Sashe 86
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Alhamdulillah,Alhamdulillah" ya fara cewa
"Wato a yau labari ya iskemu gwamnatin tarayya ta aiko da takarda ma'aikatarmu,ta zabemu mu goma zamu tafi london bayan sallahn nan mai zuwa da sati daya,zamu qaro karatu don samun qwarewa kan aikinmu na tsawon shekara guda" ya fada yana sauke numfashi,duk sai fuskokinsu suka sauya,kowa da abinda ya fara yawo cikin zuciyarsa,suna wassafa yadda zai tafi ya barsu da yadda zasuyi kewarsa,dariyan da ya saki ita ta maido hankalinsu kanshi
"Jibi fuskansu,to gwamnati ta bamu daman tafiya da iyalanmu amma kada su wuce mutum hudu,shine babbar matsalar,gashi mu mun kai mu shida,tunani daya wa za'a bari da wa za'a tafi?" Shuru dakin ya dauka,murna ta soma komawa ciki,kowa na zulumin kada ace shi za'a cire,banda sumayya da farinciki ya mamayeta zata koma kano kenan har tsawon shekara daya,don dama ko a mafarki bata zaci ma zata bar state dinta ba balantana akai ga qasarta,ganin ba wanda yace komai sai sumayyan tayi gyaran murya don fidda abinda ke cikinta,dubanta uncle farouq yayi yace
"Ummm,me zaki ce?" A ladabce tace
"Dama uncle.....cewa nayi.....ni mai zai hana a cireni a lissafi sai na koma kano kafin dawowar taku?"
"Shawara bata karbu ba" anty dije ta fada kanta tsaye,sai ya saki dariya yana kallon sumayya
"To kinji abinda antynki tace" yana maganar tare da mai da hankalinsa kan anty dije
"To ke hajjaju mai zai hana cikin taskarki din nan da ake boyo ki dauki nauyinmu baki daya?" Ya fada cikin zolaya wanda hakan ya sanyasu dariya baki dayansu,sai da suka nutsa sannan yace
"Ni a binda nake gani,hafiz,kai zakayi haquri saboda karatunka a yanzu yake buqatar nutsuwa da dagewa,kai zamu bari a nan garin,sumayya kuma kema 'yar mu ce,kinga kuwa mai 'ya mace bazai dinga barinta wani gu ba,ni zan yi mata passport da visa a kudina,shikenan madam?"murmushi ta saki
" yayi yallabai,mun gode Allah ya saka da alkhairi ya qara arziqi"hafiz wanda sam baiji dadi ba har cikin ranshi,amma da yake yarone mai hankali da haquri,da wuya ka gane bacin ranshi sai yace
"A wanne gida abba Zan zauna?"
"Duk inda ka zaba,ko gidan inna(kakarsu da yake nan ya dawo da ita,ba wata tazara bace mai nisa tsakaninsu),ko gidan baabaa prof,kayi haquri kaji hafiz,girman kenan kaji?"
"Ba komai abba" ya fada,sai ya baiwa antu dije tausayi
"Ni har ka tunan ma abban laila,ina zuci zuci sukai sumayya ta gaidata,innan tace wai ba zata iya gane sumayyan yanzu ba"
Yana miqewa yace
"Kinsan tsufa sai a hankali,ai babu damuwa ko zuwa gobe ko jibi sai suje"
"Allah ya kaimu" injita,miqewa hafiz din yayi yabi bayan abban nasa da ya kirashi yace yazo ya karbi wani abu,take falon ya sarqe da murna,laila anata wassafa kai a jirgi,sumayya na dubanta tana dan murmushi duk da hankalinta ya kasu kashi biyu,ran qwashi anty dije ta zuba mata tace kota nutsu ko ta saka a cire sunanta a saka na hafiz take ta kame bakinta duk da bata fasa mutsu mutsun murna ba.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽[1/9, 7:24 AM] +234 807 885 3729: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
5⃣8⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*KO KUNSAN ACIKIN 'YAN WUTA WAYE MAI QANQANUWAR AZABA MAFI SAUQI?,WANDA AKA FI SAUQAQAWA??*
*Shine wanda za'a sanya garwashin wuta a tafin qafafunsa guda biyu,kowanne tafi daya garwashi daya,sai qwaqwalwarsa ta dinga tafasa*
*ALLAHUMMA AJIRNA MINANNAR*
__________________________________
Falon anty dije ta basu tana fita laila ta dora daga inda ta tsaya,har gwada irin shigar da zata dinga yi take idan suka tafi,sumayya na gefe tana kallonta tana dariya,can qasan ranta kuwa tana ta jujjuya maganar,wai itace zata wata qasa wata uwa duniya a jirgi har london?.
