Sashe 81
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sanda labari ya iske sumayyan sai jikinta yayi sanyi saidai a fuska bata nuna komai ba ko don darajar yaran dake ta munnar zata koma gidansu,ya zata iya rabuwa da mahaifarta?,inda ta taso tayi wayo ta gabatar da rayuwarta baki daya?,inda anan dukkan wani tarihi na rayuwarta ya samo asali ya kuma kafu?,zata bi anty dije amma bata jin zata iya zama a garin din din din,zainab ce ta zungureta tana fadin
"Wai nikam wacce iri ce ke yaya sumayya don Allah,ina ma nice anty dihe tace zan koma gurinta,wallahi da kinga yadda ake abu" harara ta watsa mata
"Yanzun ma ki gayawa Abdulmalik kin fasa aurensa sai kizo ayi musaya da ni ke ki bita ni na zauna" dariya ta tuntsire da ita,tana son taga yaya sumayyan tata na masifa,sai tayi mata wani iri saboda bata saba ba ba al'adarta bace
"Bazan iya ba wallahi,ni da abdul malik jini da hanta ne"
"Madalla" ta fada taba juyawa taci gaba da abinda take cikim zuciyarta tana musu kyakkyawan addu'a da fatan dacewa da rayuwar aure mai inganci ba irin tata ba data kasance farkonta zaqi,qarshenta madaci wanda har yau take fama da taunarsa dacin bai bar bakinta ba,har yau duk farincikin da take ji idan ta tuna mukhtar sai ya gushe,duk sukunin da take ciki idan ta tunashi sai ya tarwatse,ko a yanzun data yi wannan tunani sai da hawaye suka biyo kuncinta.
To sati daya anty dijen ke da niyyar yi,siyayya dama zasuyi kasancewar ba zasu sake dawowa kano ba sai bayan qaramar sallah,haka ta dinga zuwa tana daukan sumayyan suna shiga kasiwa siyayya,a kwanakin baki daya sumayya bata zama bata da sukuni,hakan ya sanya abdur rahman ko lukman babu mai sukunin ganinta,saidai kullum ta Allah saqonninsu na tafe ta ma'adanar saqonnin na wayarta,wani lokaci har da tarin misscall na kiran da bata daga ba,taso sumayyan ta dauki kayayyaki amma tace bata buqatar komai,data matsane ta yanki sababbin yadin hijabai da zasu kai mata har qasa ta bayar a dinka mata,anty dijen nata tsokanarta mai hijabai bqta ce komai ba ta dai yi dariya don ita a yanzun babu shigar dake mata dadi irin ta hijaban.
Ana ya jibi zasu tafi bayan sun dawo daga kasuwa,suba zaune falon anty dije sumayya na tayata hada kaya wayar anty dije daga hannunsu laila ta dauji ruri,da sauri lailan ta sauko saga kan kujera ta nufi anty dijen tana cewa
"Hajiya mama ce take kiranki"
"Kamar kuwa tasan suna raina" anty dijen ta fada tana karbat wayar,sumayya nata shirya kayan ita kuma na wayar har ta kammala tana fadin
"Komawa kasuwa ya kama mu fa gobe sumayya" tana zuge zif din jakar matafiya ta trolly ta dago kai ta dubeta
"Naji kamar dazu kince kin kammala siyayya ko kinyi mantuwa ne?,nikam ma gaji da shiga kasuwan nan wlh kinsan ban taba shiga kasuwa haka ba?"tana zama gefan kujera tace
"Nima kaina na gaji sumayya,amma hajiya mama ce tafi qarfin komai gunmu,ko abban laila sai da ya soma qorafi jiya wai kasuwannin kano zamy siye ne baki daya har yau bamu gama siyayya ba?" Ta qarashe tana dariya sumayya na tayata
"Amma idan nace masa hajiya mama ce nasan bazai hana ba,ki kwana nan kawai gobe sai muje,atamfofi take so supers zatayi barka"idanuwa sumayya ta zaro
"da super zatayi barka?"murmushi anty dije tayi
"hajiya mama ce fa?,akwai yin harkar girma" shiru sumayya tayi sai data gama ta ture jakar gabanta sannan tace
"Nikam bazan kwana a nan ba,ni da ku ganni sai randa zamu tafi ku biyo daukata,zanje na qarasa jin dumin tsohuwata" hararata anty dije tayi
