Sashe 2
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan ya kammala ya tako gaban madubin yana gyara zaman hularsa a kanshi,sumayya ta dubeshi cikin zuciyarta tana yaba kyawun da yayi,ya kula da ita saboda haka cikin salon tsokana yace
"Ki fito kawai kice na fiki kyau yarinya,sai wani satar kallona kike" sau tari idan ya fadi haka kunya da dariya yake bata,har ma wani lokacin musu ya dan kaure tsakaninsu,yau din ma dariyar tayi,maimakon ta biye masa auyi musun su na ta fishi kyau da iya kwalliya yadda suka saba sai tace
"Yaa mukhtar,yau ne fa sunan fiddausin" yanayin fuskarsa taga ya dan sauya,bai ce komai ba yana daura agogon hannunsa,har ta fidda rai tayi zaton ba zaya ce komai din ba sai taji yace
"Zaki je dinne?" Murmushi tayi saboda mamaki tambayar ta bata,fiddausi ai kamar diyarsa ce saboda 'yar yaya yahanasu ce,kuma shi da kansa ya bada kudin ankon sunan harda kudin dinkin ma
"Me zai hana yaa mukhtar,saidai idan kai ka hana" shiru ya sake yi har ya kammala ya dauki jakarsa ya rataya sannan ya sanya hannu cikin aljihun rigarsa ya fiddo da dari biyar ya miqa mata kudin cefane,sannan ya sake fitar da dubu daya daban yace mata kudin mota,ya sake bata wata dubu biyun yace ta baiwa mai jego barka,hannu biyu ta saka ta amsa tana jera godiya kamar yadda ya zame mata al'ada duk qanqantar alkhairin da zaya yi mata,tako masa tayi ta rakoshi har ya fidda babur dinsa waje tayi masa a dawo lafiya.
Tana shirin mayar da qofar gidan ta rufe taga ya juyo
"Idan kika je kada ki dade,ki dawo gida da wuri,kuma bana son ki shiga cikinsu kuyita faman surutu" dan jim tayi saboda bai taba cewa hakan ba idan zata shiga cikinsu sai yau,amma sai ta share ta gyada kai kawai tace
"Insha Allahu".
Qarfe sha biyu da arba'in ta kammala shirinta tsaf,tayi kyau cikin ankon sunan duk da cewa qaramar atamfa ce 'yar leda wadda kudinta bai wuce dubu da dari biyar ba,mayafinta takalmi da jakarta har sarqarta duka sun dace da atamfar,yau cikin yaranta ba wanda ya leqo,hakan baya rasa nasaba da ce musu da tayi zata unguwa ne gobe,yaran kusan tarbiyyarta ce,suna da hankali da nutsuwa,tsahon shekara shida suna tare suke debe mata kewa,sanda aka kawota unguwar ita din ma tana qwailarta,yaran basu wuce shekara biyu ba harda masu daya da rabi,ita ta dinga rainonsu,don karbo su take su wuni gurinta,iyayensu sun riqeta tamkar 'yarsu,don haka sabo da shaquwa ne tsakaninsu sosai.
Gidan maman sadiya ta shiga saboda tahowa da nana yarinyar maman sadiya wadda zata rakata,duk cikin yaran yarinyar tafi shiga ranta,a kitchen ta samu maman sadiyan na dora girkin rana,nana anci kwalliya ana tsaye bakin qofar daki,hatta da takalminta na qafarta,cikin barkwanci suka gaisa da maman sadiya kana tac" ga mutuniyar nan,tun dazun ta addaba sai taje taga kin shirya,ni na hanata"dariya sumayya tayi
"Ai na gama sai tafiya" fatan dawowa lafiya maman sadiyan tayi musu kana suka fice.
