Sashe 177
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sautin murmushin dat fitar kadai ya sanar da shi ta gane waye,shima yana murmushin ya cire tafukan hannunshi daga fuskarta yayi kissing wuyanta a tausashe,sannan ya zagaya gabanta ya dane saman mudubin yayi zamanshi hannayenshi harde a qirjinsa bayan ya ajjiye ledan takeaway din daya shigo mata da shi na abinci yana ci gaba da qare mata kallo,baki daya ta takura,kunya ta lullubeta
"Me yasa baki taba zama nayita kallon ki a haka ba bayan kinsan hakan ashe ba qaramin qayatarwa gareshi ba?" Murmushi ta saki cikin kunya,bai tsaya jin amsarta ba ya dora
"Tunanin me kike haka ummu abdallah?,kinsan hakan yana da illa ga lafiyarki?"kai ta gyada sannan ta maida masa amsa
"Babu komai abu abdallah" sosai sunan ya masa dadi har qoqon ranshi,sai da ya lumshe idanunshi sannan ya bude bisa kanta
"Kada ki cemin bakiyi bacci ba"
"Nayi,na farka ne naje nayi wanka da sallah" ta fada tana murmushi
"Ummee na gaisheshi" idanu ta dan zaro
"Shine kayi tafiyanka baka tsayani munje na gaisheta ba ita da baba,kwana nawa ban gansu ba" ta qarashe maganar a shagwabe,binta kawai yake da kallo,ko iya nan ta samu wata madaukakiyar daraja da baiga macen data sameshi ba,ta maida iyayenshi tamkar naga,tana sonsu so na bilhaqqi,ya samu kabarin tun kafin suyi aure take sonsu da ganin girmansu,abinda har yau su'ad ra kasa fahimta daga gareshi,mutum ne shi wanda da iyayensa kadai zaki iya cinsa da yaqi,saboda daraja da matsayi ya basu bana wasa ba,yace bazai taba yin wasa da aljannarsa ba,duk duniya idan suka take masa ita babu mai bashi,ki ubangijinsa bai isa ya tunkara ba bayan babu kyakkyawar alaqa tsakaninshi da su,saboda yardar Allah tana tattare da yardar iyaye,hakan fushinsa yana tare da nasu fushin,sirrin nasararsa da daukakarsa ba'a komai take ba face ga albarkar iyaye,koda bata mallaki komai wanda za'a sota ba yana da yaqinin ya samawa yaranshi uwa ta gari,ya tabbata yaransji zasu tsira da sanin girman na gaba
"Yanzun ma banje wajen baba ba,shirya idan na idar da isha'i zan shigo muje" ya fada yana duba agogonshi tare da sauka daga saman madubin
"Ina fata amma baka gayawa ummee komai ba ko?" Ta fada saboda tana jin nauyinta,bata son ummeen ta fuskanci akwai wani abu,murmushi yayi,ya gano sarai mai take nufi
"Don me zanqi gaya mata?" Tuni idanunta sukayi qwalqwal da hawaye,sai ya dawo da baya,ha dagata suna fuskantar juna,nauyi ya cikata,yadda yake sake qare mata kallo a kaikaice
"Banason naga wani abu mai kama da hawaye a fuskarki......kinsan me?" Kai ta girgiza tana dubanshi
"Nima kunya nakeji,bansan me zance musu ba,espicially baba,na masa ba dai dai ba sanda ya bani aurenki ya damqa min amanarki....yanzu idan nace kina da ciki kinsan me zaice?" Kai ta sake girgizawa,sai ya jawota ya rungumeta tsam,jikinsu na gogar na juna,ya dora bakinshi a kunnenta
"Zai iya rayawa a zuciyanshi....dan banza,yace baya so ashe har yayi aiki irin haka?" Dariya ta qwace mata cike da kunya,sai ta tura kanta a qirjinsa tana dariya qasa qasa,shi dinma dariyar yake ya dan janyeta yana dubanta
