Sashe 80
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 7 min read
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
5⃣4⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*Rabbukum a'alamu bima fi nufusikum*
*(haqiqa)ubangijinku shine mafi sani ga abinda yake cikin zukutanku*
_________________________________
A rude anty dije ta soma tambayarta
"Lafiya sumayya?,me yake faruwa?,ko wani ne ya mutu?" Ta jero mata tambayoyin baki daya,jin tayi shiru bata tanka ba ya sanyata itama shirun tana sauraren kukanta,ta tabbatar wata matsalarce ta taso mata haka jikinta ya bata,tausayin yarinyar take ji,sai yaushe ne zata fita daga matsala,sai data dauki a qalla minti goma sannan ta soma magana cikin karayar zuciya
"Anty,lukman da abdur rahman"
"Me ya samesu?"
"Anty......dukkaninsu sun dawo,kowanne so yake na aureshi,fisabilillahi anty ni bazan huta ba?,duka duka yaushe na soma samun nutsuwa?,anty bana buqatar sake wani auren yanzu,tsoro nake ji kada su nufi malam da maganar,idan malam ya umarceni anty bazan iya bijire masa ba" sai ta fashe da kuka,tsaki anty dijen tayi sannan tace
"Zancan banza,kema kin riga da kinsan cewa malam yasan haqqinki na hannunki yanzu,ke zaki zabawa kanki miji ko?,sannan tsakanin lukman da abdur rahman akwai wanda ya isa ya aureki ne bada amincewarki ba da zaki tadawa kanki hankali ki dinga zubda hawayenki?,duk wanda kika zubar a baya bai isheki bane sumayya?,ko so kike wani ciwon ya sokeki?,to nikam na gaji da ji da gani,kishirya da gaske idan nazi tare zamu koma,idan yaso naga wanda zai qara bata ranki" ta fada tana katse wayar.
Shiru tayi tana juya wayar a hannunta,ba haka taso anty dije tace ba shawarar yadda zata kubuce daga tsakanin da lukman da abdurrahman suka sanyata take so ta bata,amma da tayi tsai sai ta lura lallai babu hanyar da zata zille musun idan ba barin garin kanon zata yi ba kamar yadda anty dije tace,sai ta sauke ajiyat zuciya tana goge hawayenta,tana qiyasta idan ta bar kano koda na tsawon wata daya ne itama ta samu hutu,ta samu ta manta da wasu lamuran ta manta da damuwoyinta.
******* ******* *******
Washegari ta shirya don zuwa gidan yaya yahanasu ta dauko abdallah tunda duka duka saura kwana biyu anty dije tazo,tana tsaye a falon mama tana sanya hijabinta tare da yiwa mama sallama suka ji sallamar abdur rahman,kamar ta juya ta shige daki amma tasan idan tayi hakan kamar ta nunawa mama akwai wani lamari tsakaninsu irin wanda ya faru a baya,abinda bata da buri ko fatan kowa ya fahimta kenan
"Ina yini" sumayyan ta gaisheshi tana shirin ficewa bayan sun gaisa da mama
"Lafiya......ina zuwa haka?" Ya tambayeta yana dan dubanta,cikin hanzari ta soma sanya takalmanta tana bashi amsa
"Zan dauko abdallah he gidan ya yahanasu"
"Yauwa,nafi jin dadin tafiya,dama jiya da naje na yiwa abdallah alqawarin yoghourt" ya fada yana miqewa tsaye,kamar ta zura da gudu haka taji,take yanayin fuskarta ya sauya wanda tashin farko ya fahimci bata ji dadin shishshigin da ya mata ba,saidai sam bashi da damuwa matuqar zai kasance da ita,inda zata iya zata ce masa bata so amma idanuwan mama ya sanya ta kasa cewa komai
"Sai mun dawo mama"
"Allah ya kiyaye hanya ku gaida min yahanasun"maman ta fada ba don son ranta ba,don ba kasafai take barinsu suna shiga motocin gida ba koda na 'yan uwa ne,tafi ganewa su hau ta haya
"Zataji" inji zainab wadda ita ce 'yar rakiyar.
