Sashe 152
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shi da kanshi yake tuqa motar zuwa filin sauka da tashin jirage na qasar,yayin da m'aikatansa biyu ke binsu a wata motar ta daban dake bayansu,har suka isa airphort din wani farinciki na ratsata,musamman data duba ticket dinta taga jirgin zai sauka kano ne,hakan na nuna cewa gida zata fara isa,waiwayowa tayi sanda aka fara kira matafiyan da zasu tashi zuwa nijeria ta dubeshi,sai ta sadda kai ta rasa me zata ce
"Allah ya tsare,ki gaida su"ya fada hannayensa zube cikin aljihunsa,wani yanayi ke ratsashi wanda baisan na meye ba,kamar wani abu na neman gushewa daga gareshi wanda ya jibanceshi,ranshi a bace yake haka kawai baijin duk wani karsashi da farinciki,dagowa tayi ta dubeshi suka hada idanu
"zasu ji,na gode"
"Ba case" ya fada yana ci gaba da dubanta ba tare da ya janye idanuwanshi ba,a hankali ta daga qafafunta tana takawa,tana jin idanuwanshi a kanta,ita dinma sai taji karsashinta da murnarta na dan raguwa,sabo ne take zato wanda hausawa ke cewa turken wawa,ko dabba ce kana tare da ita randa kuka rabu sai kaji wani iri,yana nan tsaye hakanan ya kasa tafiya har ta bacewa ganinshi sannan ya juya a hankali ya bar wajen,kwance yayi cikin salo na kashingida abayan motar drivan ka janshi wanda ya kama tashar gidan redion dake qasar,umarni mustapha ya bashi kan ya kashe,baison hayaniya,
"Sorry sir" ya fada yana kasheta.
Cikin awannin da basu da yawa suka iso qasata nijeria,tuni mota daga gidan baba prof dake kano ta iso tana jiran ta,tamkar jira wayarta take ta soma ruri network ya dawo,ta laluba aljihun jakar na baya ta zaro wayar tana dubawa,amira ce,murmushi ya subuce mata tana mirgina kai
"Wohoho amira,i missed you wallahi so much" ta fada a fili sanda take shigewa bayan motar sannan ta daga wayar,wani ihu da amiran ta sakiwa kunnuwanta sai data rufe ido
"Kunne na amira kunne na"
"Wallahi kaman a mafarki namecy ashe kin iso,last week muka je umra na takurawa my saif sai munje wajenki wallahi yaqi wai nauyin ya musty yake ji,wayyo namecy kina ina?"
"Saukata kenan ko gida ban qarasa ba,ina mota a kani na sauka,next week insha Allah zan qaraso"
"Qarasa gida namecy ki huta akwai labarai wallahi" ta fada tana dariya,murmushi sumayya ta saki
"To ba damuwa"
"Ki gaidan mama,amma fa idan naga ba dama zan biyoki na zaqu wallahi naga matar yaya na" dariya suka sa baki daya sumayya ta kashe wayar,har yau amira halin dai bai sauya ba.
Saboda murna bata iya tsayawa an shiga mata da kayanta ba,wanda itama batsan da kayan bama sai da suka sauka ta gansu,da sallama ta kutsa kai tsakar gidan,wata dake shirin shiga kitchen ta dakata ta juyo,halima ce,ta zama wata babbar mace,haliman da ake zaton ba zatayi qiba ba saiga kumatu a fuskarta,da gudu ta nufo sumayya suia rungume juna kowa na ambatar sunan dan uwansa,hayaniyar ita ta sanya mama dake falon ta daga labule ta leqo
"Kada dai kicemin gudu kike halima me yasa kike da kunnen qashine wai?" Sak maman tayi sanda sumayya ke dagowa,bakinta har kunne,da hanzari sumayya ta saki halima ta nufi mama tana kiran sunanta,hannayen mama ta kama ta riqe gam qwalla na taruwa a idonta
"Me kuma na kukan ne sumayya?" Maman ta fada cikin farinciki sanda sumayyan ta fada jikinta,dakin suka shige baki daya farinciki zuciyar kowannansu ba magana.
