Sashe 10
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana nan tana yanka salad din ta soma jiyo tashin maganganunsu gami da shewa
"Wai dama wannan ce kishiyar taki?
Cab di wannan ai ma'aikaciya kurum kika samu
Lallai ai wannan banga abun kishi ba
Ke irinsu fa sunfi iya tsiya wallahi,kada ki soma cewa zaki sakar mata fuska balle ta rainaki,ki dasa mata tsoronki,bada umarni ne kawai tsakaninku
Wallahi ki bautar da shegiya,ki mori bati" take taji jikinta ya kama rawa gabanta ya shiga faduwa,lallai ba shakka suna iya dukanta,haka zuciyarta ta dinga raya mata,zuciyarta tsoro fal irin na yarinta,su kamsu suna sane suka dinga maganar don ta jisu,saboda su dasa tsoro cikin zuciyarta.
Kitchen din ta tattara ta koma tana ci gaba da ayyukanta,sai dai har yanzu tsoron bai saketa ba,addu'a ta dinga yi cikin zuciyarta hakan ya sanya ta dan samu nutsuwa.
Tana gab da kammala girkin fa'iza ta shigo kitchen din ita da daya daga cikin baqin nata tana fadin
"Ga bangare na nan,ki dafa duka abinda kuka ga ya muku yadda zai isheku" sumayya ta waiwayo tana dubanta
"Amma amarya har da ku nayi abincin fa zaya ishemu duka,ina ga idan aka dafa wani zaiyi yawa" juyowa itama tayi ta zabga mata wata harara sannan ta nunata da yatsa
"Ina cewa ko awa biyu ba'a yi ba da yi miki maganar ki guji shiga sabgata ba ko,ke har kin isa kina sa'ar qanwata ki dinga dafawa kina bani iya limit din da kika ga dama ina ci?,kin shirya cin na jaki kenan,don wallahi jibgarki zanyi a gidan nan banza juya kawai" sai ta dauke kanta daga garesu ta maida kan girkinta,abun mamaki sai kalmar juya yau tayi mata zafi,karo na farko kenan da ta taba jin hakan.
Tana jinta ta gama gayawa baquwar tata abinda za'ayi ta fice,bakin fanfo ta wuce ta tari ruwa ta shiga wanka don sai yanzu ta samu damar yin.
Tana kammala girkin ta zubawa mukhtar nashi,ta zuba nasu fa'izan ta aza a bangaren kantarta ta dibi wanda zata ci ta shige daki abinta,bata sake fitowa ba har suka gama tsiyar da zasuyi suka tafi wajen qarfe biyar na yamma,a sannan ta fito ta shiga kitchen don dora ruwan wanka.
Tamkar ba'a taba guara kitchen din ba haka suka lalatashi,ga uban abinci nan da suka dafa sun kasa cinyeshi cikin tukunya a bude,kwanukan duka vikin sink din fa'iza gaje gaje,hatta wanda ta ajjiye musu sun cakalkala shi sun bar cooler rabi a bude rabi a rufe.
Ranta taji ya baci karo na farko,ta tsani almubazzaranci da abinci,saboda tana da imamin abinda ka raina shi wani ke nema yasa a bakin salatinsa amma ya gagareshi,to don me kai don Allah ya baka zaka wulaqanga,bayan ya baka ne ba don kafi kowa ba.
Bata gaji ba bayan ta dora ruwan ta soma tattara kitchen din,ta gyara ko ina fes,saidai batasan ya zatayi da abincin ba tun kafin mukhtar ya gani yaji babu dadi,ita ba leqe take ba kuma yaro gidan bare ta samu almajiri ta bashi,dole ta jira dan aike yazo.
Ruwanta na zafi ta juye ta shiga wanka,can ma sai da ta tsaya ta gyara,sam bata qaunar taga guri ko yaya ya sauya yanayi.
Taji qarar babur dinsa sanda take maida kaskon turaren wuta kitchen,sanin cewar gidan a bude yake ba kamar sanda tana ita daya ba saboda haka ta toge a tsakar gidan tana jiran shigowarsa.
Cikin mintuna ya qaraso tsakar gidan,tana murmushi ta qarasa inda yake tana niyyar karbar jakarsa,sai ya bude hannayensa ya kai mata runguma sai ta goce tana murmushi tare da kallon qofar dakim fa'iza,qasa qasa da murya tace
"Bamu kadai bane fa a gidan" ta miqa hannu ta karbi kayan hannun nasa,sai ya kalleta yana turbune fuska
"Haka kawai tun yau an fara shiga haqqina,ai shikenan" yayi maganar yana wucewa dakinsa ta bishi a baya tana masa gwalo.