"Ki shirya muje,idan kin shirya jin wannan kunyar sai a sanar mai,amma nikam ban shirya ba gaskiya,ga abinci nan kici kafin na dawi,ba nama kawai zalla ba za kiyita ci" ya fada yana juyawa,dan rage dariyar tayi tana bin bayanshi da kallo
"Me kayi masa naba dai dai dinba sanda yace ya aura maka ni?....." A ba zata tambyar tazo masa,sai ya tsaya cak ba tare da yaci gaba da tafiyar ba,jin yayi dif ya sanyata tace
"Kace masa baka sona ko?" Ta baiwa kanta amsa tana ci gaba da duban bayanshi,a nutse ya waiwayo sannan ya sake takowa zuwa gabanta,hannunshi daya ya dora kan kafadarta ya riqe yana dubanta
"Sumayya......daga kanki ki dubeni" ya bata amsa cikin kakkaurar murya,a hankali ta daga kan ta dubeshi
"Ci gaba da kallon qwayar idanuna,ina son ki bawa kanki amsa ne,kada na fadi ki dauka wasa nakeyi" a hankali ta saka idanunta cikim nashi,tsahon mintuna aqalla hudu,kamar masu kallon quda,saiga tsaiwa na neman gagararta,tuni ta janye daga kallon nashi,ba zata iya jurewa ba,ya tareta suka fada gefan gado
"Uhmmmm,zaki iya explaining?"kai ta girgiza tana niyyar tureshi,murmushi ma subuce mata,sai yanzu ta karanci wayau yayi mata,yau ta sake yarda da maganar anty dije da tace vatasan sanda sumayya zata girma ba
"Ko ni kike so nayi miki?" Da sauri ta dora hannunta saman bakinshi yana girgiza kaj,sai yayi murmushi yana sauke hannunta daga kan bakinsa
"Okey......daga yau duk ranar da kika sake min tambaya makamanciyar wannan zan hukuntaki fiye da haka,mace nada dataja wajena.......macen ma matar aurena na......matar aurena wanda ta soma kawon cikakken farinciki cikin rayuwata......kinsan wani abu?.....uwar d'ana.....dole ta zama ta daban,dole na bata wani matsayi na musamman,koda kuwa kuturwa ce gurguwa ce makauniya ce....balle ke...ke din da kika zama wata ta musamman a dukka tarihin rayuwata,kika kafamin tarihin da ban taba cin karo da shi cikin rayuwata ba" tabbas ta gamsu,ta gamsu koda bai fada ba,miqewa yayi
"Ki shirya zan kiraki muje mu gaidashi"kai kawai ta iya gyadawa,har ya fice kowannensu na murmushi.
Saman kujerar falon sama ya tadda ta wannan karon zaune,sai ua dauke kai kamar bai ganta ba yayi niyyar wucewa ciki,ganin haka ya sanyata cikin hanzari ta isa gareshi ta rungumeshi ta bayansa,cikin salon kwantar da murya ta soma fadin
"am sorry my dear,am sorry,ba nufina na bata ranka ba,u know i love you thats why,but am sorry"baisan ya zaiyi ta zama yadda yake so ba,har ga Allah bai nufin tozarci ko wulaqanci gareta,saboda bazai manta hadisin da annabi ke wasiyya ga maza su kyautatawa mata da alkhairi ba,but hakan baya nufin idan ta kauce kayi qoqafin nusashsheta taqi kabi dukka hanyoyin da zaka ladabtar da ita wadanda suka dace ba tare daka cutar da ita ba,hannunshi ya sanya ya zagayo da ita gabansa ya sanyata a jikinshi
"shikenan,ya wuce,amma kiyi qoqarin sauyawa,kiyi koyi....." Sai kuma ya katse bai qarasa din na,saboda bai kamata yayi mata misali da itan ba zata ga kaman cin fuska ne
"Ki gyara ki zaka yadda nake so,koda ba duka ba kiyi qoqarin kamantawa"