Gaban motar ya bude mata da kansa,sai da yaga ta shiga ta zauna sannan ya zagaya nashi mazaunin ya tashi motar suka tafu,shiru ya ratsa motar,babu mai magana tsakaninsu,sai ya sanya hannunshi ya dannan plate jikin redion motar,cikin sakanni lacture malamin dake cikin fefan ta fara tashi,ya daj qaro volume din sannan ya dauke hannayensa ya maida kan sitiyarin motar
"Nikam bansan wanne irin baqin jini ne da ni ba" ya fada qasa qasa yadda ita da shi ne kawai zasu iya jin me yake fadi,ta gefen ido ta kalleshi don ta tabbatar da ita yake ko kuwa,sai ta gane da ita din yake saboda yadda yake kallonta kadan kadan,shiru tayi bata da niyyar tankawa saboda bata fuskanci ma inda zaurancen nasa ya sa gaba ba
"Sumayya me nayi da jiya baki sona,yau ma kinqi karbata,ko na aikata miki wani laifi ne?,ko ina da wani aibu da ban cancanci a soni ba?" Ya tambayeta yana mai muradin jin amsarta
"Baka aikata komai ba,amma don son annabi mubar maganar nan,kada ka manta har yau jinyar zuciyata nake bata warke ba,ban kuma san ranar warkewarta ba" ta fadi tana duban gabanta ba tare da ta dubeshi ba.
Shuru yayi yana jin yadda ransa ya quntata,karo na farko da ya soma jin kishin nukhtar har cikin ransa,mukhtar jininsa ne wanda har ya mutu babu wani abu mara dadi da ya taba hadasu,hakan ya sanya bai sake tofa komai ba har suka iso gidan yaya yahanasun,tayi zaton zai shigo ne da ya ajjiyesu,sai taga ya juya kan motar yayi gaba.
A tsakar gida suka samu abdallan,yana ta wasa da dan qaramin keke da yaya yahansun ta siya masa,jamila na faman binsa tana sauya masa kayansa da yayi kaca kaca da su da miya amma yaqi yarda,ya maidata abar wasansa sai zagaye suke yana dariya,yana ganinta yayi cilli da keken ya taho a guje ya dafeta yana dariya,itama dariyar take,sai taji sanyi a cikin zuciyarta,yaya yahanasu da taji muryarsu ta fito cikin fara'a tana musu sannu da zuwa.
Ina ka saka ina ka ajjiye take tayi da su,kamar zata goya sumayyan,abdallah ya wani ajiye kumatu,abinda yakeso kawai yake cikin gidan,sai bayan sallar magariba sannan suka shirya tafiya,qeme me abdallah yace ba zai bisu ba,saidai sumayyan itama ta dauko kayanta ta zauna anan,dariya suka dinga yi,ganin haka ya sanya sumayyan tace a barshi,duk sanda ya gaji ya dawo.
Ga mamakinta suna fitowa ta tadda abdur rahman tsaye qofar gidan,qofa bude yana kallonta,ta fuskanci me yake nufi saboda haka babu musu ta shiga,zainab ma ta bude gidan baya ta shiga,sau daya rufe sannan taga ya shiga gidan,baifi mintina biyar ba ya fito suka tafi,har suka je gida baice uffan ba,ya saukesu ta masa godiya ta wuce,tana shirin kwanciya saqonshi ya shigo wayarta,saqo ne dake dauje da kalamai masu nuna tsantsar qauna,da nuna ba za'a rabu da abinda ake so ba,tana gama karantawa ta goge ta kwanta,tana ayyana ta kusa nesa da dukkan wadan nan rudanin.
****** ********* *****
*BAYAN KWANA BIYAR*
Anty dije suka iso kano ita da yaran da mai gidan baki daya,gidansu na da anan suke masauki duk sanda suka zo din,bata samu zuwa gidansu sumayyan ba sai bayan kwana biyu da zuwan nata.
