunar zama wajen hajiya akan wurinta,saboda babu abinda ke shiga tsakaninsu sai duka hantara da tsawa saboda basa mata yadda takeso,babu mai bin umarninta cikinsu matuqar ba kan dai dai bane hatta da qaramarsu basma,bata fuskanci sumayya ta gama da rayuwar gidanta ba sai da yaran suka dinga gudunta,idan ranar makaranta ne ba zata sanyasu a idanunta ba sai dare,don idan suka dawo daga boko don kada ta hanasu zuwa uslamiyya gun hajiya suke togewa su shirya su wuce abinsu,ranakun qarshen mako kuwa gun hajiyar suke wuni,idan ka gansu a bangarensu to wani abu suka zo yi suyi su sake komawa.
Lukman kuwa mallakar data yi masa sai ra soma damunta,ba irinta take buqata daga gunsa ba,ya zama kamar irin dolayen nan,komai tace sai yace to,ya zama kamar qaramin yaro,hatta wanka da cin abinci sai tace yayi,sai ya zame mata qarin nauyi cikim rayuwarta,bashi da wani tunani ko kadan,ko wuta tace ya sanya hannunsa ba musu zai tsumbula,abinda ta fuskanta har yau sumayya na maqale cikin zuciyarsa,sau tari zai zauna ya yita kallon qofar dakinta babu qaqqautawa har sai tazo ta koreshi,hakanan ko sunan sumayya yaji an kira koda a hanya ne sai yayi firgigit kamar wanda aka tasa daga bacci,idan kuwa su nuwaira na zaune suna hirarta sai ya zauna daga gefansu yana saurararsu yana tambayarsu kan wasu abubuwa ko sanya musu baki,a kan hirarta da suke zama suyi sai da karima ta tara su ta musu dukan tsiya,ta kulle nuwaira kuma a daki sai da hajiya ta shigo taci mata mutunci ta bude ta tace kada kuma ta sake dukar mata jikoki itace abar a daka ai basu ba,nan ta saki baki ta dinga caccabawa hajiyan magana,bata bu ta kanta ba ta kada kan jikokinta suka fice.
Wannan shine halin da karima ke ciki.
******* ******* ********
"Sumayya" taji malam ya kirata
"Na'am" ta amsa murya a sarqe
"Ga mukhtar nan yazo neman gafararki kan abunda ya faru tsakaninki da shi a baya,wanda mu nasan ya riga da ya wuce a gunmu saidai tsakaninku dai" ya fada yana miqe ya fice ya turo halima ta zauna da su tunda ya sani a lokacin bai halatta ya barsu su kebe ba,har a sannan tana matsayin matar lukman har zuwa sanda ta kammala idda.
Dauke idanunsa yayi da sauri daga kanta saboda tunawa da yayi matar wani ce,rabonsa da ya sanyata a idanunsa ya mance,tun kafin aurenta.
"Sumayya,nazo gareki a matsayina na mutum mai tarin laifi,a matsayina na mutumin da yafi kowa laifi duk duniya a gurinki,nasan cewa kalmomina basu isa su haqurqurtar da ke kan abinda na aikata a gareki ba cikin jahilci,gaggawa da yanke hukunci cikin rashin bincike,tun ranar da na san gaskiyar lamarin naso neman gafararki amma hakan bazai yiwu ba saboda kina gidan wani,yanzun ma mama da malam mazo sanarwa ya gayan kina kusa,don girman Allah sumayya na roqeki ki yafemin,koda kuwa wannan ne alfarma na qarshe da zakiyimin,babu shakka zainab ta zalunce ni ta zalunceki ta kuma zalunci danmu,kimin afuwa don Allah" tsam ta miqe ba tare da tace komai ba ta dauki abdallah ta fice daga falon,sai yayi qasa da kansa zuciyarsa na masa zafi,yayin da nauyi ya kama halima,sai ta miqe tabi bayan sumayya itama.
Ranar bacci barawo ne kawai ya dauketa,zafi goma da ashirin ke bugun zuciyarta,ta duba ta laluba kaf rayuwar aurenta babu wanda ya ruguza farincikinta sai mata 'yan uwanta,babu abinda ta aikata musu don kawai sun hada miji?,me yasa kishiya ta zame mata qalubale cikin rayuwarta baki daya?.