Nan da can kowa ya kasa motsawa cikinsu,anata hirar yaushe rabo,mama nata kallon sumayyan,farinciki na zagayata,bata taba ganin diyar tata cikin kyakkyawan yanayi makamancin wannan ba tunda take aure,wani kyau haiba da cikar kamala,ta sake zama babbar mace qwarai,da alama hankali ya fara gameta,ita kuma sumayyan na duban halima sannan ta dubi mama
"Wai dama mama halima zatayi qiba?" Murmushi ya subucewa maman
"Gata nan kuwa sumayya"
"Masha Allah,lallai abdur rahman ya iya kiwo"
"Har ya kai yayanmu,wai baki kallon madubi ne yaya,wallahi sanda kika shigo na zaci baquwar balarabiya mukayi Allah kuwa kada ki dauka sharri ne ko mama baki gani ba?" Murmushin jin dadi maman ta saki
"Masha Allah kam" sai kunya ta kama sumayya tadan rausayar da kai,idanunta ya sauka kan abdallah dake kwance yana bacci,baki ta bude
"Kai dama mama yaron nan na gunki?" Dubanshi sukayi baki daya
"Sunzo dai tare da mamarshi halima,abdur rahman yayi uwa yayi makarbiya ya karbe abdallah daga gunmu baki daya,baki ga dambun tsiyar da aka dinga yi tsakaninsa da yahanasu ba amma yace saidai tayi haquri shida mu saidai ziyara" kai take gyadawa taba duban halima,dariya ta saki
"To ai koni bazan bada abdallah ba Allah yanzu ko kece saidai ki haqura" dariya ta saki
"Ni meye mawa,dama abdallah ai danku ne,kuyi duk yadda kuka ga dama da shi,Allah ya qara zumunci" miqewa mama tayi ta basu waje don sauke tukunyar abinci,wanda halima ba zata iya ba sabida an hanata duk wani motsi mai qarfi sabida juna biyun da take da shi wanda bai wuce wata daya da rabi ba,a nan haliman ke gayawa sumayya da kuma barin da zainab tayi wanda ita taje dubawa ma ta biyo ta gida,baki sumayya ta saki tana dariya tare da duban halima
"Kai halima ko kunyata bakiji,Allah ya inganta mana ya raba lafiya" cikin jin 'yar kunya ta amsa.
Sosai sumayyan ta zage ta daki abincin,ba qaramin missing abincin gida tayi ba,wanda kullum suna fama dana hotel,wanda idan ba fried rice ba bata iya cin wani abu sosai saidai kawai ta taba sama sama,da qyar ta yakice ta kira nafisa ta shaida mata zuwan ta,kamar ta ballo itama tazo haka take ji,amma sumayyan ta gaya mata satin sama tana tafe,tace tana nan tana jiranta,daga nan anty dije ta kira,bakin antyn har kunne,itama ta zaqu taga sumayyan,sun dan jima kan layi kafin suyi sallama,sun sha hira qwarai,a nan mama ke bata labarin irin gidajen gonar da baba prof ya damqawa malam yace nashine,tun tsohuwar dukiyarsa da bai tsaya da juya masa ba,irin hayayyafar da tayi,kai kawai sumayyan ke kadawa,babu shakka samun abota irin wannan tana da wuya a wannan zamanin,wani qima da mutuncin baba ke sake hauhawa cikim zuciyar sumayya,qaunarsa na sake kamata,qauna ta fisabilillahi wanda tun kafin tasan matsayinsa wajen mahaifinsu take masa ita
"Allah ya saka da alkhairi ya cika masa burikansa duniya da lahira" amsawa itama maman tayi,tana sake gaya mata ci gaban da aka samu,kwanaki kadan ya rage subar wannan gidan zuwa wani sabin gidan da malam din ya saya,wanda da baba ne zai biya malam din yaqi,dawainiyar da karamcin tayi yawa inji malam.