Qarfe daya da wasu mintina ta isa gidan,tuni har ya fara cika da jama'a kasancewar haihuwar fari fiddausin tayi,gaisawa ta dinga yi da duk wanda taci karo har ta dangana da dakin mai jegon,'yan uwan mukhatar ne cike da falo zuwa uwar dakan fiddausin,bata gajiya ba sai data bi ta gaida kowa,yayin da kowa ke amsa mata cikin mabanbantan yanayi,wani ya amsa mata ba yabo ba fallasa,wani ya amsa mata cikin shakulaton bangaro,yayin da wani bai amsawa ma sai an tabo shi ance ana gaidaka,duk hakan bai dameta ba saboda shekaru biyu kenan da fara fuskantar irin hakan daga garesu,mutum ce ita mai qaranta zargi qwarai a kan mutum,babu wani abu da suka taba ce mata face sauyin fuska kawai da take gani daga garesu.
Cikin uwar dakan ta cimma fiddausi tare da yaya bara'atu wadda ita ke bin muktar sai mai bi mata fadima sai kubra 'yar yayan mukhtar,sai babbar 'yar yaaya yahanasu mansura,jaririyar ta dauka fuskarta qunshe da murmushi tana fadin
"Kai masha Allah,jariri akwai abun sha'awa"
"Hmmm,ku kam ba ruwanku da ita ko?"cewar fadima kafin tace wani abu yaaya bara'atu ta karbe zancen
"Nan da wata goma idan Allah yaso gidan mutari zamu suna,wannan karon kam shima Allah ya kusa kawo masa"
"Allah yasa"inji fadiman.
Hakanan ta samu kanta da fargaba hadi da faduwar gaba,bata fita daga wannan yanayin ba maganar fiddausi ta katse mata zaren tunanin da ta fara qullawa
" au,ciki ne da sumayyan?"tabe baki yaya bara'atu tayi tana fadin
"Hmm,ina fa,yaaya yahanasu ke nema masa auren fa'iza" wata matsananciyar faduwar gaba ta saukar mata,jikinta yayi sanyi qalau,ta dinga jin zuciyarta na bugawa da sauri
"Alla ya sanya alkhairi" fiddausi ta fada tana kwashe rigunan barka na jaririyar daga kan gadonta tana lodawa cikin sif,hakanan take,baka fiya gane alqiblarta kan lamura ba.
A hankali ta zame yarinyar daga cinyarta cikin kasala sakamakon shigowar 'yan suna cikin dakin,ta budr jakarta ta fito da dubu biyun da mukhtar ya bata ta miqawa fiddausin tana cewa
"Gashi,a siyawa baby turare" karba tayi tana fadin
"An gode".
Duk yadda zancan ya daketa haka ta dinga dakewa tana yaqe,sam hankalinta ba'a kwance yake ba,qarfe hudu da rabi ta musu sallama don komawa gidan,ba wanda ya damu da tafiyar tata ballantana ya tambaya,sai data miqa nana gida sannan ta bude gidanta ta shigr.
Kan kujerar falonta ta zube tana kiran sunan Allab,tayi a qalla awa guda tana saqa tana warwarewa,tabbas sauyin fuska da ta samu daga garesu yana da nasaba da rashin haihuwarta?,aure kenan mukhtar zai qara?,eh mana,dole mukhtar ya qara aure,'yana da buqatar ganin jininsa kamar yadda danginsa ke da irin wannan buqatar',abinda zuciyarta ta tunasar da ita kenan,ambaton sunan Allah tayi ta runtse idanunta,babu shakka don so tana son mukhtar,amma bata jin zata yarda ta zama silar batawarsa da yayarsa wadda take tamkar mahaifiya a wajensu,tasan halin yaaya yahanasu sarai,duk abinda ta quduri aniya sai ta aiwatar da shi,hana na nufin bashi da amfani tace zatayi adawa da abinda ta umarceshi.
Cikin mutuwar jiki ta miqe don yin sallar la'asar tana istigfari,saboda lokacin ta da ya kusa qwace mata ba tare da ta yita ba,ko da ta idar ta jima zaune saman abun sallar tana addu'o'i sannan ta samu ta miqe,kitchen ta shiga,ta riga da tasan yau ta makara don haka bata da buqatar dora girki mai wuya saboda bata son mukhtar din ya dawo ya buqaci abinci bata kammala ba.