Har ta kammala kintsa abinda ya shigo da shi babu fa'iza babu alamarta,sai da ta gama zata fita daga dakin sukayi kacibus da fa'izan na shigowa,harara ta balla mata,gefe ta matsa ta raba ta kawai ta wuce.
Tunda ta gabatar musu da abinci tayi alwalar sallar magariba shigewarta daki,bata sake fitowa ba sai da taji mukhtar na qwala mata kira,ta miqe a hankali ta gyara daurin dankwalinta ta amsa tana fitowa.
A kitchen ta tadda shi tsaye ransa bace yana qarewa himilin abincin kallo,gefe guda kuma ga dankali da qwai da fa'izan ta soya a wulaqance cikin cooler ba'a idasa cinye shi ba,ya dago idanunsa daga kallon coolers din ya maida su ga sumayya,da hannu yayi mata nuni
"Me wannan?,meye haka sumayya?" A ladabce tace
"Nima ban sani ba ya mukhtar saidai ka tambayi amarya" baiyi musun hakan ba tunda a gefanta yaga tarin coolers din,ya daga murya ya qwala mata kira,ta shigo kitchen din sanye da hijab
"Gani" ta fada tana kallonshi.
Ya kalli kayan ya kalleta sannan yace
"Wannan na waye?"
"Na baqin da nayi ne" ya hadiye wani takaici saboda yadda tayi maganar cikin halin ko in kula da nuna rashin muhimmancin laifinta,wacce iriyar yarinya ce ita,yinin farko kenan a gidan mijinta?,yayi qoqarin danne bacin ransa yace
"Na lura kamar harda dankali ya akayi aka dafa abinci yayi yawa haka?"
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍🏽 *~KUNDIN QADDARATA~*✍🏽
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
_______________________
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*hasbiyallahu la'ilaha illa huwa,alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim*
_________________________
0⃣7⃣
Hannunta riqe kan qugunta tace
"Dankali ne ta barmin ya huce,ni kuma ban iya ci ba,abinci rana kuma gaskiya bazan zauna qanwar qanwata tana dafa abinci tana bani ba,bayan ba cewa nayi bazan iya ba", shiru yayi yana ci gaba da kallonta zuciyarsa na quna,da qyar ya samu ya hadiye wani abu mai zafi a qirjinsa sannan ya gyada bayan wani tunani da yayi
" yayi kyau"kawai ya fada sannan ya ratsa ta tsakaninsu ya fice cikin bacin rai.
Sa kai sumayya tayi itama tana shirin bin bayansa
"Banza munafuka,idan ma ke kika nuna masa an gaya miki wani abun zai min" bata kulata ba tayi ficewarta ta koma dakinta,tana kammala sallar isha'i ta tura qofarta tayi kwanciyarta.
Washe gari shi ya shigo ya tada ta sallah,ta miqe tana mutstsuka idanunshi a kanta,sam bata ma ji kiran sallahr ba yau
"Ki tashi haka kiyi sallar asuba" ya fada yana qare mata kallo ta cikin rigar baccinta wadda tayi mata kyau
"Kinyi kyau sosai my sumy" ya fada sanda take qoqarin saukowa daga kan gadon,sai ta waiwayo ta dubeshi,dan qaramin murmushi ta sakar masa wanda yaso rudashi,ya qarasa inda take tsaye tana zura hijab dinta don fita waje tayi alwala,ya janyota da baya ya rungumeta yana rada mata
"Nayi missing dinki sumy ta" sai ta zare daga jikinsa ta waiwayo tana dubanshi idanunta a waje,ta maida su kana ta langabe kai
"Kai ya mukhtar,ni ban fafi haka ba sai kai dake da amarya?" Baice komai ba sai wani guntun murmushi da ya saka ya sanya kai yana ficewa tare da ce mata ta fito tayi salla.
Yauma kamar jiya ta fito ta kammala aikinta,saidai sabanin jiyan yau a bude taga dakinsa da alama yana ciki,saidai bata san ko me yake yi ciki ba,tana fitowa daga wanka sukayi kacibus,ya zuba mata ido yana dubanta
"Yanzu sumayya ko ruwan wanka ma an daina bani?" Ya fada murya a karye
"Ba haka bane ya mukhtar,na dauka aikin amarya ne wannan ko,amma kayi haquri akwai wani da na dora zan zuba a flask bari na juye maka" ta fada tana shigewa zuwa kitchen din da sauri.
