Sashe 63
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya sake bude mata shafi ne daga lokacin da karima ta cika wata biyu da rabi da barin gidan,sauyin data fara gani daga lukman din,kusan tun bayan tafiyar karima sumayya ta dorashi kan ibada saboda gunewa faruwar wani abu,cikin sati gaba daya ta fuskanci ya zama mai son jiki da wata muguwar kasala,da qyar yake iya sallolinsa na farilla balle akai ga na nafila,idan qur'ani suka dauko zasuyi tilawa yadda suka saba sai ya soma gyangyadi daga nan sai bacci,idan sallar asuba ce kullum sai ya makara sai tayi da gaske,duk wani abu na ibada ya zama very lazy akansa,tun abun na bata mamaki har ya soma bata tsoro,hakan ya sanya ta samu hajiya da maganan,sam bata kowa komai ba tace sumayyan taci gaba da haquri da kuma qoqarin ci gaba da dorashi a hanya har ya daina,kuma itama zata yi masa fada
A hankali sai abun ya soma cin tura,hatta idan yana bacci bai da aiki sai kiran sunan karima,idan ya tashi kuwa washegari haka zai yini babu wannan walwalar sam.haka kawai yake jin rayuwarsa da zuciyarsa cikin takura da qunci,ji yake kamar yana cikin wata kurkuru,burinsa kawai yaga karima cikin gidan,saidai duk da haka bai taba furtawa sumayya ba.
*_Bayan sati d'aya_*
Bayan sallar isha'i ne dukkansu suna zaune a falom gidan banda hajiya dake bangarenta saboda yau da wuri ta kwanta,sumayya da nuratu da nuwaira na zaune tana koya musu aikin gida(assigment)da aka basu a makaranta,basma na saman kujera tana bacci tun sanda suka gama cin abincin dare,sai islam dake kwashe kwanukan da suka ci abinci da su tana shigarwa kitchen.
Lukman ne ya fito falon a gaggauce wanda tunda ya dawo daga kasuwa yana cikin daki bai fito ba sai yanzu,hannunsa riqe da dan mukulli,daya hannun nasa kuma riqe da hularsa,kana ganinsa kamar wanda aka jefo ko aka tunkudo,daga kai sumayya tayi tana dubansa sanda ya giftasu zai fice ganin bai cewa kowa komai ba
"Abban nuwaira" waiwayowa yayi yana dubanta tare da amsawa
"Ina zaka fita haka tara na dare?" Ta fada a marairaice
"Sorry airphort zani,yanzu zamu dawo" ya fadi yana ficewa da sauri jin wayarsa na ringing,kanta ta maida suka ci gaba da assigment din da yaran,hakanan taji gabanta na yawaita faduwa,hasbunallahu wa ni'imal wakil ta dinga maimaitawa,suna gamawa ta tattara yaran duka suka tafi dakinsu,sai da kowa ya sanya kayam baccinsa ya karanta addu'ar kwanciya bacci suka kwanta sannan ta rufo musu dakin ta koma nata dakin,alwala tayu tayi shafa'i da wutirinta sannan ta zauna ta karanta suratul mulk,har ta gama abinda take bata ji shigowarsa ba,saboda haka ta sanya hijabinta ta nufi bangaren hajiya.
A kashingide ta sameta riqe da carbi,ganin sumayyan ya sanyata zama tana murmushi
"Yanzu kuwa nake zancanki a zuciyata" itama murmushin take tana cewa
"Hajiya baki bacci ba?"
"Kin ganni nan wlh banyi ba,gabana ne yake ta faduwa sai na tuna dazu banyi waraddallahu ba,sai nake yinta yanzu (waraddallahul lazina kafaru bi gaizihim lam yanaluu khairaa,wa khafallahul mu'umininal qital,wa kanallahu qawiyyan aziza,ana karanta ta ne qafa dari bayan sallar asaba kariya daga dukkan kaidin wani maqiyi dake nufarka da shi in sha Allah)"
"Ai gwara hajiya" ta fada tana tunanin faduwar gaban da itama take ji tayi dai dai data hajiya kenan
"Ina lukman din kuma?"