Suna haka hafiz ya fito daga wajen uncle farouq,fuskarsa qunshe da murmushi hannunsa dauke da laptop sabuwar qar,idanun laila suka fara kaiwa kai
"Laaah,ya hafiz sabuwar laptop abba yayi ne?"
"Wannan ba ta abba bace,tawa ce wanda ba za'a london da shi ba" ya fada yana zama tare da budeta ya kunna,tuni laila aka fara raba ido,ta matso kusa da shi
"Da gaske kake ya hafiz" hararta yayi
"Da da wasa nake miki" shiru tayi sannan daga bisani tace
"Allah ko nima na fasa zuwan ne a siya min,kada muje mu dawo dadi ya qare kai kuma ga abarka nan kama mora?" Dariya ta qwacewa sumayya,tana niyyar cewa wani abu anty dije itama ta fito daga dakin hannunta dauke da wata laptop dim,gefansu sumayyan ta zauna tana kallon hafiz
"Tofa,an samu nayi ko?" Murmushi yayi kawai yana danne dannensa dadi ya cikashi,sumayya ta miqawa laptop din tana cewa
"Ungo wannan" amsa tayi tana duban antyn
"Daki zan kai miki?"
"A'ah taki ce,abba laila ya siya miki yace zai miki bayani,akwai abinda ya shirya miki kan bunqasar karatunki yana so kiyi karatu ne da ita,idan mun tafi ina tsammanin akwai makaranta da zai sama miki da zaki koyi karatu ma shekara gudan,nasan baki da matsala ta karatu da rubutu duka kin iya,hakanan turancinki ba laifi zaki iya karantawa ki fahimci wasu abubuwan,fahimtar sosai da maidawa yadda ya kamata ne kawai matsalarki" qamewa tai a gun tana mamaki,to ita ya zata iya da wannan aba da uncle din ya mallaka mata,kasa magana tayi har sai da laila ta saki dan ihu tana karbarta daga hannunta
"Wayyo!,muma munyi computer,ya hafiz ka daina mana kallon banza" cikin sanyin murya da sake gasgata qaunarta da anty dije tace
"Anty na rasa wacce iriyan godiya zan muku,na gode na gode Allah ya saka muku da alkhairi,ya biya muku dukkan buqata ya jiqan magabatanku,ya hada kan zuriyyarku baki daya"
"Amin" anty dijen ta amsa tana shigewa ciki.
Da sauri laila ta miqe ta jona mata chargy hadu da kunnata,tana da rawar kai hakan ya sanya ta iya laptop din kamar wadda ako koyawa,don suna game sosai a cikin ta muhsina daya daga cikin qawayenta jikokin gidan baabaa prof,nan ta fara duba games din ta ta tarar a ciki,ta zabi daya ta fara bugawa minal ta matso tana kallo.
Daga bakin qofa akayi sallama,dukkansu hankalinsu na kan laptop din sai sumayua wadda ta amsa yana waiwayowa,amira ce ke shigowa fuskarta qunshe da murmushi,sanye take da black gown brided tube midi mai adon zane orange a jiki mai dogon hannu,kanta yane da mayafi medium orange haka plate shoes dinta,hannunta riqe da wayarta,fuskarta ba makeup saidai akwai alamun hoda da lipstic,bayanta wata matashiya ce,sanye da baqin skert da t.shirt ruwan omo dukkansu na yadi,sai dan madaidaicin hijab dake wuyanta,kallon farko zaka gane 'yar aiki ce,eh tana daya daga cikin ma'aikatan gidan baabaa prof,qarasowa tayi cikin falon wanda hakan ya ankarar da su laila
"Anty amira ina wuni" suka gaisheta baki dayansu ta amsa tana zama gefan sumayya
"Kin ganni da daddare ko?" Murmushi kawai tayi tana janyo lemo da ruwa nata wanda tun dazun bata sha ba da suka gama cin abinci ta ajjiye gaban amiran tana cewa
"Bismillah"
"Um_um,a qoshe nake,shopping naje nayo sai nace bari na shigo,ina so dama na baki haquri ne kan abunda ya faru dazu" kusan ta mance ma ma ya farun
"Mefa?" Sumayyan ta tambayeta
"Bigeki da antynmu tayi dazu,kiyi haquri don Allah,antynmu ce saidai bata da kirki sam,kiyi haquri" murmushi ta kuma yi har fararen haqoranta na bayyana
"Babu komai,ai karo mukayi"kai amira ta girgiza
" duk da haka,nasan halinta ai,kiyi haquri"
"Bafa komai" ta sake maimaitawa,maida dubanta tayi ga wadda suka shigo din tare,tana tsaye har yanzu
