Sashe 107
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wajen sha biyu ta sameta dakinta tana fitar da kayan da suka dawo da su tana kuma shirya wasu cikin wata jakar daban
"Sumayya,meke damunki?,ko don na miki fada jiya" kamar mai jira sai taji qwalla ta cika mata idanu,kai take girgizawa tana duban anty dijen
"Ba don wani abu yasa na miki magana ba,na fuskanci abinda ke faruwa da ke ne,ina so ki sauya kanki ne" da sauri ta tareta
"Ki daina fadar haka anty,wlh ba haka bane,ke uwa ce a gareni,kina da ikon zartar da duk hukuncin da ya dace da ni,nima bansan me yasa a duk sanda yayi magana nake zamowa haka ba,mukhtar dina nake tunawa anty har yau yaqi barin zuciyata,muryar mukhtar nake ji cikin tasa,sai na dinga jin kamar shine tare da ni" tausayin sumayya ya kamata,ta kama hannuwanta tana duban idanuwanta tana murmushi
"Na fahimceki sumayya,amma shi baisan da haka ba,bana son ya raina min ke ko yayi tunanin wani abu na daban,nafa ji zafin abinda ya miki da fari,ban fadi miki bane saboda yayi ne cikin rashin sani......ki zama jaruma pls,ki dinga tunawa ba shine mukhtar ba....any way,mu ajjiye wannan maganar a gefe,me zakiyi da wadan nan kayan da kike shiryawa a jaka?" Hawayen take gogewa da tafin hannunta itama tana murmushi
"Kano nake so gobe na tafi" idanu ta zaro
"Kano sumayya gobe daga dawowarmu jiya,ko dai wani abun daban aka yi miki?" Marairaice wa tayi
"Don Allah umman khalipha ki daina cewa an min wani abu,kin taba gani uwa ta yiwa 'yarta wani abu ba dai dai ba,kuma diyar ranta ya baci?"
"To idan ba haka ba ai kya bari ko zuwa next week ne atleast ko?,zuwa sannan kin warware gajiyar tafiya kin fidda tsarabar su malam"
"Anty inata kara amma baki gane me nake nufi ba,na qagu any naga abdallah,i missed him alort anty,shima kuma nasan haka ne" kama baki tayi taja dariya
"Iyeeee,lallai yarinya,ga malam ga mama duka su bakiyi missing dinsu ba sai yaronki gaskiya ne" kunya ta kama sumayyan ta kifa kanta saman hannun anty tana dariya qasa qasa,ba zata iya boyewa ba,tabbas tayi missing yaronta
"Shikenan,Allah ya kaimu,amma fa saidai ki bari sai jibi,zamu bude jaka afidda kayan su malam" duk da cewa ba hakan taso ba amma anty dije tafi gaban tayi jayayya da ita haka ta amsa mata da to.
Misalin uku na rana suna zaune suna cin abincin rana amira ta shigo,bisa dukkan alamu daga makaranta take,don ga handout nan a hannunta da key din motarta,wani daj ihun farinciki ta saki tana qarasowa kusa da sumayya,gaisawa sukayi da anty dije tana tsatstsokanar su laila khalipha da minal,baki daya tace sun sauya,lallai garin ya karbesu,sai ta maida dubanta ga sumayya
"Umman khalipha wai wannan amiran umman khalipha ce ko wata kuka samo a can?" Dariya suka saki baki daya kowa ya gane me take nufi,cikin salon zolaya itama sumayyan tace
"Sun baro waccar a can,wannan musanyota sukayi" dukan cinyar sumayyan amira tayi tana fadin
"Kina kallon mudubi kuwa?,wallahi kin bala'in zama wata queen namesake,ni zan fara yiwa alqasim wannan albishir din" harara ta aika mata tana murmushi
"Ban aikeki ba,bismillah sa hannu muci abinci" idanuwanta ta maida kan abincin wanda saura duk da miya suke ci banda ita,fara da man take jin ci don an dade ba'a hadu ba