"Kome zaki fada saidai ki fada an riga an bamu ke kuma kin badu,so kike kice zaki ji duminta kafin jibi mu rabaki da ita ko?" Dariya ta qyalqyale da ita
"Ni ba haka nake nufi ba anty"
"Koma hakanne gobe da yamma kizo muje"
"To" ta amsa tana dan miqewa saboda bayanta da ya qage,kiran abdur rahman ya katse mata hutun nata,da kamar ba zata daga ba sai kuma ta kasa
"Gimbiya sumayya,ni yanzu lallabawa nake,naga alama ganinki sai an cike foam"
"Baka fara cike foam din ba ka dai kusa ka fara cikewa" ta fada a zuciyarta,a fili kuwa sai tayi 'yar qaramar dariya data sanyashi lumshe iso saboda yadda sautin ya ratsashi
"Ko kadan,sabgogi ke sukayi yawa,ina tare da anty dije kasan jibi zata koma"
"Ayyah,amin gaisuwa gurinta don Allah,naso in shigo mu gaisa na fara kamun qafa saidai yanzun haka ina sokoto,baki ma sani ba saboda baki damu da ni ba" murmushi kawai tayi mishi,a ranar ta sake masa sun taba hira,hakan ya masa dadi sosai,itama sai ta danji dadi a ranta,saboda rabon tayi hira haka da wani har ta mance,sanda ta gama taga misscall din lukman kusan goma,bata bi ta kaiba ta kashe wayar,anty dije ce ta dinga tsokanarta kodai ta barta kanon kawai,murmushi tayi wanda baikai zuci ba,don har ga Allah bata son ayi mata maganar aure,sai magariba sannan ta koma gida.
IDAN NA SAMU LOKACI WATAQIL ANJIMA KU SAMU WANI,IDAN KUMA KUNJI SHIRU TO BAN SAMU DAMA BA.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
5⃣5⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wa lillahi Aaqibatul umur*
*qarshen al'amari mallakar Allah ne*
__________________________________
*WANNAN SHAFIN SADAUKARWA NE GAREKI*
*UMMU RAMLAT(meena slimzy novel group)*
Qarfe sha daya na safiya su Anty dije ta qaraso da motar su wadda drivern su ne zai ja motar kamar yadda suka zo,alhj farouq tuni shi ya riga su komawa saboda kira da ya samu daga wajen aikinsu.
Tuni aka sanya kayanta a mota saidai ta tsaya sallama da mama,hawaye ne ya balle mata sanda suke sallaman,dariya maman tayi
"Saikace wadda aka ce idan ta tafi ba zata dawo ba,jeki don Allah sunata jiranki kada ku bata lokaci a hanya" halima da zainab ne suka rakota har bakin motar,tana shirin shiga halima tace
"Yaya sumayya,me za'a cewa yaya abdur rahman idan yazo,baki sanar masa ba fa,sannan baki bar saqo ba"
"Ki fada masa duk abinda kika ga ya dace" dariya sukayi don sun fuskanci gatse take musu,tana shiga yaran suka fara raba gardama,kowa na fadin kusa da shi zata zauna,motar akwai yalwa,sit uku ne da ita harda gun mai tuqi na hudu,hakan ya sanya ta tattara ta koma sit din cab qarshe ita da laila da minal,khalifa da hafiz na sit na biyu,anty dije ita kadai na sit na uku wanda ke kusa da driver tana rubuce rubucenta da lissafi na siye siyen da tayi don ta taba kudinta sosai har ta so shiga kudin abban lailah shi yasa tace su barta tayi lissafi,saidai duk da ita daya ce a sit dinta hayaniyarsu bata barta tayi aikin da take so ba,sun cika motar da karadi sumayya na biye musu,duk da zuciyarta babu dadi amma haka ta dinga biye musu har suka hau kwalta sosai,minal ita ta fara bacci sannan hafiz da yake bashi da son hayaniya sosai,khalipha shima yabi sahu sai laila ta dinda dariya tana cewa
"Yauwa kwa qyalemu ni da anty sumayya ta muyi hirarmu",su biyu suka dinga hirarsu tafiyar tasu naci gaba da gangawarawa,kafin a kai zaria sai ya zamto motar babu kowa sai sumayya da anty dije wadda sai lokacin ta samu sukunin yin aikinta.