"Ki zauna mana" sumayya tace mata,murmushi tayi tace
"No madam,na gode". Kan ta sake cewa komai wayarsu ta tafi da gidanka dake kitchen ta fara burari,laila ta subi khalipha
" jeka duba khalipha"kanta na ga laptop don bata son a mata game over,da sauri ya miqe ya shige kitchen din minti daya tsakani ya fito
"Anty sumayya ke ake nema" yana fada alqasim ya fado mata,fuska ta tsuke
"Kace bana nan"
"Yace don annabi ki daure ki daga" khaliphan dake tsaye bakin qofar kitchen din ya fada,goshinta ta dafe da tafin hannunta,bata so a hadata da ma'aiki taqi yin abu,amira ta miqe tana dubanta
"Kije ki amsa mana namecy,zan tafi sai da safe ki gaida umman khalipha" ta fadi tana murmushi
"Sai da safe ki gaida gida" sumayyan ta fadi itama tana miqewa,ita tayi kitchen su suka fice ita da mai aikinta.
Murya a sanyaye ya mata sallama,a dake ta amsa
"Bakisan halin da zuciyata ta fada sanadinki ba sumayya,please don Allah ki daure ki dinga daga wayata ko ba zaki ce min komai ba"shiru ta danyi ta rasa me zata ce da shi,zuwa yanzu yaci ace yayi zuciya ya bar nemanta
"me kake so nace mai kake buqata?"
"Yauwa beauty,a qalla ko gaisuwa ma ta wadatar" kusan wannan ne abinda abdur rahman ya gaya mata,gashi yana neman jefata cikin tarkon sabo da jin muryarsa,wannan wanne irin wayo ne,ba zata yarda ba kam
"Sai anjima" tace masa tana kife kan wayar ta fito daga kitchen din tana sauke numfashi,inda ta tashi nan ta koma ya zauna ta janyo wayarta tana laluban lambar mamanta tana son jin muryar abdallah.
****** ******** ********
"Wato a yau labari ya iskemu gwamnatin tarayya ta aiko da takarda ma'aikatarmu,ta zabemu mu goma zamu tafi london bayan sallahn nan mai zuwa da sati daya,zamu qaro karatu don samun qwarewa kan aikinmu na tsawon shekara guda" ya fada yana sauke numfashi,duk sai fuskokinsu suka sauya,kowa da abinda ya fara yawo cikin zuciyarsa,suna wassafa yadda zai tafi ya barsu da yadda zasuyi kewarsa,dariyan da ya saki ita ta maido hankalinsu kanshi
"Jibi fuskansu,to gwamnati ta bamu daman tafiya da iyalanmu amma kada su wuce mutum hudu,shine babbar matsalar,gashi mu mun kai mu shida,tunani daya wa za'a bari da wa za'a tafi?" Shuru dakin ya dauka,murna ta soma komawa ciki,kowa na zulumin kada ace shi za'a cire,banda sumayya da farinciki ya mamayeta zata koma kano kenan har tsawon shekara daya,don dama ko a mafarki bata zaci ma zata bar state dinta ba balantana akai ga qasarta,ganin ba wanda yace komai sai sumayyan tayi gyaran murya don fidda abinda ke cikinta,dubanta uncle farouq yayi yace
"Ummm,me zaki ce?" A ladabce tace
"Dama uncle.....cewa nayi.....ni mai zai hana a cireni a lissafi sai na koma kano kafin dawowar taku?"
"Shawara bata karbu ba" anty dije ta fada kanta tsaye,sai ya saki dariya yana kallon sumayya
"To kinji abinda antynki tace" yana maganar tare da mai da hankalinsa kan anty dije
"To ke hajjaju mai zai hana cikin taskarki din nan da ake boyo ki dauki nauyinmu baki daya?" Ya fada cikin zolaya wanda hakan ya sanyasu dariya baki dayansu,sai da suka nutsa sannan yace
"Ni a binda nake gani,hafiz,kai zakayi haquri saboda karatunka a yanzu yake buqatar nutsuwa da dagewa,kai zamu bari a nan garin,sumayya kuma kema 'yar mu ce,kinga kuwa mai 'ya mace bazai dinga barinta wani gu ba,ni zan yi mata passport da visa a kudina,shikenan madam?"murmushi ta saki
" yayi yallabai,mun gode Allah ya saka da alkhairi ya qara arziqi"hafiz wanda sam baiji dadi ba har cikin ranshi,amma da yake yarone mai hankali da haquri,da wuya ka gane bacin ranshi sai yace
"A wanne gida abba Zan zauna?"