Tana girkin tana saqe saqe,tana ta faman hada daya da daya,sai yanzu ta tabbatar cewa damuwar jiya da mukhtar ya shigo da ita bata rasa nasaba da wannan zancan kenan?,da gaske ne kenan auren mukhtar zai qara?,sai tasa tafin hannunta ta share qwallar da take zubo mata tana addu'ar neman agajin ubangiji,babu shakka qauna ce ta sanya mukhtar ya kasa gaya mata komai.
Jallope din shinkafa tayi da kayan lambu saboda haka ana kiraye kirayen sallar magariba ta kammala,tuni dama tana da lemonta cikin dan qaramim fridge dinta wanda zobo ne da lemon tsamiya saboda mukhtar na sonsu musamman lemon tsamiya saboda maiqo.
A gurguje tayi wanka ta hada da alwala,bayan ta kammala sallah ta shirya tsaf cikin qananun kaya wanda take siya cikin gumama da ake budewa bayan layinsu,sosai kayan suka yi mata kyau,sai ka rantse babu wani abu dake damun zuciyarta.
Tana cikin yin turaren wuta taji bugun qofa,ta ajjiue kaskon ta zira hijabinta kana taje ta bude,Amrah ce 'yar maqotansu daya daga cikin yaran gidanta kenan riqe da kwanon samira a hannunta
"Anty yau duk bamu ganki ba,baki dawo daga unguwar da wuri bane?" Yarinyar ta tambaya tana murmushi,murmushin itama sumayya tayi
"Da wuri na dawo amrah,banajin dadi ne sosai yau"
"Allah sarki anty sannu" yarinyar ta fada cikin nuna alhini,sumayyan ta amsa mata tana karbar kwanon da amrahn ke miqo mata
"Gashi,dama mama ce tace na kawo miki dambu ne" murmushi ta sake yi tana cewa
"Ayyah ki cewa mama na gode,ashe bata manta da ni ba,jirani ina zuwa" ta fada tana shiga da kwanon ciki,alewa ta ciro guda biyu cikin jakar alawar 'yar dari da hamsin da take badawa ana siyo mata saboda yaran
"Ungo ki gaida mama da kyau" hannu biyu tasa ta amsa tana cewa an gode ta juya ta tafi.
Tana shirin maida qofar ta rufe horn din mashin din mukhtar ya dakatar da ita,sai ta zare sakatar gami da bude masa qofar ta raabe daga can bakin qofar tana jiran shigowarsa.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍🏽 *~KUNDIN QADDARATA~*✍🏽
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
_bismilla hir rahmanir rahim_
*_qul ya ibadiyal lazina asrafu ala anfusihim la taqnad'u minr rahmatillah_*
_____________________
0⃣2⃣
Shi din ma a yau kallo daya yayi mata ya tabbar akwai abinda ya mata kutse cikin farinciki da walwalarta,sosai fuska da jikinta baki daya suka nuna gazawa da kasawarta,gabansa ya fadi saboda wani tunani da ya darsu cikin zuciyarsa,a hankali qirjinsa ya dinga bugawa.
Yarinya ce amma a dabi'unta sam ba zaka kirata haka ba,tana da halin manya da dattako da sanin ya kamata,sai tayi qoqarin cilla duk wata damuwarta gefe guda ta garbeshi yadda suka saba,a yau din ya sake sosai har ma yana tsokanarta,amma ta nan fannin sai ta samu kanta da gaza amsa masa,duk da murmushin yaqen da take ta qoqarin binsa da shi,wani abu ne cunkushe a qirjinta.
Tana ta kai kawon shirya masa abinci yana ta binta da kallo,babu shakka iya kula da miji ba wai mace mai karatun boko kawai ta iya ba,shi ya yadda da wannan,komai na sumayya a nutse yake,ba zaka taba tunanin bata taba shiga aji ba face ajinsa,shi ya koya mata yadda zata yi karatu da rubutu,rainonsa ce shi ya raini abarsa,ko motsi sumayya tayi yasan me yake nufi,hakan ya sanya a yanzu kallon da yake binta da shi karantarta yake,duk wani motsi nata na gaya masa akwai damuwa mai yawa cikin zuciyarta.