"Ya dan fita ne hajiya yara kuma sun kwanta saboda makaranta goben"
"Sannunki kedai sumayya,Allah yayi albarka" "amin hajiya"ta fada tana murmushi kanta a qasa,shiru ne ya biyo baya kafin su soma taba hira kadan kadan,ganin har sha daya na dare tayi ya sanyata yiwa hajiyan sallama ta koma sashenta.
Tana zaune har sha daya da rabi sannan taji muryar lukman,a hankali ta tashi ta leqa,shine a gaba janye da akwati daya hannun jaka,sai KARIMA dake biye da shi a baya,da sauri ta saki labulen ta koma da baya tana kiran sunayen Allah,sannu a hankali nutsuwa ta saukar mata,sai ta daura alwala ta kwanta,don jikinta na bata lukman ba zaya nemeta a yau ba.
Ilai kuwa bata sake jin motsinsa ko na karima ba har bacci yayi awon gaba da ita.
****** ******* *****
Washegari yadda suka saba haka tayi bata fasa ba,ita ta tashi yaran baki daya sukayi sallar asuba,sannan ta dafa ruwa mai zafi islam ta fara yi sannan nuwaira ta dinga yiwa qananan tana tura su islam na shiryasu ita kuma tayi daga qarshe,sumayya kuma na kitchen tana hada breakfast da wanda zasu tafi da shi makaranta,abinda dukka a da basu saba yi ba amma a yanzu ya zame musu jiki.
Sun shirya tsaf suna karyawa ya zagaya ta buga dakin karima don taga idan sun tashi ta tura yaran su gaida mamansu kan su wuce,saidai har ta gama bugunta ko tari bata ji anyi ba,abinda bata sani ba lukman na jin bugun,ya kuma san sumayyarsa ce,kamar ya zura a guje ya bude saidai ina sam bai isa ba,saboda bai samu umarni ba,tunda ta dawo a jiyan qasan zuciyarsa ke a cunkushe cike da baqinciki bacin rai da tsananin tsoronta,amma a fili tsantsar farinciki ne da tsananin biyayya bayyane a fuskar tasa,abinda zai baka mamaki tunda ta dawo bai taba kwatanta tambayarta inda ta tafi da aurensa a kanta ba kuma ba tare da izininsa ba har na tsawon wata biyu ba,a lokacin ma yana bandaki yana wanke mata tana son shiga wanka saidai ya hada qura a tsawon wata biyu da bata nan tunda ba wani ke shiga ba gun nata na a rufe ne.
Dawowa tayi inda suke kowa ya kammala mai adaidaitan dake kaisu ma ya iso ta dubesu
" mamanku fa ta dawo jiya da daddare"ta tsammaci zata ga tsantsar farinciki a fuskokinsu,sai taga babu yabo ba fallasa,babu wani zumudi ko doki,nuwaira kuwa tsoro da fargaba ne ma ya mamayeta,a haka ta rakasu suka fice sannan ta dawo ta gyara falo zuwa kitchen ta barwa mai aikinsu wanke wanke idan ta iso tayi wanka ta leqa bangaren hajiya,sai ta sameta tana bacci,saboda haka ta mata 'yan gyare gyarenta ta fito ta barta ta dawo falo ta zauna tana jira sha daya da rabi tayi ta karya,sai ta kunna t.v tana kallon arewa 24 don ta debe mata kewa,zuwa yanzu sum shaqu sosai da yaran,idan basa tare duk sai taji babu dadi kasancewarta mai son yara.