"Thank you,thank you verry much" ta fada cikin farinciki,don ba zata iya missing wannan daren ba,ta tabbatar ya juya mata baya ba komai bane wajenshi,ko a jikinsa tun sanda suke su biyu bare yanzu da yake da wata,alwala ya daura ya fice masallaci,sanda ya dawo zai sake fita ta tareshi kan ina zaya je yace zashi gaida baba
"Sau nawa kika je gaidasu bayan bana nan?" Ya tambayeta yana tsareta da ido,sai ta rausayar da kaibtana son basarwa,ranshi ya quntata,amma gyara yake son kawowa,dole yabi abuna hankali cikin hikima
"U know what?" Da sauri ta juya tana dubanshi gami da girgiza kai
"Duk yadda zaki soni....ko hadiyeni zaki kina fiddo ni,zan qaryata son da kike min matuqar baki bawa iyayena darajar data fi wadda kika bani ba" ya gaya mata da yaren da zata fi ganewa,sosai zancan ya shigeta,cikin zuciyarta ya soma mitan wanne irin sone wannan da zaya takurata da taso iyayenshi,itakam bata ga ana irin haka ba a al'ummar data taso,kuna iya kai iyayenku gidan gajiyayyu ma idan suka soma zama nauyi kanku,ko ka kai qararsu ga hukuma matuqar suna takura ka,kana iya komai gaban idanunsu ma ba kwaba ba hantara,suna yin nasu zasuyi,amma shi ko hugging dinta bai taba ba a gabansu,randa ma tayi gigin yin hakan sai da ya sabar mata,daga haka bata sake gwadawa ba,to kuma haka kawai ba zamansu take ba zai tilastata hulda da su,wannan qaddara da yawa take,ba yadda ta iya ta shiga daki ta sauya kayan jikinta zuwa gown,sakakkiya ce ba'a matse take ba,har ya soma sauka tabi bayansa,yaji dadi sosai har y fuskanshi ya nuna hakan,wanda itama hakan ya sanyata jin dadi cikin ranta.
A bakin qofa ya tsaya yayi mata knocking,koda taji tasan cewa shine,sai ta zura dogon hijabinta kan riga da skert dake jikinta ta fito,sun sanyashi tsakiya saidai ba wadda ke cewa da 'yar uwarta kanzil,suna tsaka da tafiya hibba ta hangosu ita da hibban yaran fahariyya da adam yayan almustapha,gudu ta debo ta iso inda suke kai tsaye ta ruqunqune sumayya iya qarfinta tana kiran anty
"Sake antyn taku hakanan kada ta fadi hibbah,bata jin dadi" cewaf almustapha,tana dariya ta gaidashi hibban ma haka,suka gaida su'ad sannan suka gaida sumayya
"Anty...tun ran nan rananan din cannnn.....da kika je zaki bamu labari baki bamu ba har yanzu" murmushi ta saki tana shafa kanta,tana mamakin kaifin qwaqwalwa irin ma yarinyar da har yau ta kasa mancewa sa maganar
"Zan baku in sha Allah"
"Yaushe anty"
"Ba yanzu ba sai ta warke" almustapha ya fada
"Abbanku na gida?" Ya kuma tamyarsu,hibban ne ya amsa,yace suje suce yana sin ganinshi amma ya shiga wajen baba tukunna
"Yana wajen baba prof din ai muma daga can muka fito"
"Is ok,ku shiga gida to ba kyau yawo da dare" da gudu suka juya suja wuce shi,su kuma suka ci gaba da takawa
"Anya son yaranki baifi nawa ba" murmushi ta saki
"Yara ai rahama ne,ko wajen ubangiji sau tari albarkacinsu muke ci,ba don su ba da wataqila ko ruwan sama mun daina samu" ta fada tana murmushi tare da dan dubanshi,kusan da biyu ta fadi haka,raddi ne kan maganar da su'ad ta gaya mata dazu na ta gama aiki tunda ta dauki ciki
"Gaskiya ne" ya furta a fili,cikin zuciyarsa yana sake jinjinawa baiwa da fasahar zancanta,tsaki takeso tayi amma dole ta bame bakinta,don bata son abinda zai bata daren nasu.