"Ki fito kawai kice na fiki kyau yarinya,sai wani satar kallona kike" sau tari idan ya fadi haka kunya da dariya yake bata,har ma wani lokacin musu ya dan kaure tsakaninsu,yau din ma dariyar tayi,maimakon ta biye masa auyi musun su na ta fishi kyau da iya kwalliya yadda suka saba sai tace
"Yaa mukhtar,yau ne fa sunan fiddausin" yanayin fuskarsa taga ya dan sauya,bai ce komai ba yana daura agogon hannunsa,har ta fidda rai tayi zaton ba zaya ce komai din ba sai taji yace
"Zaki je dinne?" Murmushi tayi saboda mamaki tambayar ta bata,fiddausi ai kamar diyarsa ce saboda 'yar yaya yahanasu ce,kuma shi da kansa ya bada kudin ankon sunan harda kudin dinkin ma
"Me zai hana yaa mukhtar,saidai idan kai ka hana" shiru ya sake yi har ya kammala ya dauki jakarsa ya rataya sannan ya sanya hannu cikin aljihun rigarsa ya fiddo da dari biyar ya miqa mata kudin cefane,sannan ya sake fitar da dubu daya daban yace mata kudin mota,ya sake bata wata dubu biyun yace ta baiwa mai jego barka,hannu biyu ta saka ta amsa tana jera godiya kamar yadda ya zame mata al'ada duk qanqantar alkhairin da zaya yi mata,tako masa tayi ta rakoshi har ya fidda babur dinsa waje tayi masa a dawo lafiya.
Tana shirin mayar da qofar gidan ta rufe taga ya juyo
"Idan kika je kada ki dade,ki dawo gida da wuri,kuma bana son ki shiga cikinsu kuyita faman surutu" dan jim tayi saboda bai taba cewa hakan ba idan zata shiga cikinsu sai yau,amma sai ta share ta gyada kai kawai tace
"Insha Allahu".
Qarfe sha biyu da arba'in ta kammala shirinta tsaf,tayi kyau cikin ankon sunan duk da cewa qaramar atamfa ce 'yar leda wadda kudinta bai wuce dubu da dari biyar ba,mayafinta takalmi da jakarta har sarqarta duka sun dace da atamfar,yau cikin yaranta ba wanda ya leqo,hakan baya rasa nasaba da ce musu da tayi zata unguwa ne gobe,yaran kusan tarbiyyarta ce,suna da hankali da nutsuwa,tsahon shekara shida suna tare suke debe mata kewa,sanda aka kawota unguwar ita din ma tana qwailarta,yaran basu wuce shekara biyu ba harda masu daya da rabi,ita ta dinga rainonsu,don karbo su take su wuni gurinta,iyayensu sun riqeta tamkar 'yarsu,don haka sabo da shaquwa ne tsakaninsu sosai.
Gidan maman sadiya ta shiga saboda tahowa da nana yarinyar maman sadiya wadda zata rakata,duk cikin yaran yarinyar tafi shiga ranta,a kitchen ta samu maman sadiyan na dora girkin rana,nana anci kwalliya ana tsaye bakin qofar daki,hatta da takalminta na qafarta,cikin barkwanci suka gaisa da maman sadiya kana tac" ga mutuniyar nan,tun dazun ta addaba sai taje taga kin shirya,ni na hanata"dariya sumayya tayi
"Ai na gama sai tafiya" fatan dawowa lafiya maman sadiyan tayi musu kana suka fice.
Qarfe daya da wasu mintina ta isa gidan,tuni har ya fara cika da jama'a kasancewar haihuwar fari fiddausin tayi,gaisawa ta dinga yi da duk wanda taci karo har ta dangana da dakin mai jegon,'yan uwan mukhatar ne cike da falo zuwa uwar dakan fiddausin,bata gajiya ba sai data bi ta gaida kowa,yayin da kowa ke amsa mata cikin mabanbantan yanayi,wani ya amsa mata ba yabo ba fallasa,wani ya amsa mata cikin shakulaton bangaro,yayin da wani bai amsawa ma sai an tabo shi ance ana gaidaka,duk hakan bai dameta ba saboda shekaru biyu kenan da fara fuskantar irin hakan daga garesu,mutum ce ita mai qaranta zargi qwarai a kan mutum,babu wani abu da suka taba ce mata face sauyin fuska kawai da take gani daga garesu.