"Wai wai,an kuwa zanci,shinkafa da wake da manja ne da yaji ko?,ga kuma salad,rabona da abincin nan da dewa,ina son fara da mai da yaji,su kam saidai suyi miya,musamman idan waccan baturiyar tazo,bama tasan fara da mai ba,idan taga wani yana ci har kyabe baki take wai muna cin abinci gaya" ta fada itama tana tabe baki,murmushi anty dije tayi
"Dan gidanku yayarki ce dai,kuma kinsan baki isa ku fadi ba gaban maigidanta" amsa mata ta soma bayan tayi cokali daya
"Me ruwa na da su,shima shi yaga zaya iya,haka kawai mutum bashi da maraba da gauro,kowa yana ci gaba ta fuskan family amma banda shi,haka kawai jiya har na kwanta ya tada ni wai na hada mishi fruit salad baturen kawai ga abinci ba zaya ci ba wai yayi masa nauyi"
"Ke amira,zakici gidanku,ba yayanki bane?" Saki tabe fuska tayi kakar zata saki kuka
"Ni umman khalipha bama wannan bane ya qonan raj,Allah anty su'adah 'yar rainin sense ce,na shiga kai mishi naji suna waya,ta baro america ta biyoshi dubai wai bata tadda shi,yace bai nan yana naija wai gobe zata biyoshi,wannam ai ba matar aure bace matar yawo ce,kuma kowa yw zuba mishi idanu wai matarshi ce haka suka tsara rayuwansu,to wallahi aure zamu masa" baki daya ta basu dariya saboda salon yadda tayi maganar bilhaqqi,har sumayya na qwarewa sai data kurbi ruwa
"To ba sai ki masa ba tunda kece gaba da shi,kijimim tsaurin ido,musty zaki ma aure?,yo ko adam ai bai usa yace zaya yi masa aure ba bare ke" tsaki sumayya ta ja bayan ta samu tarin ya tsaya tana dan dukan cinyar amiran
"Kinga malama,ki dinga maganar da zata amfanemu,juyo muci abinci" waiwayowa tayi tana duban sumayya
"Uhmmmm,wallahi kuwa,don wannan babu ranar sauyawarsu" sai tayi qasa qasa da murya
"Kefa kawai nake jira ki dawo a fara tsara mai yiwuwa,jibi za'a kawo lefe fa,kuma da sati uku zasu zo kwanakin bikin"
"Komai kika tsara dai dai ne,amma ni jibin zan wuce kano" idanu ta zaro tana tsaida cin abincin da take
"Me kika fada namesake,ina ce miki jibi kawo lefe kina cemin jibi zaki tafi kano,a satin nan fa zamu je dubai siyo kayan kitchen,tare da ya musty zamu koma,shigowar nan da nayi passport naki nazo karba za'a buga mana visa" cabdi,wane musty din,mustaphansu?,ta godewa Allah da ya bata idea din tafiya kano,don ko ana yankan jikinta ba zata bisu ba,wannan dan jin kan?,dan wulaqancin dan rainin wayo?
"Kice wani abu mana kinyi shiru,duk kin rusan plan,wallahi idan baki je ba da wannan matar tashi zaya hadanu siyan kayan kitchen,bayan babu abinda tasan amfaninsa a kitchen saidai ta ganshi da ido,sai shegen izza da dagawa,zata siya min kayan shirme ne masu dan banzar tsada tana ganin kudin mijinta ne,kamar an gaya mata shi mai kudi baisan ciwo da zafinsu ba" ajiyar zuciya ta saki
"Banji dadi bane amira,amma zuwa kano ya zame min dole jibi,malam na son ganina" ta hada da qarya,sai anty dije tayi saurin tashi ta doshi kitchen don kada amira ta roqeta ta hana sumayyan zuwa,don qaryan sumayyan ta mata dai dai,koda tana abuja ba zata barta taje ba,don ta fuskanci inuwa daya bata zaunuwa tsakanin sumayyan da shi uban gayyar,bare tafiya ma wata uwa duniya babu muharramin sumayyan ba zata yarda tayi ta ba.