Tare suka karya yauma,saidai bai aikata kiran fa'iza ba da kansa ya gaya mata tazo zasu karya ya juya ya fito,saidai har suka gama karyawar bata fito din ba,har ya fita daga gidan.
Tana kwance kan doguwar kujerar falonta tana hutawa taji sallamar anty dije,da sauri ta sauko daga kujerar tana amsawa don ko da wasa fa'iza wadda tafi maqotaka da qofa bata yi kuskuren amsawa ba.
Rungume anty dije qanwar maman nata tayi tana mata sannu da zuwa kana suka wuce dakinta,bayan gaishe gaishe da tambayarta zaman gidan ta gaya mata komai lafiya suka shiga hira,lokaci lokaci ta dinga tashi tana duba girkinta na rana da ta dora.
Kammalawarta yayi dai dai da lokacin sallah,saboda haka anty dije tace sai tayi sallah kafin taci abincin,tare suka fito anty dije tayi bakin famfo ita kuma ta nufi kitchen don gama kwashe abincin.
A bakin qofar kitchen sukayi kacibus da fa'iza na shirin fitowa ita kuma na qoqarin shiga,hannun fa'izar riqe da qatuwar kula da ta gama shaqewa da abincin da ta girka wanda a zahiri ko yara gareta yafi qarfinsu su duka balle cikinta ita daya,harara ta galla mata kana cikin daga murya tace
"Gafara malama na wuce,da wani idonta kamar jiqaqqiyar aya" rabe mata tayi tazo ta wuce fuuu tamkar guguwa cike da tsoro sumayya ta bita da kallo.
Duk a idanun anty dijen haka ya faru,ta kada kai cike da takaici ta wuce bandakin ta daura alwalar.
Tana saka hijabin sallarta sumayyan ta shigo dakin dauke da coolers din abincin,tun kafin ta saukesu anty dije ta finciki hannunta tayi bedroom dinta da ita,gefan gado ta zaunar da ita kana ta zauna kusa da ita suna fuskantar juna,cike dabacin rai ta tsareta da ido sannan ta soma magana
"Kar dai kice min sumayya tsoron kishiya kike?,kada ki gayan cewa kin fara nuna mata cewa kina tsoronta?" Da idanu sumayyan ke bin anty dijen cikin sanyi jiki.
"Wai dama wannan ce kishiyar taki?
Cab di wannan ai ma'aikaciya kurum kika samu
Lallai ai wannan banga abun kishi ba
Ke irinsu fa sunfi iya tsiya wallahi,kada ki soma cewa zaki sakar mata fuska balle ta rainaki,ki dasa mata tsoronki,bada umarni ne kawai tsakaninku
Wallahi ki bautar da shegiya,ki mori bati" take taji jikinta ya kama rawa gabanta ya shiga faduwa,lallai ba shakka suna iya dukanta,haka zuciyarta ta dinga raya mata,zuciyarta tsoro fal irin na yarinta,su kamsu suna sane suka dinga maganar don ta jisu,saboda su dasa tsoro cikin zuciyarta.
Kitchen din ta tattara ta koma tana ci gaba da ayyukanta,sai dai har yanzu tsoron bai saketa ba,addu'a ta dinga yi cikin zuciyarta hakan ya sanya ta dan samu nutsuwa.
Tana gab da kammala girkin fa'iza ta shigo kitchen din ita da daya daga cikin baqin nata tana fadin
"Ga bangare na nan,ki dafa duka abinda kuka ga ya muku yadda zai isheku" sumayya ta waiwayo tana dubanta
"Amma amarya har da ku nayi abincin fa zaya ishemu duka,ina ga idan aka dafa wani zaiyi yawa" juyowa itama tayi ta zabga mata wata harara sannan ta nunata da yatsa
"Ina cewa ko awa biyu ba'a yi ba da yi miki maganar ki guji shiga sabgata ba ko,ke har kin isa kina sa'ar qanwata ki dinga dafawa kina bani iya limit din da kika ga dama ina ci?,kin shirya cin na jaki kenan,don wallahi jibgarki zanyi a gidan nan banza juya kawai" sai ta dauke kanta daga garesu ta maida kan girkinta,abun mamaki sai kalmar juya yau tayi mata zafi,karo na farko kenan da ta taba jin hakan.
Tana jinta ta gama gayawa baquwar tata abinda za'ayi ta fice,bakin fanfo ta wuce ta tari ruwa ta shiga wanka don sai yanzu ta samu damar yin.