Suna shiga kaduna suka farka baki dayansu,nan anty dije ta sanya salihu direban nasu ya wuce da su wani gidan cin abinci (restaurant)da sukan tsaya suci abinci duk sanda zasu taho kano ko zasu koma abuja,cikin mintina qalilan suka isa da yake kamar kan hanya yake,sai da suka fara shiga masallacin dake daura da wajen suka bada farali sannan duk suka fito sumayya na dauke da minal take ta saje da 'yan garin,tun a hanya ta dinga qarewa yanayin garin kallo,akwai yawaitar mata masu dogon hijabi da niqab kamar nata,sai kuma qabilu data lura suna da wani kaso na musamman cikin garin,baka tafiya daya biyu baka gansu ba cikin irin nasu shigan,hakan ya sanya ta yiwa garin hasashen gari mai tarin mabanbantan qabilu da yare.
Table biyu suka kama kowanne nada kujeru uku uku,daya sumayya laila da minal,sau dayan kuma anty dije hafiz da khalipha,salihu kuma na can wajen wani tsohon abokinsa ya karbi nashi abincin yana ci suna hira.
Kowa cin abincinsa yake cikin kwanciyar hankali,saidai sam ita ta kasa cin nata,hasalima jinta take a takure tamkar ita kowa yake kallo saboda bata taba zama gu irin wannan taci abinci haka cikin guri dake cakude da maza da mata ba,ko da can ita mai kunya ce rashin sabo da rashin saurin sakin jiki,don haka minal kawai take ta bawa abincin idanuwanta na kan minal din duk motsin da take,don a tsarge take.
tunda ta shigo gun ya zuba mata na mujiya,sau biyu suna hada idanu yana jifanta da murmushi,hakan ya sanya ta saka hannunta ta maida niqabin fuskarta,duka anty dije na ankare da yadda take a takure,saidai bata san dalilinta na sakin niqab din ba,ta dai dauka rashin sabo ne na shiga irin wadan nan wuraren,laila ce ta dubeta tana dariya
"Wai anty sumayya anan din ma sai kin rufe fuskarki,wurin cin abinci ne fa kowa abinci yake ci,duba ki gani" ta fada tana waiwayawa tare da yi mata nuni da ido,sai itama lailan idanuwanta ya kai kansa,matashine wanda zaiyi shekara talatin da biyu,fari ne sosai,yana sanye da shadda ruwan madara dinkin yarbawa,kansa babu hula,kallo daya zaka masa kasan cewa hutu ya ratsa jikinsa,su uku ne saman teburinsu shi da wasu matasan da aqalla zasuyi shekaru daya,biyun cin abincinsu suke suna duba wayar da take hannun na kuaa da shi,sam basu ma lura da yanayin da dan uwansu ke ciki ba
"Anty sumayya,kinga wani sai kallonki yake ya sanki ne?" Laila ta fada cikin sigar gulma murya qasa qasa taba ranqwafowa kan teburin
"Ku da kuke wucewa ta gun baki sanshi ba sai ni da yau na fara zuwa" sumayya ta fadi tana gogewa minal baki da tissue bayan ta gama bata abincin
"Ku taso mu wuce ko?" Anty dije tace tana daukar minal don ta ragewa sumayya tayi gaba suka bita a baya,da kanta taje wajen biya da yake har sun saba da su sosai,tasa aka hado takeaway saboda sumayya don ta lura bata ci komai ba ta amsa sannan suka wuce.