Shuru amira tayi wanda hakan ke gwada baki daya bata ji dadi ba,jikinta a sanyaye taci gaba da cin abincin,sai da daqiqa kusan biyar ta shude sannan ta iya cewa
"Malam yafi gaban komai amira,sai kin dawo Allah ya kiyaye,amma don Allah ki dawo da wuri,sannan kimin alqawari zaki shiga ayi komai da ke,zaki dauki kanki kamar diyar baabaa,wallahu tun wancan satin baabaa ke tsokanata,wai idan baki dawo ba baisan ya zanyi ba,qila saidai ya daga bikin ko?" Murmushi tayi,alqawarin yayi mata girma da yawa,amma tilas ta dauka,anayi da kai yafi ba'a yi da kai,masoyinka kuma yafi maqiyinka
"Kada ki damu,nayi alqawari in sha Allah"
"Amma kafin ki wuce zaki shigo ki gaida su ummee,daga nan kiga ankon da aka fitar ko,ku hudu amma kalar naku daban,ke da qawaye na su uku"
"Me zai hana,in sha Allah" ta fada kawai din a wuce gun,amma mai zai kaita gidan a irin wannan lokacin da wannan mutumin ke qasar,daga haka ta ware suka ci gaba da hirarsu.
******** ******** ********
Tun dare ta kasa bacci,gani take kamar gari bazai waye ba,bata ji kwanciyar hankali ba sai data ganta a mota sun dauki hanya,babu wanda ta gayawa tana zuwa don so take tayi masu ba zata.
Qarfe daya da minti ashirin na azahar a qofar gida tayi musu kasancewar sun fito ne da wuri,ita ta fara shiga kafin driver din su anty dijen ya soma shiga mata da akwatunta da qatuwar jakar dake dauke da kayan tsaraba.
Halima ce a kitchen,mama na bakin fanfo tana daura alwalar sallar azahar,yayin da zainab ke mopping falon mama wanda ta dage labulensa,hakimin abdallah na kwance abinsa saman kujera yana kallon cartoon,zainab na mopping din tana mitar ya hanasu kallon kowacce tasha sai ta 'yan aljanu,mama na fadin ai yafi,sunfi son suyita kallon waqe waqe da raye rayen banzan nan da wofi.
Tana sallamar halima ta saki kwashe miyar da takeyi ta fito,zainab ta saki mopper,yayin da mama tayi tsaye tana dubanta tare da amsa mata sallamar fuskarta dauke da madaukakin murmushi,kusan a tare suja ruqunqumeta suna ambatar sunanta,dadi ya cika kowannansu,sam abdallah bai fahimci me ake ba sai da suka shigo falon,dirowa yayi daga kan kujerar yayi kan sumayya yana kiran
"Mamiiiiiiii naaaaaaa" baki daya ya cukuikuyeta kamar zai shige jikinta,itama tsam ta rungumeshi tana dariya farinciki fal zuciyarta kamar an wanketa da ruwan qanqara.
Baki daya sun baibayeta,idanuwanta na kam abdallah,photocopy na mukhtar take kalla,cikin shekara guda tal ya sake wani girma da wayo na ban mamaki,ya fara zama dan saurayi,shekara kusan biyar ba wasa bace,girman dan mutum babu wuya,duba daya ya wadatar da kai ka gane yaron na samun gata da kulawa,don suturar jikinsa ma kadai amsa ce,zainab da halima kowa da abinda zai fadi
"Yaya sumayya kin ganki kuwa?,kamar irin hajiyoyin nan"
"Yaya sumayya kin zama budurwa wallahi,irin 'yammatan abujan nan,gaskiya tafiyan nan ta karbeki,kaman an canjoki baki daya" dariya take ta rasa abin cewa,tunda ta sauko daga mota ta lura da kallon da jama'ar unguwar tasu ke mata wasu ma kamar basu ganeta ba,haka su halina suka cikata da surutu har sai da mama ta korasu halima taje ta zubo abinci ta kaima driver a waje din da yayi salla zai koma,sannan ta zubowa sumayyan ma, zainab kuma ta kai mata kayan daki,sai bayan fitarsu sannan suka ji kunnuwansu,abdallah na maqale jikinta yana ta bare choculets yana gama musu aiki.
Haka suka wuni ba wanda ya fita a gidan,sai maqota dake shigowa jifa jifa yi mata sannu da zuwa,wanda wasunsu labarin yadda sumayyar ta koma suka ji suka zo ganewa idanuwansu.