Tana kammala girkin ta zubawa mukhtar nashi,ta zuba nasu fa'izan ta aza a bangaren kantarta ta dibi wanda zata ci ta shige daki abinta,bata sake fitowa ba har suka gama tsiyar da zasuyi suka tafi wajen qarfe biyar na yamma,a sannan ta fito ta shiga kitchen don dora ruwan wanka.
Tamkar ba'a taba guara kitchen din ba haka suka lalatashi,ga uban abinci nan da suka dafa sun kasa cinyeshi cikin tukunya a bude,kwanukan duka vikin sink din fa'iza gaje gaje,hatta wanda ta ajjiye musu sun cakalkala shi sun bar cooler rabi a bude rabi a rufe.
Ranta taji ya baci karo na farko,ta tsani almubazzaranci da abinci,saboda tana da imamin abinda ka raina shi wani ke nema yasa a bakin salatinsa amma ya gagareshi,to don me kai don Allah ya baka zaka wulaqanga,bayan ya baka ne ba don kafi kowa ba.
Bata gaji ba bayan ta dora ruwan ta soma tattara kitchen din,ta gyara ko ina fes,saidai batasan ya zatayi da abincin ba tun kafin mukhtar ya gani yaji babu dadi,ita ba leqe take ba kuma yaro gidan bare ta samu almajiri ta bashi,dole ta jira dan aike yazo.
Ruwanta na zafi ta juye ta shiga wanka,can ma sai da ta tsaya ta gyara,sam bata qaunar taga guri ko yaya ya sauya yanayi.
Taji qarar babur dinsa sanda take maida kaskon turaren wuta kitchen,sanin cewar gidan a bude yake ba kamar sanda tana ita daya ba saboda haka ta toge a tsakar gidan tana jiran shigowarsa.
Cikin mintuna ya qaraso tsakar gidan,tana murmushi ta qarasa inda yake tana niyyar karbar jakarsa,sai ya bude hannayensa ya kai mata runguma sai ta goce tana murmushi tare da kallon qofar dakim fa'iza,qasa qasa da murya tace
"Bamu kadai bane fa a gidan" ta miqa hannu ta karbi kayan hannun nasa,sai ya kalleta yana turbune fuska
"Haka kawai tun yau an fara shiga haqqina,ai shikenan" yayi maganar yana wucewa dakinsa ta bishi a baya tana masa gwalo.
Har ta kammala kintsa abinda ya shigo da shi babu fa'iza babu alamarta,sai da ta gama zata fita daga dakin sukayi kacibus da fa'izan na shigowa,harara ta balla mata,gefe ta matsa ta raba ta kawai ta wuce.
Tunda ta gabatar musu da abinci tayi alwalar sallar magariba shigewarta daki,bata sake fitowa ba sai da taji mukhtar na qwala mata kira,ta miqe a hankali ta gyara daurin dankwalinta ta amsa tana fitowa.
A kitchen ta tadda shi tsaye ransa bace yana qarewa himilin abincin kallo,gefe guda kuma ga dankali da qwai da fa'izan ta soya a wulaqance cikin cooler ba'a idasa cinye shi ba,ya dago idanunsa daga kallon coolers din ya maida su ga sumayya,da hannu yayi mata nuni
"Me wannan?,meye haka sumayya?" A ladabce tace
"Nima ban sani ba ya mukhtar saidai ka tambayi amarya" baiyi musun hakan ba tunda a gefanta yaga tarin coolers din,ya daga murya ya qwala mata kira,ta shigo kitchen din sanye da hijab
"Gani" ta fada tana kallonshi.
Ya kalli kayan ya kalleta sannan yace
"Wannan na waye?"
"Na baqin da nayi ne" ya hadiye wani takaici saboda yadda tayi maganar cikin halin ko in kula da nuna rashin muhimmancin laifinta,wacce iriyar yarinya ce ita,yinin farko kenan a gidan mijinta?,yayi qoqarin danne bacin ransa yace
"Na lura kamar harda dankali ya akayi aka dafa abinci yayi yawa haka?"
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍🏽 *~KUNDIN QADDARATA~*✍🏽
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
_______________________
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*hasbiyallahu la'ilaha illa huwa,alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim*
_________________________
0⃣7⃣
Hannunta riqe kan qugunta tace
"Dankali ne ta barmin ya huce,ni kuma ban iya ci ba,abinci rana kuma gaskiya bazan zauna qanwar qanwata tana dafa abinci tana bani ba,bayan ba cewa nayi bazan iya ba", shiru yayi yana ci gaba da kallonta zuciyarsa na quna,da qyar ya samu ya hadiye wani abu mai zafi a qirjinsa sannan ya gyada bayan wani tunani da yayi
" yayi kyau"kawai ya fada sannan ya ratsa ta tsakaninsu ya fice cikin bacin rai.