Sannu kwanaki suka dinga hada satittika,satittika suka hadu suka bada watanni,ta miqawa Allah dukkan lamarinta baki daya,ta yadda babu bawan da ya isa ya gujewa qaddararsa,watanni uku cif cif iddarta ta cika,ta godewa Allah bisa baiwa da ni'inar lafiya da ya bata,ta watsar da dukkan wani abu ta rungumi rayuwarta,riqon Abdallah ya dawo wajenta,hakanan taci gaba da makarantarta na koyon sana'o'i,wanda zuwa lokacin ta qware sosai wajen iya humra kwalakca da turaren daki na kaya da na tsuguno,ya abbakar shi ya bata jari ta soma gwadawa,Allah kuwa ya sanyawa abun albarka don ciniki take sosai,don kana shigowa gidansu zakasan ana saida humra balle kuma jikinta,nutsuwa sosai ta sake zuwa mata,wani girma da hankali na musamman ya soma gameta,mukhtar kuwa har yau bata yarda ta sake ganinsa ba ma bare ya dagula mata lissafi.
**** ***** ****** *****
Qarfe bakwai na bayan sallar magariba ta gangaro cikin layinsu abdallah na sabe a kafadarta,tun daga makaranta ta wuce gidan anty maryam qanwar mama sai gab da magariba ta fito.
Tana gab da gidan nasu ta kula da motar wadda ko daga bacci ta tashi zata iya ganeta,motar mukhtar ce,sai ta dauke kai tana qoqarin wucewa cikin gidan,saidai abdallah dake kafadarta wanda ya soma zillo ganin babansa yaqi bada hadin kai,tilas taja tunga ta saukeshi da niyyar ta wuce ta barshi a gun,saidai tana dagowa daga durquson da tayi ta tsinci mukhtar din tsaye a gabanta
"Zan wuce malam" ta fada ranta a hade
"Kiyi haquri malama" ya fada da irin salon muryarta,kicin kicin tayi ganin yadda yake son maida lamarin wasa
"Ka bani hanya da Allah kana batamin lokaci bana son shirme" tsit yayi yana kallonta,ita kanta sai taji kalma ta mata nauyi,don haka ta basar ta hanyar gyara hannun hijabinta
"Sumayya" ya kirata da wani irin salo wanda ada can yake kiranta da shi,kira ke da idan yayi mata take jinsa har cikin jikinta
"Ki yafemim sumayya,a kullum tsahon wata biyar kenan cikin neman yafiyarki nake,idan na kira baki dauka,idan nayi miki saqo baki reply,kiyi haquri ki yafemin,na yadda nayi babban kuskure a rayuwata amma na girbe abinda na shuka ai,na rasaki na tsahon wasu shekaru,ban taba tunani a baya akwai abin zai rabani da ke ba idan ba mutuwa ba,tunda na rabu da ke sumayya ban taba samun nutsuwa ta minti guda ba,Allah ya hukuntani tunda har kin shiga gidan wani sumayya,ki zama mai afuwa da yafiya kamar yadda na sanki nasam halinki a baya,mukhtar dinki ne sumayya bazan daina neman yafiyarki ba matuqar baki yafemim ba har sai ranar da numfashina ya bar gangar jikina...."da sauri ta katseshi don yana neman karya mata zuciya
" don Allah ka bani hanya,na gaji da jin kalaman bakinka"murmushi ya saka yana kada kai
"Shikenam sumayya,idan kinso ma ba zaki sake gani na ba tunda haka kika buqata,amma bazan daina neman afuwarki ba,na barki lafiya"ya fada yana juyawa ya danqawa Abdallah wani dan madaidaicin kwali ya wuce motarsa,sai ta samu kanta da tsayawa cak a gun ta kasa tafiya har ya bar layin,tausayinsa nason rinjayar zuciyarta,tuna wahalhalun da tasha shi ya bijiro mata ya taurarar da zuciyarta,kama hannun abdallah tayi suka shige ciki.