"Duk inda ka zaba,ko gidan inna(kakarsu da yake nan ya dawo da ita,ba wata tazara bace mai nisa tsakaninsu),ko gidan baabaa prof,kayi haquri kaji hafiz,girman kenan kaji?"
"Ba komai abba" ya fada,sai ya baiwa antu dije tausayi
"Ni har ka tunan ma abban laila,ina zuci zuci sukai sumayya ta gaidata,innan tace wai ba zata iya gane sumayyan yanzu ba"
Yana miqewa yace
"Kinsan tsufa sai a hankali,ai babu damuwa ko zuwa gobe ko jibi sai suje"
"Allah ya kaimu" injita,miqewa hafiz din yayi yabi bayan abban nasa da ya kirashi yace yazo ya karbi wani abu,take falon ya sarqe da murna,laila anata wassafa kai a jirgi,sumayya na dubanta tana dan murmushi duk da hankalinta ya kasu kashi biyu,ran qwashi anty dije ta zuba mata tace kota nutsu ko ta saka a cire sunanta a saka na hafiz take ta kame bakinta duk da bata fasa mutsu mutsun murna ba.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽[1/9, 7:24 AM] +234 807 885 3729: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
5⃣8⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*KO KUNSAN ACIKIN 'YAN WUTA WAYE MAI QANQANUWAR AZABA MAFI SAUQI?,WANDA AKA FI SAUQAQAWA??*
*Shine wanda za'a sanya garwashin wuta a tafin qafafunsa guda biyu,kowanne tafi daya garwashi daya,sai qwaqwalwarsa ta dinga tafasa*
*ALLAHUMMA AJIRNA MINANNAR*
__________________________________
Falon anty dije ta basu tana fita laila ta dora daga inda ta tsaya,har gwada irin shigar da zata dinga yi take idan suka tafi,sumayya na gefe tana kallonta tana dariya,can qasan ranta kuwa tana ta jujjuya maganar,wai itace zata wata qasa wata uwa duniya a jirgi har london?.
Suna haka hafiz ya fito daga wajen uncle farouq,fuskarsa qunshe da murmushi hannunsa dauke da laptop sabuwar qar,idanun laila suka fara kaiwa kai
"Laaah,ya hafiz sabuwar laptop abba yayi ne?"
"Wannan ba ta abba bace,tawa ce wanda ba za'a london da shi ba" ya fada yana zama tare da budeta ya kunna,tuni laila aka fara raba ido,ta matso kusa da shi
"Da gaske kake ya hafiz" hararta yayi
"Da da wasa nake miki" shiru tayi sannan daga bisani tace
"Allah ko nima na fasa zuwan ne a siya min,kada muje mu dawo dadi ya qare kai kuma ga abarka nan kama mora?" Dariya ta qwacewa sumayya,tana niyyar cewa wani abu anty dije itama ta fito daga dakin hannunta dauke da wata laptop dim,gefansu sumayyan ta zauna tana kallon hafiz
"Tofa,an samu nayi ko?" Murmushi yayi kawai yana danne dannensa dadi ya cikashi,sumayya ta miqawa laptop din tana cewa
"Ungo wannan" amsa tayi tana duban antyn
"Daki zan kai miki?"
"A'ah taki ce,abba laila ya siya miki yace zai miki bayani,akwai abinda ya shirya miki kan bunqasar karatunki yana so kiyi karatu ne da ita,idan mun tafi ina tsammanin akwai makaranta da zai sama miki da zaki koyi karatu ma shekara gudan,nasan baki da matsala ta karatu da rubutu duka kin iya,hakanan turancinki ba laifi zaki iya karantawa ki fahimci wasu abubuwan,fahimtar sosai da maidawa yadda ya kamata ne kawai matsalarki" qamewa tai a gun tana mamaki,to ita ya zata iya da wannan aba da uncle din ya mallaka mata,kasa magana tayi har sai da laila ta saki dan ihu tana karbarta daga hannunta
"Wayyo!,muma munyi computer,ya hafiz ka daina mana kallon banza" cikin sanyin murya da sake gasgata qaunarta da anty dije tace
"Anty na rasa wacce iriyan godiya zan muku,na gode na gode Allah ya saka muku da alkhairi,ya biya muku dukkan buqata ya jiqan magabatanku,ya hada kan zuriyyarku baki daya"
"Amin" anty dijen ta amsa tana shigewa ciki.