"Sumayya,meke damunki?,ko don na miki fada jiya" kamar mai jira sai taji qwalla ta cika mata idanu,kai take girgizawa tana duban anty dijen
"Ba don wani abu yasa na miki magana ba,na fuskanci abinda ke faruwa da ke ne,ina so ki sauya kanki ne" da sauri ta tareta
"Ki daina fadar haka anty,wlh ba haka bane,ke uwa ce a gareni,kina da ikon zartar da duk hukuncin da ya dace da ni,nima bansan me yasa a duk sanda yayi magana nake zamowa haka ba,mukhtar dina nake tunawa anty har yau yaqi barin zuciyata,muryar mukhtar nake ji cikin tasa,sai na dinga jin kamar shine tare da ni" tausayin sumayya ya kamata,ta kama hannuwanta tana duban idanuwanta tana murmushi
"Na fahimceki sumayya,amma shi baisan da haka ba,bana son ya raina min ke ko yayi tunanin wani abu na daban,nafa ji zafin abinda ya miki da fari,ban fadi miki bane saboda yayi ne cikin rashin sani......ki zama jaruma pls,ki dinga tunawa ba shine mukhtar ba....any way,mu ajjiye wannan maganar a gefe,me zakiyi da wadan nan kayan da kike shiryawa a jaka?" Hawayen take gogewa da tafin hannunta itama tana murmushi
"Kano nake so gobe na tafi" idanu ta zaro
"Kano sumayya gobe daga dawowarmu jiya,ko dai wani abun daban aka yi miki?" Marairaice wa tayi
"Don Allah umman khalipha ki daina cewa an min wani abu,kin taba gani uwa ta yiwa 'yarta wani abu ba dai dai ba,kuma diyar ranta ya baci?"
"To idan ba haka ba ai kya bari ko zuwa next week ne atleast ko?,zuwa sannan kin warware gajiyar tafiya kin fidda tsarabar su malam"
"Anty inata kara amma baki gane me nake nufi ba,na qagu any naga abdallah,i missed him alort anty,shima kuma nasan haka ne" kama baki tayi taja dariya
"Iyeeee,lallai yarinya,ga malam ga mama duka su bakiyi missing dinsu ba sai yaronki gaskiya ne" kunya ta kama sumayyan ta kifa kanta saman hannun anty tana dariya qasa qasa,ba zata iya boyewa ba,tabbas tayi missing yaronta
"Shikenan,Allah ya kaimu,amma fa saidai ki bari sai jibi,zamu bude jaka afidda kayan su malam" duk da cewa ba hakan taso ba amma anty dije tafi gaban tayi jayayya da ita haka ta amsa mata da to.
Misalin uku na rana suna zaune suna cin abincin rana amira ta shigo,bisa dukkan alamu daga makaranta take,don ga handout nan a hannunta da key din motarta,wani daj ihun farinciki ta saki tana qarasowa kusa da sumayya,gaisawa sukayi da anty dije tana tsatstsokanar su laila khalipha da minal,baki daya tace sun sauya,lallai garin ya karbesu,sai ta maida dubanta ga sumayya
"Umman khalipha wai wannan amiran umman khalipha ce ko wata kuka samo a can?" Dariya suka saki baki daya kowa ya gane me take nufi,cikin salon zolaya itama sumayyan tace
"Sun baro waccar a can,wannan musanyota sukayi" dukan cinyar sumayyan amira tayi tana fadin
"Kina kallon mudubi kuwa?,wallahi kin bala'in zama wata queen namesake,ni zan fara yiwa alqasim wannan albishir din" harara ta aika mata tana murmushi
"Ban aikeki ba,bismillah sa hannu muci abinci" idanuwanta ta maida kan abincin wanda saura duk da miya suke ci banda ita,fara da man take jin ci don an dade ba'a hadu ba