Tana jiyo qarar bude qofar karima amma bata maida hankalinta kai ba har sai da taji cikin taqama tana fadin
"Ina yara na" cikin ladabi kamar bawa da uban gidansa taji lukman na cewa
"Eh sun tafi makaranta ai sumayya ta turasu" cikin harzuqa tace
"Eh wato suma an shige musu za'a shanyesu a rabani da su kenan?" Sai ta saki wani shu'umin murmushi tana kada kai
"Mu zuba mu gani,muje ka rakani naga hajiya nata salon ita kuma" ta fada tana yin gaba,jiki na rawa yana tafe yana waiwayen sumayya yabi bayanta,kai ta jinjina bayan fitarsu
"Innalillahi wa 'inna ilaihi raji'un" ta fada tana kada kai ganin hannun agogo nason komawa baya game da lamarin lukman din.
Zuwanta gun hajiyan ta taddata fiye da yadda ma ta barta,don fada hajiyan ma ta mata kan dalilin tafiyarta wani gu bayan tana da aure,sosai hajiyan keji qarfin zuciyarta sam babu wani dar da taji balle taji tsoron karimar,sai lokacin ta yadda lallai idan kayi sakaci da addu'a babu abinda ba zaya iya faruwa da bawa ba duk da cewa akwai QADDARA amma babu abinda ke sauya qaddarar irin ADDU'A.
Ko da rana da yaran suka dawo sun gaidata,baki ta saki tana kallon yadda suka sauya baki daya,tana kallon yadda suke girmama nuwaira da islam,lallai sumayya ta sauya mata yara,ya akayi bata sanya an musu farraqu ba ita da au ta barsu suka shaqu haka,tana gani suka sauya kayansu zuwa na islamiya bayan sunci abinci,suna sanya hijabansu sumayya na tsakiyarsu tana hada musu litattafan islamiyar su kariman ta banko qofar dakin tana huci,tsayawa tayi tana dubansu fuska a tsuke,sumayya data kalleta saita maida kai taci gaba da abinda take
"Laaa,mama bakiyi sallama ba fa,kuma babu kyau shiga gu ba sallama" nuratu ta fada,mamaki ya kama kariman sai ta waiwaya tana kallonta amma sai ta wayance da cewa
"Ku cire kayan nan,babu wata makaranta da zaku sake zuwa daga dawowarku daga boko ko hutawa bakuyi ba" islam ce ta maqe wuya tana cewa
"Mama ki barmu muje,idan mun dawo ma huta din,idan kana fashi fa ana wuceka a karatun" ido ta kuma zarowa mamki na sake kasheta,lallai sumayya tayi amfani da irin surkullensu ta rabata da yaranta,tsawa ta daka musu tana cewa
"Don ubanki da ni kike jayayya,ku cire kayanku nace babu inda zaku" sumayya ce ta bar abinda take ta tako zuwa inda take tana cewa
"Haba maman nuratu,meye na zagi har haka?,ina cewa ke zaki fi kowa farincikin zuwan yaranki makaranta,ba girmanki bane" sai ta waiwaya ga yaran da sukayi carko carko suna kallon karimar
"Maza ku wuce ku tafi mamarku ta haqura" da sauri suka fice kuwa daya bayan daya,sai da suka kammala ficewa tas sannan karima ta kalli sumayya
"Yaro man kaza,ke da su baki daya baku da bambanci a gurina,lokaci na baki shi nake jira" tana gama fada ta fita
"Allah ya fiki,Allah ya isar min da ke akan dukkan wani nufinki,alkhairin ubangiji nake nemawa rayuwata" ta fada tana gyara dakin yaran da suka bata tare da killace kayan makarantarsu gu guda kafin su dawo su wanke
Baki daya sai aka koma 'yar gidan jiya kan halayen mukhtar,yayin da bangare guda sauyawar yaranta da hajiya ke ciwa kariman tuwo a qwarya,saidai ta kammala dukkan wani shirinta na maida hannun agogo baya ranar kawai take jira,wanda hakan ya sanya ta sanyawa kowa ido,wannan kuma ya bada damar da shaquwa mai qarfi taci gaba da gudana tsakanin sumayya yaran da hajiyar.