***** ****** ******
Tunda ya bar gidan yaso tilastawa kansa cireta daga zuciyarsa saidai ya gaza hakan,wata sabuwar soyayya da qaunarta ke yawo ko ina cikin jinin jikinsa fiye da irin qaunarta da yake ji a da,sai ya soma komawa wani iri,ko da yaushe cikin tunani,ga wani matsanancin ciwon kai dake matsanta masa wanda ke kwantar da shi,yana mamakin yadda ya kasa haqura da ita,ji yake tamkar idan ya haqura da ita din zai rasa numfashinsa,hakan ya sanya ya shirya da kansa wani dare bayan ya yiwa abbakar waya ya sanar masa ya gayawa malam zaizo zasu tattauna,idan da hali abubakar din ma ya zauna.
Qarfe takwas yana sitring room din malam din dake qofar gidansu,hakan ne ya sanya babu wanda yasan da zuwansa a cikin gidan
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:45] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
4⃣6⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wa yuhazzirikumul lahu nafsah*
*_Allah yana tsoratar da ku game da kansa_*
_______________________________
Duk yadda ta kai ga tunanin duniyar gidanta zata sameta yadda takeso ba haka abun yazo mata ba,komai na neman lalace mata bayan ta tabbatar da cewa tayi nasarar tuge sumayya daga gidan,gaba daya yaranta yadda ta sansu a yanzu ba haka suke ba,baki dayansu kansu a hade yake,qarami na girmama babba,haka babba na tausayin qarami,nuwaira na cikinsu tamkar cikinsu daya da ita,ita ke jagorancin ragamar sauran a matsayinta na babba,duk yadda taso ga sake raba kansu abun yaci tura,duka ne a yanzu basa tsoron dukanta,da tayi abu zasu ce mama babu kyau fa abu kaza,ko daya daga cikin tarbiyyar da sumayya ta dorasu babu wadda suka watsar,a yanzu haka sunfi qaunar zama wajen hajiya akan wurinta,saboda babu abinda ke shiga tsakaninsu sai duka hantara da tsawa saboda basa mata yadda takeso,babu mai bin umarninta cikinsu matuqar ba kan dai dai bane hatta da qaramarsu basma,bata fuskanci sumayya ta gama da rayuwar gidanta ba sai da yaran suka dinga gudunta,idan ranar makaranta ne ba zata sanyasu a idanunta ba sai dare,don idan suka dawo daga boko don kada ta hanasu zuwa uslamiyya gun hajiya suke togewa su shirya su wuce abinsu,ranakun qarshen mako kuwa gun hajiyar suke wuni,idan ka gansu a bangarensu to wani abu suka zo yi suyi su sake komawa.
Lukman kuwa mallakar data yi masa sai ra soma damunta,ba irinta take buqata daga gunsa ba,ya zama kamar irin dolayen nan,komai tace sai yace to,ya zama kamar qaramin yaro,hatta wanka da cin abinci sai tace yayi,sai ya zame mata qarin nauyi cikim rayuwarta,bashi da wani tunani ko kadan,ko wuta tace ya sanya hannunsa ba musu zai tsumbula,abinda ta fuskanta har yau sumayya na maqale cikin zuciyarsa,sau tari zai zauna ya yita kallon qofar dakinta babu qaqqautawa har sai tazo ta koreshi,hakanan ko sunan sumayya yaji an kira koda a hanya ne sai yayi firgigit kamar wanda aka tasa daga bacci,idan kuwa su nuwaira na zaune suna hirarta sai ya zauna daga gefansu yana saurararsu yana tambayarsu kan wasu abubuwa ko sanya musu baki,a kan hirarta da suke zama suyi sai da karima ta tara su ta musu dukan tsiya,ta kulle nuwaira kuma a daki sai da hajiya ta shigo taci mata mutunci ta bude ta tace kada kuma ta sake dukar mata jikoki itace abar a daka ai basu ba,nan ta saki baki ta dinga caccabawa hajiyan magana,bata bu ta kanta ba ta kada kan jikokinta suka fice.
Wannan shine halin da karima ke ciki.
******* ******* ********