"Wai nikam wacce iri ce ke yaya sumayya don Allah,ina ma nice anty dihe tace zan koma gurinta,wallahi da kinga yadda ake abu" harara ta watsa mata
"Yanzun ma ki gayawa Abdulmalik kin fasa aurensa sai kizo ayi musaya da ni ke ki bita ni na zauna" dariya ta tuntsire da ita,tana son taga yaya sumayyan tata na masifa,sai tayi mata wani iri saboda bata saba ba ba al'adarta bace
"Bazan iya ba wallahi,ni da abdul malik jini da hanta ne"
"Madalla" ta fada taba juyawa taci gaba da abinda take cikim zuciyarta tana musu kyakkyawan addu'a da fatan dacewa da rayuwar aure mai inganci ba irin tata ba data kasance farkonta zaqi,qarshenta madaci wanda har yau take fama da taunarsa dacin bai bar bakinta ba,har yau duk farincikin da take ji idan ta tuna mukhtar sai ya gushe,duk sukunin da take ciki idan ta tunashi sai ya tarwatse,ko a yanzun data yi wannan tunani sai da hawaye suka biyo kuncinta.
To sati daya anty dijen ke da niyyar yi,siyayya dama zasuyi kasancewar ba zasu sake dawowa kano ba sai bayan qaramar sallah,haka ta dinga zuwa tana daukan sumayyan suna shiga kasiwa siyayya,a kwanakin baki daya sumayya bata zama bata da sukuni,hakan ya sanya abdur rahman ko lukman babu mai sukunin ganinta,saidai kullum ta Allah saqonninsu na tafe ta ma'adanar saqonnin na wayarta,wani lokaci har da tarin misscall na kiran da bata daga ba,taso sumayyan ta dauki kayayyaki amma tace bata buqatar komai,data matsane ta yanki sababbin yadin hijabai da zasu kai mata har qasa ta bayar a dinka mata,anty dijen nata tsokanarta mai hijabai bqta ce komai ba ta dai yi dariya don ita a yanzun babu shigar dake mata dadi irin ta hijaban.
Ana ya jibi zasu tafi bayan sun dawo daga kasuwa,suba zaune falon anty dije sumayya na tayata hada kaya wayar anty dije daga hannunsu laila ta dauji ruri,da sauri lailan ta sauko saga kan kujera ta nufi anty dijen tana cewa
"Hajiya mama ce take kiranki"
"Kamar kuwa tasan suna raina" anty dijen ta fada tana karbat wayar,sumayya nata shirya kayan ita kuma na wayar har ta kammala tana fadin
"Komawa kasuwa ya kama mu fa gobe sumayya" tana zuge zif din jakar matafiya ta trolly ta dago kai ta dubeta
"Naji kamar dazu kince kin kammala siyayya ko kinyi mantuwa ne?,nikam ma gaji da shiga kasuwan nan wlh kinsan ban taba shiga kasuwa haka ba?"tana zama gefan kujera tace
"Nima kaina na gaji sumayya,amma hajiya mama ce tafi qarfin komai gunmu,ko abban laila sai da ya soma qorafi jiya wai kasuwannin kano zamy siye ne baki daya har yau bamu gama siyayya ba?" Ta qarashe tana dariya sumayya na tayata
"Amma idan nace masa hajiya mama ce nasan bazai hana ba,ki kwana nan kawai gobe sai muje,atamfofi take so supers zatayi barka"idanuwa sumayya ta zaro
"da super zatayi barka?"murmushi anty dije tayi
"hajiya mama ce fa?,akwai yin harkar girma" shiru sumayya tayi sai data gama ta ture jakar gabanta sannan tace
"Nikam bazan kwana a nan ba,ni da ku ganni sai randa zamu tafi ku biyo daukata,zanje na qarasa jin dumin tsohuwata" hararata anty dije tayi
"Kome zaki fada saidai ki fada an riga an bamu ke kuma kin badu,so kike kice zaki ji duminta kafin jibi mu rabaki da ita ko?" Dariya ta qyalqyale da ita
"Ni ba haka nake nufi ba anty"
"Koma hakanne gobe da yamma kizo muje"