****** ******* ******
Qarfe daya na rana ne wanda saika dauka qarfe takwas ne na safe saboda yanayin sanyin da ake zabgawa a garin,tuni ta kammala abincin rana ita da mai aikin gidan qwaya daya saboda biyu na rana yaran zasu dawo ta baiwa kowa haqqinsa,kasancewar tunda karima ta dawo gidan bata ko dubi kitchen ba.
A hankali sai abun ya soma cin tura,hatta idan yana bacci bai da aiki sai kiran sunan karima,idan ya tashi kuwa washegari haka zai yini babu wannan walwalar sam.haka kawai yake jin rayuwarsa da zuciyarsa cikin takura da qunci,ji yake kamar yana cikin wata kurkuru,burinsa kawai yaga karima cikin gidan,saidai duk da haka bai taba furtawa sumayya ba.
*_Bayan sati d'aya_*
Bayan sallar isha'i ne dukkansu suna zaune a falom gidan banda hajiya dake bangarenta saboda yau da wuri ta kwanta,sumayya da nuratu da nuwaira na zaune tana koya musu aikin gida(assigment)da aka basu a makaranta,basma na saman kujera tana bacci tun sanda suka gama cin abincin dare,sai islam dake kwashe kwanukan da suka ci abinci da su tana shigarwa kitchen.
Lukman ne ya fito falon a gaggauce wanda tunda ya dawo daga kasuwa yana cikin daki bai fito ba sai yanzu,hannunsa riqe da dan mukulli,daya hannun nasa kuma riqe da hularsa,kana ganinsa kamar wanda aka jefo ko aka tunkudo,daga kai sumayya tayi tana dubansa sanda ya giftasu zai fice ganin bai cewa kowa komai ba
"Abban nuwaira" waiwayowa yayi yana dubanta tare da amsawa
"Ina zaka fita haka tara na dare?" Ta fada a marairaice
"Sorry airphort zani,yanzu zamu dawo" ya fadi yana ficewa da sauri jin wayarsa na ringing,kanta ta maida suka ci gaba da assigment din da yaran,hakanan taji gabanta na yawaita faduwa,hasbunallahu wa ni'imal wakil ta dinga maimaitawa,suna gamawa ta tattara yaran duka suka tafi dakinsu,sai da kowa ya sanya kayam baccinsa ya karanta addu'ar kwanciya bacci suka kwanta sannan ta rufo musu dakin ta koma nata dakin,alwala tayu tayi shafa'i da wutirinta sannan ta zauna ta karanta suratul mulk,har ta gama abinda take bata ji shigowarsa ba,saboda haka ta sanya hijabinta ta nufi bangaren hajiya.
A kashingide ta sameta riqe da carbi,ganin sumayyan ya sanyata zama tana murmushi
"Yanzu kuwa nake zancanki a zuciyata" itama murmushin take tana cewa
"Hajiya baki bacci ba?"
"Kin ganni nan wlh banyi ba,gabana ne yake ta faduwa sai na tuna dazu banyi waraddallahu ba,sai nake yinta yanzu (waraddallahul lazina kafaru bi gaizihim lam yanaluu khairaa,wa khafallahul mu'umininal qital,wa kanallahu qawiyyan aziza,ana karanta ta ne qafa dari bayan sallar asaba kariya daga dukkan kaidin wani maqiyi dake nufarka da shi in sha Allah)"
"Ai gwara hajiya" ta fada tana tunanin faduwar gaban da itama take ji tayi dai dai data hajiya kenan
"Ina lukman din kuma?"
"Ya dan fita ne hajiya yara kuma sun kwanta saboda makaranta goben"
"Sannunki kedai sumayya,Allah yayi albarka" "amin hajiya"ta fada tana murmushi kanta a qasa,shiru ne ya biyo baya kafin su soma taba hira kadan kadan,ganin har sha daya na dare tayi ya sanyata yiwa hajiyan sallama ta koma sashenta.