Farincikin da malam yaji sanda yaga diyar tashi ba mai misaltuwa bane,ido ba mudu ba yasan kima,yasan cewa bisa dukkan alamu addu'ar da yake binsu da ita dare da rana zatayi tasiri a kansu,sun jima sosai suna hira da malam har kusan sha daya na dare,shi da kansa ya sake warware mata abinda ya faru na danqa masa gidajen gonakinsa da baba yayi,wanda har yau basu ma je na wasu garuruwan ba,addu'a sosai ta yiwa baban malam na amsawa.
Washegari tare suka karya ita da malam din da abdallah,wanda abdur rahman yace a barshi yaga mamanshi har sanda zata tafi,shi kansa abdur rahman din tsokanarta ya dinga yi yana cewa manyanmuyaya sumayya,raha suka yi sosai kamar babu wani abu da ya taba faruwa tsakaninsu,dariya ta dinga kawai,shi kansa ya sauya ya sake zama magidanci,alamun hutu da kwanciyar hankali baki daya sun bayyana tattare da shi,cikin zuciyarta tana gode ma Allah,tasan ko ba komai 'yar uwarta na cikin rayuwar jin dadi da walwala kamar yadda take fata.
Kwalayen jiya ta bude ta duba,uwar tsaraba ce a ciki,akwai wasu dake nannade da sunayen malam da baba,bata taba ba ta miqa musu cikin mamaki,sai take jin wata qimarsa cikin ranta
(Gareku maza,abune mai kyau ka dinga kyautatawa iyaye da 'yan uwan matarka,don haka na qara qimarka a idanunsu da idanun matar taka gaba daya,ko yaya alkhairi yake dadi gareshi,Allah ya hore ya kuma bada iko amin),sai data gama sannan ta shirya zuwa gidan zainab,ranan can ta wuni baki daya,ta sameta cikin kyakkyawan yanayi itama kamar 'yar uwarya,jikin nata ma ya warware gaba daya,washegari kuma gidan yaya yahanasu ta wuni,kallonta yayan ta dinga tana qarawa,har sai data kasa shiru
"Allah qadiran ala may yasha'u,ashe sumayya ke din rabon wani ce da muntarinmu ba,kowanne bawa da kalar tashi qaddarar" ta fada tana matse hawaye,hakan ya sosa tabon dake zuciyar sumayyan,duk da haka sai ita ta lallashi yaya yahanasun,sai la'asar taje ta gaida hajiyan bahijja da abdur rahman,sosai taji dadin ganin sumayyan,ita ta tsaidata ma bata wuce gida ba sai magariba.
Again washegari kuma gidan yaya abubkar ta wuni,amina ta rasa inda zata sanyata saboda murna,itama dubanta take kamar yadda kowa kallonta,sosai sumayyan ta sauya mata cikin 'yan watanni
"Masha Allah sumayya masha Allah,dama haka almustaphan naki ya iya kiwo?"
"Kai anty kai" ta fada tana qyalqyala dariyar irin yadda meena tayi maganar.
****** ******* *******
Qarfe sha daya na dare ya dawo daga office din,baki daya ranar ya maida kanshi busy,sosai ya tsaya da kanshi cikin kamfanin yana zagayawa waje waje yana ganin yadda ma'aikatan ke gudanar da aikinsu,abinda tunda suka taho tare da sumayyan baiyi ba,baisan me ya hanashi ba,daga qarshe ya tuqe a warehouse nasu,hamza ne ya dubeshi a gajiye
"Gaskiya maan na gaji gida zan wuce,magariba fa ta gota,na tabbata abida na can na zuba ido" cikin ko in kula yana duban bangaren da suke ajjiye kayan aikinsu yace
"Wani ya hanaka tafiya?"
"Ok,dama kai na tsaya,na lura kuma kai yau aikin naka ba mai qarewa bane,ko don yau gauro kake?" A nutse ya waiwayo ya maka masa harara
"Ba yau na fara ba bare ka gaya min ba dadi" dariya hamza ya saka
"Gaskiya ne wannan,ko zaka zo mu wuce tare kaci abinci wajena?"