"To" ta amsa tana dan miqewa saboda bayanta da ya qage,kiran abdur rahman ya katse mata hutun nata,da kamar ba zata daga ba sai kuma ta kasa
"Gimbiya sumayya,ni yanzu lallabawa nake,naga alama ganinki sai an cike foam"
"Baka fara cike foam din ba ka dai kusa ka fara cikewa" ta fada a zuciyarta,a fili kuwa sai tayi 'yar qaramar dariya data sanyashi lumshe iso saboda yadda sautin ya ratsashi
"Ko kadan,sabgogi ke sukayi yawa,ina tare da anty dije kasan jibi zata koma"
"Ayyah,amin gaisuwa gurinta don Allah,naso in shigo mu gaisa na fara kamun qafa saidai yanzun haka ina sokoto,baki ma sani ba saboda baki damu da ni ba" murmushi kawai tayi mishi,a ranar ta sake masa sun taba hira,hakan ya masa dadi sosai,itama sai ta danji dadi a ranta,saboda rabon tayi hira haka da wani har ta mance,sanda ta gama taga misscall din lukman kusan goma,bata bi ta kaiba ta kashe wayar,anty dije ce ta dinga tsokanarta kodai ta barta kanon kawai,murmushi tayi wanda baikai zuci ba,don har ga Allah bata son ayi mata maganar aure,sai magariba sannan ta koma gida.
IDAN NA SAMU LOKACI WATAQIL ANJIMA KU SAMU WANI,IDAN KUMA KUNJI SHIRU TO BAN SAMU DAMA BA.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
5⃣5⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wa lillahi Aaqibatul umur*
*qarshen al'amari mallakar Allah ne*
__________________________________
*WANNAN SHAFIN SADAUKARWA NE GAREKI*
*UMMU RAMLAT(meena slimzy novel group)*
Qarfe sha daya na safiya su Anty dije ta qaraso da motar su wadda drivern su ne zai ja motar kamar yadda suka zo,alhj farouq tuni shi ya riga su komawa saboda kira da ya samu daga wajen aikinsu.
Tuni aka sanya kayanta a mota saidai ta tsaya sallama da mama,hawaye ne ya balle mata sanda suke sallaman,dariya maman tayi
"Saikace wadda aka ce idan ta tafi ba zata dawo ba,jeki don Allah sunata jiranki kada ku bata lokaci a hanya" halima da zainab ne suka rakota har bakin motar,tana shirin shiga halima tace
"Yaya sumayya,me za'a cewa yaya abdur rahman idan yazo,baki sanar masa ba fa,sannan baki bar saqo ba"
"Ki fada masa duk abinda kika ga ya dace" dariya sukayi don sun fuskanci gatse take musu,tana shiga yaran suka fara raba gardama,kowa na fadin kusa da shi zata zauna,motar akwai yalwa,sit uku ne da ita harda gun mai tuqi na hudu,hakan ya sanya ta tattara ta koma sit din cab qarshe ita da laila da minal,khalifa da hafiz na sit na biyu,anty dije ita kadai na sit na uku wanda ke kusa da driver tana rubuce rubucenta da lissafi na siye siyen da tayi don ta taba kudinta sosai har ta so shiga kudin abban lailah shi yasa tace su barta tayi lissafi,saidai duk da ita daya ce a sit dinta hayaniyarsu bata barta tayi aikin da take so ba,sun cika motar da karadi sumayya na biye musu,duk da zuciyarta babu dadi amma haka ta dinga biye musu har suka hau kwalta sosai,minal ita ta fara bacci sannan hafiz da yake bashi da son hayaniya sosai,khalipha shima yabi sahu sai laila ta dinda dariya tana cewa
"Yauwa kwa qyalemu ni da anty sumayya ta muyi hirarmu",su biyu suka dinga hirarsu tafiyar tasu naci gaba da gangawarawa,kafin a kai zaria sai ya zamto motar babu kowa sai sumayya da anty dije wadda sai lokacin ta samu sukunin yin aikinta.