Tana zaune har sha daya da rabi sannan taji muryar lukman,a hankali ta tashi ta leqa,shine a gaba janye da akwati daya hannun jaka,sai KARIMA dake biye da shi a baya,da sauri ta saki labulen ta koma da baya tana kiran sunayen Allah,sannu a hankali nutsuwa ta saukar mata,sai ta daura alwala ta kwanta,don jikinta na bata lukman ba zaya nemeta a yau ba.
Ilai kuwa bata sake jin motsinsa ko na karima ba har bacci yayi awon gaba da ita.
****** ******* *****
Washegari yadda suka saba haka tayi bata fasa ba,ita ta tashi yaran baki daya sukayi sallar asuba,sannan ta dafa ruwa mai zafi islam ta fara yi sannan nuwaira ta dinga yiwa qananan tana tura su islam na shiryasu ita kuma tayi daga qarshe,sumayya kuma na kitchen tana hada breakfast da wanda zasu tafi da shi makaranta,abinda dukka a da basu saba yi ba amma a yanzu ya zame musu jiki.
Sun shirya tsaf suna karyawa ya zagaya ta buga dakin karima don taga idan sun tashi ta tura yaran su gaida mamansu kan su wuce,saidai har ta gama bugunta ko tari bata ji anyi ba,abinda bata sani ba lukman na jin bugun,ya kuma san sumayyarsa ce,kamar ya zura a guje ya bude saidai ina sam bai isa ba,saboda bai samu umarni ba,tunda ta dawo a jiyan qasan zuciyarsa ke a cunkushe cike da baqinciki bacin rai da tsananin tsoronta,amma a fili tsantsar farinciki ne da tsananin biyayya bayyane a fuskar tasa,abinda zai baka mamaki tunda ta dawo bai taba kwatanta tambayarta inda ta tafi da aurensa a kanta ba kuma ba tare da izininsa ba har na tsawon wata biyu ba,a lokacin ma yana bandaki yana wanke mata tana son shiga wanka saidai ya hada qura a tsawon wata biyu da bata nan tunda ba wani ke shiga ba gun nata na a rufe ne.
Dawowa tayi inda suke kowa ya kammala mai adaidaitan dake kaisu ma ya iso ta dubesu
" mamanku fa ta dawo jiya da daddare"ta tsammaci zata ga tsantsar farinciki a fuskokinsu,sai taga babu yabo ba fallasa,babu wani zumudi ko doki,nuwaira kuwa tsoro da fargaba ne ma ya mamayeta,a haka ta rakasu suka fice sannan ta dawo ta gyara falo zuwa kitchen ta barwa mai aikinsu wanke wanke idan ta iso tayi wanka ta leqa bangaren hajiya,sai ta sameta tana bacci,saboda haka ta mata 'yan gyare gyarenta ta fito ta barta ta dawo falo ta zauna tana jira sha daya da rabi tayi ta karya,sai ta kunna t.v tana kallon arewa 24 don ta debe mata kewa,zuwa yanzu sum shaqu sosai da yaran,idan basa tare duk sai taji babu dadi kasancewarta mai son yara.
Tana jiyo qarar bude qofar karima amma bata maida hankalinta kai ba har sai da taji cikin taqama tana fadin
"Ina yara na" cikin ladabi kamar bawa da uban gidansa taji lukman na cewa
"Eh sun tafi makaranta ai sumayya ta turasu" cikin harzuqa tace
"Eh wato suma an shige musu za'a shanyesu a rabani da su kenan?" Sai ta saki wani shu'umin murmushi tana kada kai
"Mu zuba mu gani,muje ka rakani naga hajiya nata salon ita kuma" ta fada tana yin gaba,jiki na rawa yana tafe yana waiwayen sumayya yabi bayanta,kai ta jinjina bayan fitarsu
"Innalillahi wa 'inna ilaihi raji'un" ta fada tana kada kai ganin hannun agogo nason komawa baya game da lamarin lukman din.