"Bana buqata" ya fada yana ci gaba da takawa hannunsa zube a aljihu,haka kawai yake jin sam baida sha'awa ko karsashin komawa hotel din,a haka hamza ya juya ya fice ya barshi a wajen,yasan tunda yace bashi zuwa to bazashi din ba.
"Allah ya tsare,ki gaida su"ya fada hannayensa zube cikin aljihunsa,wani yanayi ke ratsashi wanda baisan na meye ba,kamar wani abu na neman gushewa daga gareshi wanda ya jibanceshi,ranshi a bace yake haka kawai baijin duk wani karsashi da farinciki,dagowa tayi ta dubeshi suka hada idanu
"zasu ji,na gode"
"Ba case" ya fada yana ci gaba da dubanta ba tare da ya janye idanuwanshi ba,a hankali ta daga qafafunta tana takawa,tana jin idanuwanshi a kanta,ita dinma sai taji karsashinta da murnarta na dan raguwa,sabo ne take zato wanda hausawa ke cewa turken wawa,ko dabba ce kana tare da ita randa kuka rabu sai kaji wani iri,yana nan tsaye hakanan ya kasa tafiya har ta bacewa ganinshi sannan ya juya a hankali ya bar wajen,kwance yayi cikin salo na kashingida abayan motar drivan ka janshi wanda ya kama tashar gidan redion dake qasar,umarni mustapha ya bashi kan ya kashe,baison hayaniya,
"Sorry sir" ya fada yana kasheta.
Cikin awannin da basu da yawa suka iso qasata nijeria,tuni mota daga gidan baba prof dake kano ta iso tana jiran ta,tamkar jira wayarta take ta soma ruri network ya dawo,ta laluba aljihun jakar na baya ta zaro wayar tana dubawa,amira ce,murmushi ya subuce mata tana mirgina kai
"Wohoho amira,i missed you wallahi so much" ta fada a fili sanda take shigewa bayan motar sannan ta daga wayar,wani ihu da amiran ta sakiwa kunnuwanta sai data rufe ido
"Kunne na amira kunne na"
"Wallahi kaman a mafarki namecy ashe kin iso,last week muka je umra na takurawa my saif sai munje wajenki wallahi yaqi wai nauyin ya musty yake ji,wayyo namecy kina ina?"
"Saukata kenan ko gida ban qarasa ba,ina mota a kani na sauka,next week insha Allah zan qaraso"
"Qarasa gida namecy ki huta akwai labarai wallahi" ta fada tana dariya,murmushi sumayya ta saki
"To ba damuwa"
"Ki gaidan mama,amma fa idan naga ba dama zan biyoki na zaqu wallahi naga matar yaya na" dariya suka sa baki daya sumayya ta kashe wayar,har yau amira halin dai bai sauya ba.
Saboda murna bata iya tsayawa an shiga mata da kayanta ba,wanda itama batsan da kayan bama sai da suka sauka ta gansu,da sallama ta kutsa kai tsakar gidan,wata dake shirin shiga kitchen ta dakata ta juyo,halima ce,ta zama wata babbar mace,haliman da ake zaton ba zatayi qiba ba saiga kumatu a fuskarta,da gudu ta nufo sumayya suia rungume juna kowa na ambatar sunan dan uwansa,hayaniyar ita ta sanya mama dake falon ta daga labule ta leqo
"Kada dai kicemin gudu kike halima me yasa kike da kunnen qashine wai?" Sak maman tayi sanda sumayya ke dagowa,bakinta har kunne,da hanzari sumayya ta saki halima ta nufi mama tana kiran sunanta,hannayen mama ta kama ta riqe gam qwalla na taruwa a idonta
"Me kuma na kukan ne sumayya?" Maman ta fada cikin farinciki sanda sumayyan ta fada jikinta,dakin suka shige baki daya farinciki zuciyar kowannansu ba magana.