"Wai wai,an kuwa zanci,shinkafa da wake da manja ne da yaji ko?,ga kuma salad,rabona da abincin nan da dewa,ina son fara da mai da yaji,su kam saidai suyi miya,musamman idan waccan baturiyar tazo,bama tasan fara da mai ba,idan taga wani yana ci har kyabe baki take wai muna cin abinci gaya" ta fada itama tana tabe baki,murmushi anty dije tayi
"Dan gidanku yayarki ce dai,kuma kinsan baki isa ku fadi ba gaban maigidanta" amsa mata ta soma bayan tayi cokali daya
"Me ruwa na da su,shima shi yaga zaya iya,haka kawai mutum bashi da maraba da gauro,kowa yana ci gaba ta fuskan family amma banda shi,haka kawai jiya har na kwanta ya tada ni wai na hada mishi fruit salad baturen kawai ga abinci ba zaya ci ba wai yayi masa nauyi"
"Ke amira,zakici gidanku,ba yayanki bane?" Saki tabe fuska tayi kakar zata saki kuka
"Ni umman khalipha bama wannan bane ya qonan raj,Allah anty su'adah 'yar rainin sense ce,na shiga kai mishi naji suna waya,ta baro america ta biyoshi dubai wai bata tadda shi,yace bai nan yana naija wai gobe zata biyoshi,wannam ai ba matar aure bace matar yawo ce,kuma kowa yw zuba mishi idanu wai matarshi ce haka suka tsara rayuwansu,to wallahi aure zamu masa" baki daya ta basu dariya saboda salon yadda tayi maganar bilhaqqi,har sumayya na qwarewa sai data kurbi ruwa
"To ba sai ki masa ba tunda kece gaba da shi,kijimim tsaurin ido,musty zaki ma aure?,yo ko adam ai bai usa yace zaya yi masa aure ba bare ke" tsaki sumayya ta ja bayan ta samu tarin ya tsaya tana dan dukan cinyar amiran
"Kinga malama,ki dinga maganar da zata amfanemu,juyo muci abinci" waiwayowa tayi tana duban sumayya
"Uhmmmm,wallahi kuwa,don wannan babu ranar sauyawarsu" sai tayi qasa qasa da murya
"Kefa kawai nake jira ki dawo a fara tsara mai yiwuwa,jibi za'a kawo lefe fa,kuma da sati uku zasu zo kwanakin bikin"
"Komai kika tsara dai dai ne,amma ni jibin zan wuce kano" idanu ta zaro tana tsaida cin abincin da take
"Me kika fada namesake,ina ce miki jibi kawo lefe kina cemin jibi zaki tafi kano,a satin nan fa zamu je dubai siyo kayan kitchen,tare da ya musty zamu koma,shigowar nan da nayi passport naki nazo karba za'a buga mana visa" cabdi,wane musty din,mustaphansu?,ta godewa Allah da ya bata idea din tafiya kano,don ko ana yankan jikinta ba zata bisu ba,wannan dan jin kan?,dan wulaqancin dan rainin wayo?
"Kice wani abu mana kinyi shiru,duk kin rusan plan,wallahi idan baki je ba da wannan matar tashi zaya hadanu siyan kayan kitchen,bayan babu abinda tasan amfaninsa a kitchen saidai ta ganshi da ido,sai shegen izza da dagawa,zata siya min kayan shirme ne masu dan banzar tsada tana ganin kudin mijinta ne,kamar an gaya mata shi mai kudi baisan ciwo da zafinsu ba" ajiyar zuciya ta saki
"Banji dadi bane amira,amma zuwa kano ya zame min dole jibi,malam na son ganina" ta hada da qarya,sai anty dije tayi saurin tashi ta doshi kitchen don kada amira ta roqeta ta hana sumayyan zuwa,don qaryan sumayyan ta mata dai dai,koda tana abuja ba zata barta taje ba,don ta fuskanci inuwa daya bata zaunuwa tsakanin sumayyan da shi uban gayyar,bare tafiya ma wata uwa duniya babu muharramin sumayyan ba zata yarda tayi ta ba.