Zuwanta gun hajiyan ta taddata fiye da yadda ma ta barta,don fada hajiyan ma ta mata kan dalilin tafiyarta wani gu bayan tana da aure,sosai hajiyan keji qarfin zuciyarta sam babu wani dar da taji balle taji tsoron karimar,sai lokacin ta yadda lallai idan kayi sakaci da addu'a babu abinda ba zaya iya faruwa da bawa ba duk da cewa akwai QADDARA amma babu abinda ke sauya qaddarar irin ADDU'A.
Ko da rana da yaran suka dawo sun gaidata,baki ta saki tana kallon yadda suka sauya baki daya,tana kallon yadda suke girmama nuwaira da islam,lallai sumayya ta sauya mata yara,ya akayi bata sanya an musu farraqu ba ita da au ta barsu suka shaqu haka,tana gani suka sauya kayansu zuwa na islamiya bayan sunci abinci,suna sanya hijabansu sumayya na tsakiyarsu tana hada musu litattafan islamiyar su kariman ta banko qofar dakin tana huci,tsayawa tayi tana dubansu fuska a tsuke,sumayya data kalleta saita maida kai taci gaba da abinda take
"Laaa,mama bakiyi sallama ba fa,kuma babu kyau shiga gu ba sallama" nuratu ta fada,mamaki ya kama kariman sai ta waiwaya tana kallonta amma sai ta wayance da cewa
"Ku cire kayan nan,babu wata makaranta da zaku sake zuwa daga dawowarku daga boko ko hutawa bakuyi ba" islam ce ta maqe wuya tana cewa
"Mama ki barmu muje,idan mun dawo ma huta din,idan kana fashi fa ana wuceka a karatun" ido ta kuma zarowa mamki na sake kasheta,lallai sumayya tayi amfani da irin surkullensu ta rabata da yaranta,tsawa ta daka musu tana cewa
"Don ubanki da ni kike jayayya,ku cire kayanku nace babu inda zaku" sumayya ce ta bar abinda take ta tako zuwa inda take tana cewa
"Haba maman nuratu,meye na zagi har haka?,ina cewa ke zaki fi kowa farincikin zuwan yaranki makaranta,ba girmanki bane" sai ta waiwaya ga yaran da sukayi carko carko suna kallon karimar
"Maza ku wuce ku tafi mamarku ta haqura" da sauri suka fice kuwa daya bayan daya,sai da suka kammala ficewa tas sannan karima ta kalli sumayya
"Yaro man kaza,ke da su baki daya baku da bambanci a gurina,lokaci na baki shi nake jira" tana gama fada ta fita
"Allah ya fiki,Allah ya isar min da ke akan dukkan wani nufinki,alkhairin ubangiji nake nemawa rayuwata" ta fada tana gyara dakin yaran da suka bata tare da killace kayan makarantarsu gu guda kafin su dawo su wanke
Baki daya sai aka koma 'yar gidan jiya kan halayen mukhtar,yayin da bangare guda sauyawar yaranta da hajiya ke ciwa kariman tuwo a qwarya,saidai ta kammala dukkan wani shirinta na maida hannun agogo baya ranar kawai take jira,wanda hakan ya sanya ta sanyawa kowa ido,wannan kuma ya bada damar da shaquwa mai qarfi taci gaba da gudana tsakanin sumayya yaran da hajiyar.
****** ******* ******
Qarfe daya na rana ne wanda saika dauka qarfe takwas ne na safe saboda yanayin sanyin da ake zabgawa a garin,tuni ta kammala abincin rana ita da mai aikin gidan qwaya daya saboda biyu na rana yaran zasu dawo ta baiwa kowa haqqinsa,kasancewar tunda karima ta dawo gidan bata ko dubi kitchen ba.