Cikin uwar dakan ta cimma fiddausi tare da yaya bara'atu wadda ita ke bin muktar sai mai bi mata fadima sai kubra 'yar yayan mukhtar,sai babbar 'yar yaaya yahanasu mansura,jaririyar ta dauka fuskarta qunshe da murmushi tana fadin
"Kai masha Allah,jariri akwai abun sha'awa"
"Hmmm,ku kam ba ruwanku da ita ko?"cewar fadima kafin tace wani abu yaaya bara'atu ta karbe zancen
"Nan da wata goma idan Allah yaso gidan mutari zamu suna,wannan karon kam shima Allah ya kusa kawo masa"
"Allah yasa"inji fadiman.
Hakanan ta samu kanta da fargaba hadi da faduwar gaba,bata fita daga wannan yanayin ba maganar fiddausi ta katse mata zaren tunanin da ta fara qullawa
" au,ciki ne da sumayyan?"tabe baki yaya bara'atu tayi tana fadin
"Hmm,ina fa,yaaya yahanasu ke nema masa auren fa'iza" wata matsananciyar faduwar gaba ta saukar mata,jikinta yayi sanyi qalau,ta dinga jin zuciyarta na bugawa da sauri
"Alla ya sanya alkhairi" fiddausi ta fada tana kwashe rigunan barka na jaririyar daga kan gadonta tana lodawa cikin sif,hakanan take,baka fiya gane alqiblarta kan lamura ba.
A hankali ta zame yarinyar daga cinyarta cikin kasala sakamakon shigowar 'yan suna cikin dakin,ta budr jakarta ta fito da dubu biyun da mukhtar ya bata ta miqawa fiddausin tana cewa
"Gashi,a siyawa baby turare" karba tayi tana fadin
"An gode".
Duk yadda zancan ya daketa haka ta dinga dakewa tana yaqe,sam hankalinta ba'a kwance yake ba,qarfe hudu da rabi ta musu sallama don komawa gidan,ba wanda ya damu da tafiyar tata ballantana ya tambaya,sai data miqa nana gida sannan ta bude gidanta ta shigr.
Kan kujerar falonta ta zube tana kiran sunan Allab,tayi a qalla awa guda tana saqa tana warwarewa,tabbas sauyin fuska da ta samu daga garesu yana da nasaba da rashin haihuwarta?,aure kenan mukhtar zai qara?,eh mana,dole mukhtar ya qara aure,'yana da buqatar ganin jininsa kamar yadda danginsa ke da irin wannan buqatar',abinda zuciyarta ta tunasar da ita kenan,ambaton sunan Allah tayi ta runtse idanunta,babu shakka don so tana son mukhtar,amma bata jin zata yarda ta zama silar batawarsa da yayarsa wadda take tamkar mahaifiya a wajensu,tasan halin yaaya yahanasu sarai,duk abinda ta quduri aniya sai ta aiwatar da shi,hana na nufin bashi da amfani tace zatayi adawa da abinda ta umarceshi.
Cikin mutuwar jiki ta miqe don yin sallar la'asar tana istigfari,saboda lokacin ta da ya kusa qwace mata ba tare da ta yita ba,ko da ta idar ta jima zaune saman abun sallar tana addu'o'i sannan ta samu ta miqe,kitchen ta shiga,ta riga da tasan yau ta makara don haka bata da buqatar dora girki mai wuya saboda bata son mukhtar din ya dawo ya buqaci abinci bata kammala ba.