Sha daya da rabi na rana suka iso baki dayansu,sun sauya baki daya daga anty dijen duka sunyi kyau da wata irin gogewa,kana ganinsu kasan kwanciyar hankali da hutu sun samu wajen zama,duk suna falon mama,maman da anty dije suna hirarsu ta zumunci,yaran duka sun kewaye sumayya suna ta bata labari,mutuniyar tata minar na zaune dare dare kan cinyarta,laila ce ta soma tambayar Abdallah wanda hakan ya janyo hankalin anty dije
"Nima fa ban ganshi ba" injita,murmushi mama tayi
"Mu zai nunawa 'yan ubanci ai,tunda yahanasu ta daukeshi kinga yaqi dawowa,uwar ma taje da kanta yaqi biyota" haba anty dijen ta riqe tana dariya
"Yanzun haka zamu tafi ki barshi a kano?" Tayi maganar ta sigar tambaya tana duban sumayya,dariya sumayya tayi
"Wai da gaske anty sai na bikin?,to idan naje ma kwana nawa ne zan dawo ai ba dadewa zanyi ba" dubanta anty dijen tayi cikin mamaki
"Wai meke damunki da baki son abuja ne kamar ana gutsurarki" tabe fuska tayi kamar qaramar yarinya
"Garin ne ni banjin dadinsa anty haka kurum" kanta ta dauke daga kan sumayyan tana cewa
"Sai kiyi kuma,mu me ya cimu?,"
"Yaya asama'u(sunan mama na asali)Allah yasa dai malam na gari,don tun yau nakeson sanar masa da sumayyan zan tafi,na lura kamar ku din a nan bata samun kwamciyar hankali da nutsuwar data dace,dama can baya kun yimim alqawarin bani ita kuma aure ya fado mata da wuri,kinga yanzu sai a cikamun alqawari na"dariya mama tayi tana cewa
"Malam yana nan ya fita ne taron bude wani sabon masallacin juma'a da aka gina,amma nan da biyar ko shida na yammaci zai dawo"
"To Allah ya dawo dashi lpy,ina nan har ya dawo"
"Amin" inji mama.
"Momy,wai anty da ita zamu tafi?" Khalipha ya fada cikin murna da doki yana dora hannunsa hannunshi kan cinyar anty dije
"In sha Allahu" ta bashi amsa,
"Yeeeeeyyyyyy" yaran suka sanya ihu baki daya har suka sanya sumayyan ta tuntsire da dariya duk da yadda jikinta yayi sanyi da zancan tafiyar tata.
Anty dije ko bata tafu din ba har sai da malam ya dawo,sanda ta tuna masa tsohon alqawarin da suka mata dariya ya saka sosai,don shi sam ya manta da maganar ma baki daya,shi kansa cikin yaransa yana son sumayya,tana da baiwa da wasu halaye na daban da ba kowa ke da su ba,amma babu yadda ya iya,tilas ya cika alqawarin da ya dauka duk da cewa tsoho ne,yace ya basu sumayya halak malak indai suna so,da yake gaban alhj farouq akayi shima yaji dadi sosai,har da shi a godiya,don shima yasan halayen sumayyan,ya tabbata ko zama tayi cikin yaransa zasu qaru da ita,hakanan zata taimaka ma matarsa zasu dinga ganin nasu na gida a kusa da su saji dadi.
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
5⃣4⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*Rabbukum a'alamu bima fi nufusikum*
*(haqiqa)ubangijinku shine mafi sani ga abinda yake cikin zukutanku*
_________________________________
A rude anty dije ta soma tambayarta
"Lafiya sumayya?,me yake faruwa?,ko wani ne ya mutu?" Ta jero mata tambayoyin baki daya,jin tayi shiru bata tanka ba ya sanyata itama shirun tana sauraren kukanta,ta tabbatar wata matsalarce ta taso mata haka jikinta ya bata,tausayin yarinyar take ji,sai yaushe ne zata fita daga matsala,sai data dauki a qalla minti goma sannan ta soma magana cikin karayar zuciya
"Anty,lukman da abdur rahman"
"Me ya samesu?"
"Anty......dukkaninsu sun dawo,kowanne so yake na aureshi,fisabilillahi anty ni bazan huta ba?,duka duka yaushe na soma samun nutsuwa?,anty bana buqatar sake wani auren yanzu,tsoro nake ji kada su nufi malam da maganar,idan malam ya umarceni anty bazan iya bijire masa ba" sai ta fashe da kuka,tsaki anty dijen tayi sannan tace
"Zancan banza,kema kin riga da kinsan cewa malam yasan haqqinki na hannunki yanzu,ke zaki zabawa kanki miji ko?,sannan tsakanin lukman da abdur rahman akwai wanda ya isa ya aureki ne bada amincewarki ba da zaki tadawa kanki hankali ki dinga zubda hawayenki?,duk wanda kika zubar a baya bai isheki bane sumayya?,ko so kike wani ciwon ya sokeki?,to nikam na gaji da ji da gani,kishirya da gaske idan nazi tare zamu koma,idan yaso naga wanda zai qara bata ranki" ta fada tana katse wayar.
Shiru tayi tana juya wayar a hannunta,ba haka taso anty dije tace ba shawarar yadda zata kubuce daga tsakanin da lukman da abdurrahman suka sanyata take so ta bata,amma da tayi tsai sai ta lura lallai babu hanyar da zata zille musun idan ba barin garin kanon zata yi ba kamar yadda anty dije tace,sai ta sauke ajiyat zuciya tana goge hawayenta,tana qiyasta idan ta bar kano koda na tsawon wata daya ne itama ta samu hutu,ta samu ta manta da wasu lamuran ta manta da damuwoyinta.