"Me yasa baki taba zama nayita kallon ki a haka ba bayan kinsan hakan ashe ba qaramin qayatarwa gareshi ba?" Murmushi ta saki cikin kunya,bai tsaya jin amsarta ba ya dora
"Tunanin me kike haka ummu abdallah?,kinsan hakan yana da illa ga lafiyarki?"kai ta gyada sannan ta maida masa amsa
"Babu komai abu abdallah" sosai sunan ya masa dadi har qoqon ranshi,sai da ya lumshe idanunshi sannan ya bude bisa kanta
"Kada ki cemin bakiyi bacci ba"
"Nayi,na farka ne naje nayi wanka da sallah" ta fada tana murmushi
"Ummee na gaisheshi" idanu ta dan zaro
"Shine kayi tafiyanka baka tsayani munje na gaisheta ba ita da baba,kwana nawa ban gansu ba" ta qarashe maganar a shagwabe,binta kawai yake da kallo,ko iya nan ta samu wata madaukakiyar daraja da baiga macen data sameshi ba,ta maida iyayenshi tamkar naga,tana sonsu so na bilhaqqi,ya samu kabarin tun kafin suyi aure take sonsu da ganin girmansu,abinda har yau su'ad ra kasa fahimta daga gareshi,mutum ne shi wanda da iyayensa kadai zaki iya cinsa da yaqi,saboda daraja da matsayi ya basu bana wasa ba,yace bazai taba yin wasa da aljannarsa ba,duk duniya idan suka take masa ita babu mai bashi,ki ubangijinsa bai isa ya tunkara ba bayan babu kyakkyawar alaqa tsakaninshi da su,saboda yardar Allah tana tattare da yardar iyaye,hakan fushinsa yana tare da nasu fushin,sirrin nasararsa da daukakarsa ba'a komai take ba face ga albarkar iyaye,koda bata mallaki komai wanda za'a sota ba yana da yaqinin ya samawa yaranshi uwa ta gari,ya tabbata yaransji zasu tsira da sanin girman na gaba
"Yanzun ma banje wajen baba ba,shirya idan na idar da isha'i zan shigo muje" ya fada yana duba agogonshi tare da sauka daga saman madubin
"Ina fata amma baka gayawa ummee komai ba ko?" Ta fada saboda tana jin nauyinta,bata son ummeen ta fuskanci akwai wani abu,murmushi yayi,ya gano sarai mai take nufi
"Don me zanqi gaya mata?" Tuni idanunta sukayi qwalqwal da hawaye,sai ya dawo da baya,ha dagata suna fuskantar juna,nauyi ya cikata,yadda yake sake qare mata kallo a kaikaice
"Banason naga wani abu mai kama da hawaye a fuskarki......kinsan me?" Kai ta girgiza tana dubanshi
"Nima kunya nakeji,bansan me zance musu ba,espicially baba,na masa ba dai dai ba sanda ya bani aurenki ya damqa min amanarki....yanzu idan nace kina da ciki kinsan me zaice?" Kai ta sake girgizawa,sai ya jawota ya rungumeta tsam,jikinsu na gogar na juna,ya dora bakinshi a kunnenta
"Zai iya rayawa a zuciyanshi....dan banza,yace baya so ashe har yayi aiki irin haka?" Dariya ta qwace mata cike da kunya,sai ta tura kanta a qirjinsa tana dariya qasa qasa,shi dinma dariyar yake ya dan janyeta yana dubanta
"Ki shirya muje,idan kin shirya jin wannan kunyar sai a sanar mai,amma nikam ban shirya ba gaskiya,ga abinci nan kici kafin na dawi,ba nama kawai zalla ba za kiyita ci" ya fada yana juyawa,dan rage dariyar tayi tana bin bayanshi da kallo
"Me kayi masa naba dai dai dinba sanda yace ya aura maka ni?....." A ba zata tambyar tazo masa,sai ya tsaya cak ba tare da yaci gaba da tafiyar ba,jin yayi dif ya sanyata tace