Sa kai sumayya tayi itama tana shirin bin bayansa
"Banza munafuka,idan ma ke kika nuna masa an gaya miki wani abun zai min" bata kulata ba tayi ficewarta ta koma dakinta,tana kammala sallar isha'i ta tura qofarta tayi kwanciyarta.
Washe gari shi ya shigo ya tada ta sallah,ta miqe tana mutstsuka idanunshi a kanta,sam bata ma ji kiran sallahr ba yau
"Ki tashi haka kiyi sallar asuba" ya fada yana qare mata kallo ta cikin rigar baccinta wadda tayi mata kyau
"Kinyi kyau sosai my sumy" ya fada sanda take qoqarin saukowa daga kan gadon,sai ta waiwayo ta dubeshi,dan qaramin murmushi ta sakar masa wanda yaso rudashi,ya qarasa inda take tsaye tana zura hijab dinta don fita waje tayi alwala,ya janyota da baya ya rungumeta yana rada mata
"Nayi missing dinki sumy ta" sai ta zare daga jikinsa ta waiwayo tana dubanshi idanunta a waje,ta maida su kana ta langabe kai
"Kai ya mukhtar,ni ban fafi haka ba sai kai dake da amarya?" Baice komai ba sai wani guntun murmushi da ya saka ya sanya kai yana ficewa tare da ce mata ta fito tayi salla.
Yauma kamar jiya ta fito ta kammala aikinta,saidai sabanin jiyan yau a bude taga dakinsa da alama yana ciki,saidai bata san ko me yake yi ciki ba,tana fitowa daga wanka sukayi kacibus,ya zuba mata ido yana dubanta
"Yanzu sumayya ko ruwan wanka ma an daina bani?" Ya fada murya a karye
"Ba haka bane ya mukhtar,na dauka aikin amarya ne wannan ko,amma kayi haquri akwai wani da na dora zan zuba a flask bari na juye maka" ta fada tana shigewa zuwa kitchen din da sauri.
Tare suka karya yauma,saidai bai aikata kiran fa'iza ba da kansa ya gaya mata tazo zasu karya ya juya ya fito,saidai har suka gama karyawar bata fito din ba,har ya fita daga gidan.
Tana kwance kan doguwar kujerar falonta tana hutawa taji sallamar anty dije,da sauri ta sauko daga kujerar tana amsawa don ko da wasa fa'iza wadda tafi maqotaka da qofa bata yi kuskuren amsawa ba.
Rungume anty dije qanwar maman nata tayi tana mata sannu da zuwa kana suka wuce dakinta,bayan gaishe gaishe da tambayarta zaman gidan ta gaya mata komai lafiya suka shiga hira,lokaci lokaci ta dinga tashi tana duba girkinta na rana da ta dora.
Kammalawarta yayi dai dai da lokacin sallah,saboda haka anty dije tace sai tayi sallah kafin taci abincin,tare suka fito anty dije tayi bakin famfo ita kuma ta nufi kitchen don gama kwashe abincin.
A bakin qofar kitchen sukayi kacibus da fa'iza na shirin fitowa ita kuma na qoqarin shiga,hannun fa'izar riqe da qatuwar kula da ta gama shaqewa da abincin da ta girka wanda a zahiri ko yara gareta yafi qarfinsu su duka balle cikinta ita daya,harara ta galla mata kana cikin daga murya tace
"Gafara malama na wuce,da wani idonta kamar jiqaqqiyar aya" rabe mata tayi tazo ta wuce fuuu tamkar guguwa cike da tsoro sumayya ta bita da kallo.
Duk a idanun anty dijen haka ya faru,ta kada kai cike da takaici ta wuce bandakin ta daura alwalar.
Tana saka hijabin sallarta sumayyan ta shigo dakin dauke da coolers din abincin,tun kafin ta saukesu anty dije ta finciki hannunta tayi bedroom dinta da ita,gefan gado ta zaunar da ita kana ta zauna kusa da ita suna fuskantar juna,cike dabacin rai ta tsareta da ido sannan ta soma magana
"Kar dai kice min sumayya tsoron kishiya kike?,kada ki gayan cewa kin fara nuna mata cewa kina tsoronta?" Da idanu sumayyan ke bin anty dijen cikin sanyi jiki.