******* ******* *******
Washegari ta shirya don zuwa gidan yaya yahanasu ta dauko abdallah tunda duka duka saura kwana biyu anty dije tazo,tana tsaye a falon mama tana sanya hijabinta tare da yiwa mama sallama suka ji sallamar abdur rahman,kamar ta juya ta shige daki amma tasan idan tayi hakan kamar ta nunawa mama akwai wani lamari tsakaninsu irin wanda ya faru a baya,abinda bata da buri ko fatan kowa ya fahimta kenan
"Ina yini" sumayyan ta gaisheshi tana shirin ficewa bayan sun gaisa da mama
"Lafiya......ina zuwa haka?" Ya tambayeta yana dan dubanta,cikin hanzari ta soma sanya takalmanta tana bashi amsa
"Zan dauko abdallah he gidan ya yahanasu"
"Yauwa,nafi jin dadin tafiya,dama jiya da naje na yiwa abdallah alqawarin yoghourt" ya fada yana miqewa tsaye,kamar ta zura da gudu haka taji,take yanayin fuskarta ya sauya wanda tashin farko ya fahimci bata ji dadin shishshigin da ya mata ba,saidai sam bashi da damuwa matuqar zai kasance da ita,inda zata iya zata ce masa bata so amma idanuwan mama ya sanya ta kasa cewa komai
"Sai mun dawo mama"
"Allah ya kiyaye hanya ku gaida min yahanasun"maman ta fada ba don son ranta ba,don ba kasafai take barinsu suna shiga motocin gida ba koda na 'yan uwa ne,tafi ganewa su hau ta haya
"Zataji" inji zainab wadda ita ce 'yar rakiyar.
Gaban motar ya bude mata da kansa,sai da yaga ta shiga ta zauna sannan ya zagaya nashi mazaunin ya tashi motar suka tafu,shiru ya ratsa motar,babu mai magana tsakaninsu,sai ya sanya hannunshi ya dannan plate jikin redion motar,cikin sakanni lacture malamin dake cikin fefan ta fara tashi,ya daj qaro volume din sannan ya dauke hannayensa ya maida kan sitiyarin motar
"Nikam bansan wanne irin baqin jini ne da ni ba" ya fada qasa qasa yadda ita da shi ne kawai zasu iya jin me yake fadi,ta gefen ido ta kalleshi don ta tabbatar da ita yake ko kuwa,sai ta gane da ita din yake saboda yadda yake kallonta kadan kadan,shiru tayi bata da niyyar tankawa saboda bata fuskanci ma inda zaurancen nasa ya sa gaba ba
"Sumayya me nayi da jiya baki sona,yau ma kinqi karbata,ko na aikata miki wani laifi ne?,ko ina da wani aibu da ban cancanci a soni ba?" Ya tambayeta yana mai muradin jin amsarta
"Baka aikata komai ba,amma don son annabi mubar maganar nan,kada ka manta har yau jinyar zuciyata nake bata warke ba,ban kuma san ranar warkewarta ba" ta fadi tana duban gabanta ba tare da ta dubeshi ba.
Shuru yayi yana jin yadda ransa ya quntata,karo na farko da ya soma jin kishin nukhtar har cikin ransa,mukhtar jininsa ne wanda har ya mutu babu wani abu mara dadi da ya taba hadasu,hakan ya sanya bai sake tofa komai ba har suka iso gidan yaya yahanasun,tayi zaton zai shigo ne da ya ajjiyesu,sai taga ya juya kan motar yayi gaba.
A tsakar gida suka samu abdallan,yana ta wasa da dan qaramin keke da yaya yahansun ta siya masa,jamila na faman binsa tana sauya masa kayansa da yayi kaca kaca da su da miya amma yaqi yarda,ya maidata abar wasansa sai zagaye suke yana dariya,yana ganinta yayi cilli da keken ya taho a guje ya dafeta yana dariya,itama dariyar take,sai taji sanyi a cikin zuciyarta,yaya yahanasu da taji muryarsu ta fito cikin fara'a tana musu sannu da zuwa.
Ina ka saka ina ka ajjiye take tayi da su,kamar zata goya sumayyan,abdallah ya wani ajiye kumatu,abinda yakeso kawai yake cikin gidan,sai bayan sallar magariba sannan suka shirya tafiya,qeme me abdallah yace ba zai bisu ba,saidai sumayyan itama ta dauko kayanta ta zauna anan,dariya suka dinga yi,ganin haka ya sanya sumayyan tace a barshi,duk sanda ya gaji ya dawo.