Da sauri laila ta miqe ta jona mata chargy hadu da kunnata,tana da rawar kai hakan ya sanya ta iya laptop din kamar wadda ako koyawa,don suna game sosai a cikin ta muhsina daya daga cikin qawayenta jikokin gidan baabaa prof,nan ta fara duba games din ta ta tarar a ciki,ta zabi daya ta fara bugawa minal ta matso tana kallo.
Daga bakin qofa akayi sallama,dukkansu hankalinsu na kan laptop din sai sumayua wadda ta amsa yana waiwayowa,amira ce ke shigowa fuskarta qunshe da murmushi,sanye take da black gown brided tube midi mai adon zane orange a jiki mai dogon hannu,kanta yane da mayafi medium orange haka plate shoes dinta,hannunta riqe da wayarta,fuskarta ba makeup saidai akwai alamun hoda da lipstic,bayanta wata matashiya ce,sanye da baqin skert da t.shirt ruwan omo dukkansu na yadi,sai dan madaidaicin hijab dake wuyanta,kallon farko zaka gane 'yar aiki ce,eh tana daya daga cikin ma'aikatan gidan baabaa prof,qarasowa tayi cikin falon wanda hakan ya ankarar da su laila
"Anty amira ina wuni" suka gaisheta baki dayansu ta amsa tana zama gefan sumayya
"Kin ganni da daddare ko?" Murmushi kawai tayi tana janyo lemo da ruwa nata wanda tun dazun bata sha ba da suka gama cin abinci ta ajjiye gaban amiran tana cewa
"Bismillah"
"Um_um,a qoshe nake,shopping naje nayo sai nace bari na shigo,ina so dama na baki haquri ne kan abunda ya faru dazu" kusan ta mance ma ma ya farun
"Mefa?" Sumayyan ta tambayeta
"Bigeki da antynmu tayi dazu,kiyi haquri don Allah,antynmu ce saidai bata da kirki sam,kiyi haquri" murmushi ta kuma yi har fararen haqoranta na bayyana
"Babu komai,ai karo mukayi"kai amira ta girgiza
" duk da haka,nasan halinta ai,kiyi haquri"
"Bafa komai" ta sake maimaitawa,maida dubanta tayi ga wadda suka shigo din tare,tana tsaye har yanzu
"Ki zauna mana" sumayya tace mata,murmushi tayi tace
"No madam,na gode". Kan ta sake cewa komai wayarsu ta tafi da gidanka dake kitchen ta fara burari,laila ta subi khalipha
" jeka duba khalipha"kanta na ga laptop don bata son a mata game over,da sauri ya miqe ya shige kitchen din minti daya tsakani ya fito
"Anty sumayya ke ake nema" yana fada alqasim ya fado mata,fuska ta tsuke
"Kace bana nan"
"Yace don annabi ki daure ki daga" khaliphan dake tsaye bakin qofar kitchen din ya fada,goshinta ta dafe da tafin hannunta,bata so a hadata da ma'aiki taqi yin abu,amira ta miqe tana dubanta
"Kije ki amsa mana namecy,zan tafi sai da safe ki gaida umman khalipha" ta fadi tana murmushi
"Sai da safe ki gaida gida" sumayyan ta fadi itama tana miqewa,ita tayi kitchen su suka fice ita da mai aikinta.
Murya a sanyaye ya mata sallama,a dake ta amsa
"Bakisan halin da zuciyata ta fada sanadinki ba sumayya,please don Allah ki daure ki dinga daga wayata ko ba zaki ce min komai ba"shiru ta danyi ta rasa me zata ce da shi,zuwa yanzu yaci ace yayi zuciya ya bar nemanta
"me kake so nace mai kake buqata?"
"Yauwa beauty,a qalla ko gaisuwa ma ta wadatar" kusan wannan ne abinda abdur rahman ya gaya mata,gashi yana neman jefata cikin tarkon sabo da jin muryarsa,wannan wanne irin wayo ne,ba zata yarda ba kam
"Sai anjima" tace masa tana kife kan wayar ta fito daga kitchen din tana sauke numfashi,inda ta tashi nan ta koma ya zauna ta janyo wayarta tana laluban lambar mamanta tana son jin muryar abdallah.
****** ******** ********