"Kace masa baka sona ko?" Ta baiwa kanta amsa tana ci gaba da duban bayanshi,a nutse ya waiwayo sannan ya sake takowa zuwa gabanta,hannunshi daya ya dora kan kafadarta ya riqe yana dubanta
"Sumayya......daga kanki ki dubeni" ya bata amsa cikin kakkaurar murya,a hankali ta daga kan ta dubeshi
"Ci gaba da kallon qwayar idanuna,ina son ki bawa kanki amsa ne,kada na fadi ki dauka wasa nakeyi" a hankali ta saka idanunta cikim nashi,tsahon mintuna aqalla hudu,kamar masu kallon quda,saiga tsaiwa na neman gagararta,tuni ta janye daga kallon nashi,ba zata iya jurewa ba,ya tareta suka fada gefan gado
"Uhmmmm,zaki iya explaining?"kai ta girgiza tana niyyar tureshi,murmushi ma subuce mata,sai yanzu ta karanci wayau yayi mata,yau ta sake yarda da maganar anty dije da tace vatasan sanda sumayya zata girma ba
"Ko ni kike so nayi miki?" Da sauri ta dora hannunta saman bakinshi yana girgiza kaj,sai yayi murmushi yana sauke hannunta daga kan bakinsa
"Okey......daga yau duk ranar da kika sake min tambaya makamanciyar wannan zan hukuntaki fiye da haka,mace nada dataja wajena.......macen ma matar aurena na......matar aurena wanda ta soma kawon cikakken farinciki cikin rayuwata......kinsan wani abu?.....uwar d'ana.....dole ta zama ta daban,dole na bata wani matsayi na musamman,koda kuwa kuturwa ce gurguwa ce makauniya ce....balle ke...ke din da kika zama wata ta musamman a dukka tarihin rayuwata,kika kafamin tarihin da ban taba cin karo da shi cikin rayuwata ba" tabbas ta gamsu,ta gamsu koda bai fada ba,miqewa yayi
"Ki shirya zan kiraki muje mu gaidashi"kai kawai ta iya gyadawa,har ya fice kowannensu na murmushi.
Saman kujerar falon sama ya tadda ta wannan karon zaune,sai ua dauke kai kamar bai ganta ba yayi niyyar wucewa ciki,ganin haka ya sanyata cikin hanzari ta isa gareshi ta rungumeshi ta bayansa,cikin salon kwantar da murya ta soma fadin
"am sorry my dear,am sorry,ba nufina na bata ranka ba,u know i love you thats why,but am sorry"baisan ya zaiyi ta zama yadda yake so ba,har ga Allah bai nufin tozarci ko wulaqanci gareta,saboda bazai manta hadisin da annabi ke wasiyya ga maza su kyautatawa mata da alkhairi ba,but hakan baya nufin idan ta kauce kayi qoqafin nusashsheta taqi kabi dukka hanyoyin da zaka ladabtar da ita wadanda suka dace ba tare daka cutar da ita ba,hannunshi ya sanya ya zagayo da ita gabansa ya sanyata a jikinshi
"shikenan,ya wuce,amma kiyi qoqarin sauyawa,kiyi koyi....." Sai kuma ya katse bai qarasa din na,saboda bai kamata yayi mata misali da itan ba zata ga kaman cin fuska ne
"Ki gyara ki zaka yadda nake so,koda ba duka ba kiyi qoqarin kamantawa"
"Thank you,thank you verry much" ta fada cikin farinciki,don ba zata iya missing wannan daren ba,ta tabbatar ya juya mata baya ba komai bane wajenshi,ko a jikinsa tun sanda suke su biyu bare yanzu da yake da wata,alwala ya daura ya fice masallaci,sanda ya dawo zai sake fita ta tareshi kan ina zaya je yace zashi gaida baba