Tana girkin tana saqe saqe,tana ta faman hada daya da daya,sai yanzu ta tabbatar cewa damuwar jiya da mukhtar ya shigo da ita bata rasa nasaba da wannan zancan kenan?,da gaske ne kenan auren mukhtar zai qara?,sai tasa tafin hannunta ta share qwallar da take zubo mata tana addu'ar neman agajin ubangiji,babu shakka qauna ce ta sanya mukhtar ya kasa gaya mata komai.
Jallope din shinkafa tayi da kayan lambu saboda haka ana kiraye kirayen sallar magariba ta kammala,tuni dama tana da lemonta cikin dan qaramim fridge dinta wanda zobo ne da lemon tsamiya saboda mukhtar na sonsu musamman lemon tsamiya saboda maiqo.
A gurguje tayi wanka ta hada da alwala,bayan ta kammala sallah ta shirya tsaf cikin qananun kaya wanda take siya cikin gumama da ake budewa bayan layinsu,sosai kayan suka yi mata kyau,sai ka rantse babu wani abu dake damun zuciyarta.
Tana cikin yin turaren wuta taji bugun qofa,ta ajjiue kaskon ta zira hijabinta kana taje ta bude,Amrah ce 'yar maqotansu daya daga cikin yaran gidanta kenan riqe da kwanon samira a hannunta
"Anty yau duk bamu ganki ba,baki dawo daga unguwar da wuri bane?" Yarinyar ta tambaya tana murmushi,murmushin itama sumayya tayi
"Da wuri na dawo amrah,banajin dadi ne sosai yau"
"Allah sarki anty sannu" yarinyar ta fada cikin nuna alhini,sumayyan ta amsa mata tana karbar kwanon da amrahn ke miqo mata
"Gashi,dama mama ce tace na kawo miki dambu ne" murmushi ta sake yi tana cewa
"Ayyah ki cewa mama na gode,ashe bata manta da ni ba,jirani ina zuwa" ta fada tana shiga da kwanon ciki,alewa ta ciro guda biyu cikin jakar alawar 'yar dari da hamsin da take badawa ana siyo mata saboda yaran
"Ungo ki gaida mama da kyau" hannu biyu tasa ta amsa tana cewa an gode ta juya ta tafi.
Tana shirin maida qofar ta rufe horn din mashin din mukhtar ya dakatar da ita,sai ta zare sakatar gami da bude masa qofar ta raabe daga can bakin qofar tana jiran shigowarsa.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍🏽 *~KUNDIN QADDARATA~*✍🏽
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
_bismilla hir rahmanir rahim_
*_qul ya ibadiyal lazina asrafu ala anfusihim la taqnad'u minr rahmatillah_*
_____________________
0⃣2⃣
Shi din ma a yau kallo daya yayi mata ya tabbar akwai abinda ya mata kutse cikin farinciki da walwalarta,sosai fuska da jikinta baki daya suka nuna gazawa da kasawarta,gabansa ya fadi saboda wani tunani da ya darsu cikin zuciyarsa,a hankali qirjinsa ya dinga bugawa.
Yarinya ce amma a dabi'unta sam ba zaka kirata haka ba,tana da halin manya da dattako da sanin ya kamata,sai tayi qoqarin cilla duk wata damuwarta gefe guda ta garbeshi yadda suka saba,a yau din ya sake sosai har ma yana tsokanarta,amma ta nan fannin sai ta samu kanta da gaza amsa masa,duk da murmushin yaqen da take ta qoqarin binsa da shi,wani abu ne cunkushe a qirjinta.
Tana ta kai kawon shirya masa abinci yana ta binta da kallo,babu shakka iya kula da miji ba wai mace mai karatun boko kawai ta iya ba,shi ya yadda da wannan,komai na sumayya a nutse yake,ba zaka taba tunanin bata taba shiga aji ba face ajinsa,shi ya koya mata yadda zata yi karatu da rubutu,rainonsa ce shi ya raini abarsa,ko motsi sumayya tayi yasan me yake nufi,hakan ya sanya a yanzu kallon da yake binta da shi karantarta yake,duk wani motsi nata na gaya masa akwai damuwa mai yawa cikin zuciyarta.