Suna shiga kaduna suka farka baki dayansu,nan anty dije ta sanya salihu direban nasu ya wuce da su wani gidan cin abinci (restaurant)da sukan tsaya suci abinci duk sanda zasu taho kano ko zasu koma abuja,cikin mintina qalilan suka isa da yake kamar kan hanya yake,sai da suka fara shiga masallacin dake daura da wajen suka bada farali sannan duk suka fito sumayya na dauke da minal take ta saje da 'yan garin,tun a hanya ta dinga qarewa yanayin garin kallo,akwai yawaitar mata masu dogon hijabi da niqab kamar nata,sai kuma qabilu data lura suna da wani kaso na musamman cikin garin,baka tafiya daya biyu baka gansu ba cikin irin nasu shigan,hakan ya sanya ta yiwa garin hasashen gari mai tarin mabanbantan qabilu da yare.
Table biyu suka kama kowanne nada kujeru uku uku,daya sumayya laila da minal,sau dayan kuma anty dije hafiz da khalipha,salihu kuma na can wajen wani tsohon abokinsa ya karbi nashi abincin yana ci suna hira.
Kowa cin abincinsa yake cikin kwanciyar hankali,saidai sam ita ta kasa cin nata,hasalima jinta take a takure tamkar ita kowa yake kallo saboda bata taba zama gu irin wannan taci abinci haka cikin guri dake cakude da maza da mata ba,ko da can ita mai kunya ce rashin sabo da rashin saurin sakin jiki,don haka minal kawai take ta bawa abincin idanuwanta na kan minal din duk motsin da take,don a tsarge take.
tunda ta shigo gun ya zuba mata na mujiya,sau biyu suna hada idanu yana jifanta da murmushi,hakan ya sanya ta saka hannunta ta maida niqabin fuskarta,duka anty dije na ankare da yadda take a takure,saidai bata san dalilinta na sakin niqab din ba,ta dai dauka rashin sabo ne na shiga irin wadan nan wuraren,laila ce ta dubeta tana dariya
"Wai anty sumayya anan din ma sai kin rufe fuskarki,wurin cin abinci ne fa kowa abinci yake ci,duba ki gani" ta fada tana waiwayawa tare da yi mata nuni da ido,sai itama lailan idanuwanta ya kai kansa,matashine wanda zaiyi shekara talatin da biyu,fari ne sosai,yana sanye da shadda ruwan madara dinkin yarbawa,kansa babu hula,kallo daya zaka masa kasan cewa hutu ya ratsa jikinsa,su uku ne saman teburinsu shi da wasu matasan da aqalla zasuyi shekaru daya,biyun cin abincinsu suke suna duba wayar da take hannun na kuaa da shi,sam basu ma lura da yanayin da dan uwansu ke ciki ba
"Anty sumayya,kinga wani sai kallonki yake ya sanki ne?" Laila ta fada cikin sigar gulma murya qasa qasa taba ranqwafowa kan teburin
"Ku da kuke wucewa ta gun baki sanshi ba sai ni da yau na fara zuwa" sumayya ta fadi tana gogewa minal baki da tissue bayan ta gama bata abincin
"Ku taso mu wuce ko?" Anty dije tace tana daukar minal don ta ragewa sumayya tayi gaba suka bita a baya,da kanta taje wajen biya da yake har sun saba da su sosai,tasa aka hado takeaway saboda sumayya don ta lura bata ci komai ba ta amsa sannan suka wuce.