Ga mamakinta suna fitowa ta tadda abdur rahman tsaye qofar gidan,qofa bude yana kallonta,ta fuskanci me yake nufi saboda haka babu musu ta shiga,zainab ma ta bude gidan baya ta shiga,sau daya rufe sannan taga ya shiga gidan,baifi mintina biyar ba ya fito suka tafi,har suka je gida baice uffan ba,ya saukesu ta masa godiya ta wuce,tana shirin kwanciya saqonshi ya shigo wayarta,saqo ne dake dauje da kalamai masu nuna tsantsar qauna,da nuna ba za'a rabu da abinda ake so ba,tana gama karantawa ta goge ta kwanta,tana ayyana ta kusa nesa da dukkan wadan nan rudanin.
****** ********* *****
*BAYAN KWANA BIYAR*
Anty dije suka iso kano ita da yaran da mai gidan baki daya,gidansu na da anan suke masauki duk sanda suka zo din,bata samu zuwa gidansu sumayyan ba sai bayan kwana biyu da zuwan nata.
Sha daya da rabi na rana suka iso baki dayansu,sun sauya baki daya daga anty dijen duka sunyi kyau da wata irin gogewa,kana ganinsu kasan kwanciyar hankali da hutu sun samu wajen zama,duk suna falon mama,maman da anty dije suna hirarsu ta zumunci,yaran duka sun kewaye sumayya suna ta bata labari,mutuniyar tata minar na zaune dare dare kan cinyarta,laila ce ta soma tambayar Abdallah wanda hakan ya janyo hankalin anty dije
"Nima fa ban ganshi ba" injita,murmushi mama tayi
"Mu zai nunawa 'yan ubanci ai,tunda yahanasu ta daukeshi kinga yaqi dawowa,uwar ma taje da kanta yaqi biyota" haba anty dijen ta riqe tana dariya
"Yanzun haka zamu tafi ki barshi a kano?" Tayi maganar ta sigar tambaya tana duban sumayya,dariya sumayya tayi
"Wai da gaske anty sai na bikin?,to idan naje ma kwana nawa ne zan dawo ai ba dadewa zanyi ba" dubanta anty dijen tayi cikin mamaki
"Wai meke damunki da baki son abuja ne kamar ana gutsurarki" tabe fuska tayi kamar qaramar yarinya
"Garin ne ni banjin dadinsa anty haka kurum" kanta ta dauke daga kan sumayyan tana cewa
"Sai kiyi kuma,mu me ya cimu?,"
"Yaya asama'u(sunan mama na asali)Allah yasa dai malam na gari,don tun yau nakeson sanar masa da sumayyan zan tafi,na lura kamar ku din a nan bata samun kwamciyar hankali da nutsuwar data dace,dama can baya kun yimim alqawarin bani ita kuma aure ya fado mata da wuri,kinga yanzu sai a cikamun alqawari na"dariya mama tayi tana cewa
"Malam yana nan ya fita ne taron bude wani sabon masallacin juma'a da aka gina,amma nan da biyar ko shida na yammaci zai dawo"
"To Allah ya dawo dashi lpy,ina nan har ya dawo"
"Amin" inji mama.
"Momy,wai anty da ita zamu tafi?" Khalipha ya fada cikin murna da doki yana dora hannunsa hannunshi kan cinyar anty dije
"In sha Allahu" ta bashi amsa,
"Yeeeeeyyyyyy" yaran suka sanya ihu baki daya har suka sanya sumayyan ta tuntsire da dariya duk da yadda jikinta yayi sanyi da zancan tafiyar tata.
Anty dije ko bata tafu din ba har sai da malam ya dawo,sanda ta tuna masa tsohon alqawarin da suka mata dariya ya saka sosai,don shi sam ya manta da maganar ma baki daya,shi kansa cikin yaransa yana son sumayya,tana da baiwa da wasu halaye na daban da ba kowa ke da su ba,amma babu yadda ya iya,tilas ya cika alqawarin da ya dauka duk da cewa tsoho ne,yace ya basu sumayya halak malak indai suna so,da yake gaban alhj farouq akayi shima yaji dadi sosai,har da shi a godiya,don shima yasan halayen sumayyan,ya tabbata ko zama tayi cikin yaransa zasu qaru da ita,hakanan zata taimaka ma matarsa zasu dinga ganin nasu na gida a kusa da su saji dadi.