Shuru amira tayi wanda hakan ke gwada baki daya bata ji dadi ba,jikinta a sanyaye taci gaba da cin abincin,sai da daqiqa kusan biyar ta shude sannan ta iya cewa
"Malam yafi gaban komai amira,sai kin dawo Allah ya kiyaye,amma don Allah ki dawo da wuri,sannan kimin alqawari zaki shiga ayi komai da ke,zaki dauki kanki kamar diyar baabaa,wallahu tun wancan satin baabaa ke tsokanata,wai idan baki dawo ba baisan ya zanyi ba,qila saidai ya daga bikin ko?" Murmushi tayi,alqawarin yayi mata girma da yawa,amma tilas ta dauka,anayi da kai yafi ba'a yi da kai,masoyinka kuma yafi maqiyinka
"Kada ki damu,nayi alqawari in sha Allah"
"Amma kafin ki wuce zaki shigo ki gaida su ummee,daga nan kiga ankon da aka fitar ko,ku hudu amma kalar naku daban,ke da qawaye na su uku"
"Me zai hana,in sha Allah" ta fada kawai din a wuce gun,amma mai zai kaita gidan a irin wannan lokacin da wannan mutumin ke qasar,daga haka ta ware suka ci gaba da hirarsu.
******** ******** ********
Tun dare ta kasa bacci,gani take kamar gari bazai waye ba,bata ji kwanciyar hankali ba sai data ganta a mota sun dauki hanya,babu wanda ta gayawa tana zuwa don so take tayi masu ba zata.
Qarfe daya da minti ashirin na azahar a qofar gida tayi musu kasancewar sun fito ne da wuri,ita ta fara shiga kafin driver din su anty dijen ya soma shiga mata da akwatunta da qatuwar jakar dake dauke da kayan tsaraba.
Halima ce a kitchen,mama na bakin fanfo tana daura alwalar sallar azahar,yayin da zainab ke mopping falon mama wanda ta dage labulensa,hakimin abdallah na kwance abinsa saman kujera yana kallon cartoon,zainab na mopping din tana mitar ya hanasu kallon kowacce tasha sai ta 'yan aljanu,mama na fadin ai yafi,sunfi son suyita kallon waqe waqe da raye rayen banzan nan da wofi.
Tana sallamar halima ta saki kwashe miyar da takeyi ta fito,zainab ta saki mopper,yayin da mama tayi tsaye tana dubanta tare da amsa mata sallamar fuskarta dauke da madaukakin murmushi,kusan a tare suja ruqunqumeta suna ambatar sunanta,dadi ya cika kowannansu,sam abdallah bai fahimci me ake ba sai da suka shigo falon,dirowa yayi daga kan kujerar yayi kan sumayya yana kiran
"Mamiiiiiiii naaaaaaa" baki daya ya cukuikuyeta kamar zai shige jikinta,itama tsam ta rungumeshi tana dariya farinciki fal zuciyarta kamar an wanketa da ruwan qanqara.
Baki daya sun baibayeta,idanuwanta na kam abdallah,photocopy na mukhtar take kalla,cikin shekara guda tal ya sake wani girma da wayo na ban mamaki,ya fara zama dan saurayi,shekara kusan biyar ba wasa bace,girman dan mutum babu wuya,duba daya ya wadatar da kai ka gane yaron na samun gata da kulawa,don suturar jikinsa ma kadai amsa ce,zainab da halima kowa da abinda zai fadi
"Yaya sumayya kin ganki kuwa?,kamar irin hajiyoyin nan"
"Yaya sumayya kin zama budurwa wallahi,irin 'yammatan abujan nan,gaskiya tafiyan nan ta karbeki,kaman an canjoki baki daya" dariya take ta rasa abin cewa,tunda ta sauko daga mota ta lura da kallon da jama'ar unguwar tasu ke mata wasu ma kamar basu ganeta ba,haka su halina suka cikata da surutu har sai da mama ta korasu halima taje ta zubo abinci ta kaima driver a waje din da yayi salla zai koma,sannan ta zubowa sumayyan ma, zainab kuma ta kai mata kayan daki,sai bayan fitarsu sannan suka ji kunnuwansu,abdallah na maqale jikinta yana ta bare choculets yana gama musu aiki.
Haka suka wuni ba wanda ya fita a gidan,sai maqota dake shigowa jifa jifa yi mata sannu da zuwa,wanda wasunsu labarin yadda sumayyar ta koma suka ji suka zo ganewa idanuwansu.