"Sau nawa kika je gaidasu bayan bana nan?" Ya tambayeta yana tsareta da ido,sai ta rausayar da kaibtana son basarwa,ranshi ya quntata,amma gyara yake son kawowa,dole yabi abuna hankali cikin hikima
"U know what?" Da sauri ta juya tana dubanshi gami da girgiza kai
"Duk yadda zaki soni....ko hadiyeni zaki kina fiddo ni,zan qaryata son da kike min matuqar baki bawa iyayena darajar data fi wadda kika bani ba" ya gaya mata da yaren da zata fi ganewa,sosai zancan ya shigeta,cikin zuciyarta ya soma mitan wanne irin sone wannan da zaya takurata da taso iyayenshi,itakam bata ga ana irin haka ba a al'ummar data taso,kuna iya kai iyayenku gidan gajiyayyu ma idan suka soma zama nauyi kanku,ko ka kai qararsu ga hukuma matuqar suna takura ka,kana iya komai gaban idanunsu ma ba kwaba ba hantara,suna yin nasu zasuyi,amma shi ko hugging dinta bai taba ba a gabansu,randa ma tayi gigin yin hakan sai da ya sabar mata,daga haka bata sake gwadawa ba,to kuma haka kawai ba zamansu take ba zai tilastata hulda da su,wannan qaddara da yawa take,ba yadda ta iya ta shiga daki ta sauya kayan jikinta zuwa gown,sakakkiya ce ba'a matse take ba,har ya soma sauka tabi bayansa,yaji dadi sosai har y fuskanshi ya nuna hakan,wanda itama hakan ya sanyata jin dadi cikin ranta.
A bakin qofa ya tsaya yayi mata knocking,koda taji tasan cewa shine,sai ta zura dogon hijabinta kan riga da skert dake jikinta ta fito,sun sanyashi tsakiya saidai ba wadda ke cewa da 'yar uwarta kanzil,suna tsaka da tafiya hibba ta hangosu ita da hibban yaran fahariyya da adam yayan almustapha,gudu ta debo ta iso inda suke kai tsaye ta ruqunqune sumayya iya qarfinta tana kiran anty
"Sake antyn taku hakanan kada ta fadi hibbah,bata jin dadi" cewaf almustapha,tana dariya ta gaidashi hibban ma haka,suka gaida su'ad sannan suka gaida sumayya
"Anty...tun ran nan rananan din cannnn.....da kika je zaki bamu labari baki bamu ba har yanzu" murmushi ta saki tana shafa kanta,tana mamakin kaifin qwaqwalwa irin ma yarinyar da har yau ta kasa mancewa sa maganar
"Zan baku in sha Allah"
"Yaushe anty"
"Ba yanzu ba sai ta warke" almustapha ya fada
"Abbanku na gida?" Ya kuma tamyarsu,hibban ne ya amsa,yace suje suce yana sin ganinshi amma ya shiga wajen baba tukunna
"Yana wajen baba prof din ai muma daga can muka fito"
"Is ok,ku shiga gida to ba kyau yawo da dare" da gudu suka juya suja wuce shi,su kuma suka ci gaba da takawa
"Anya son yaranki baifi nawa ba" murmushi ta saki
"Yara ai rahama ne,ko wajen ubangiji sau tari albarkacinsu muke ci,ba don su ba da wataqila ko ruwan sama mun daina samu" ta fada tana murmushi tare da dan dubanshi,kusan da biyu ta fadi haka,raddi ne kan maganar da su'ad ta gaya mata dazu na ta gama aiki tunda ta dauki ciki
"Gaskiya ne" ya furta a fili,cikin zuciyarsa yana sake jinjinawa baiwa da fasahar zancanta,tsaki takeso tayi amma dole ta bame bakinta,don bata son abinda zai bata daren nasu.