Nan da can kowa ya kasa motsawa cikinsu,anata hirar yaushe rabo,mama nata kallon sumayyan,farinciki na zagayata,bata taba ganin diyar tata cikin kyakkyawan yanayi makamancin wannan ba tunda take aure,wani kyau haiba da cikar kamala,ta sake zama babbar mace qwarai,da alama hankali ya fara gameta,ita kuma sumayyan na duban halima sannan ta dubi mama
"Wai dama mama halima zatayi qiba?" Murmushi ya subucewa maman
"Gata nan kuwa sumayya"
"Masha Allah,lallai abdur rahman ya iya kiwo"
"Har ya kai yayanmu,wai baki kallon madubi ne yaya,wallahi sanda kika shigo na zaci baquwar balarabiya mukayi Allah kuwa kada ki dauka sharri ne ko mama baki gani ba?" Murmushin jin dadi maman ta saki
"Masha Allah kam" sai kunya ta kama sumayya tadan rausayar da kai,idanunta ya sauka kan abdallah dake kwance yana bacci,baki ta bude
"Kai dama mama yaron nan na gunki?" Dubanshi sukayi baki daya
"Sunzo dai tare da mamarshi halima,abdur rahman yayi uwa yayi makarbiya ya karbe abdallah daga gunmu baki daya,baki ga dambun tsiyar da aka dinga yi tsakaninsa da yahanasu ba amma yace saidai tayi haquri shida mu saidai ziyara" kai take gyadawa taba duban halima,dariya ta saki
"To ai koni bazan bada abdallah ba Allah yanzu ko kece saidai ki haqura" dariya ta saki
"Ni meye mawa,dama abdallah ai danku ne,kuyi duk yadda kuka ga dama da shi,Allah ya qara zumunci" miqewa mama tayi ta basu waje don sauke tukunyar abinci,wanda halima ba zata iya ba sabida an hanata duk wani motsi mai qarfi sabida juna biyun da take da shi wanda bai wuce wata daya da rabi ba,a nan haliman ke gayawa sumayya da kuma barin da zainab tayi wanda ita taje dubawa ma ta biyo ta gida,baki sumayya ta saki tana dariya tare da duban halima
"Kai halima ko kunyata bakiji,Allah ya inganta mana ya raba lafiya" cikin jin 'yar kunya ta amsa.
Sosai sumayyan ta zage ta daki abincin,ba qaramin missing abincin gida tayi ba,wanda kullum suna fama dana hotel,wanda idan ba fried rice ba bata iya cin wani abu sosai saidai kawai ta taba sama sama,da qyar ta yakice ta kira nafisa ta shaida mata zuwan ta,kamar ta ballo itama tazo haka take ji,amma sumayyan ta gaya mata satin sama tana tafe,tace tana nan tana jiranta,daga nan anty dije ta kira,bakin antyn har kunne,itama ta zaqu taga sumayyan,sun dan jima kan layi kafin suyi sallama,sun sha hira qwarai,a nan mama ke bata labarin irin gidajen gonar da baba prof ya damqawa malam yace nashine,tun tsohuwar dukiyarsa da bai tsaya da juya masa ba,irin hayayyafar da tayi,kai kawai sumayyan ke kadawa,babu shakka samun abota irin wannan tana da wuya a wannan zamanin,wani qima da mutuncin baba ke sake hauhawa cikim zuciyar sumayya,qaunarsa na sake kamata,qauna ta fisabilillahi wanda tun kafin tasan matsayinsa wajen mahaifinsu take masa ita
"Allah ya saka da alkhairi ya cika masa burikansa duniya da lahira" amsawa itama maman tayi,tana sake gaya mata ci gaban da aka samu,kwanaki kadan ya rage subar wannan gidan zuwa wani sabin gidan da malam din ya saya,wanda da baba ne zai biya malam din yaqi,dawainiyar da karamcin tayi yawa inji malam.
Farincikin da malam yaji sanda yaga diyar tashi ba mai misaltuwa bane,ido ba mudu ba yasan kima,yasan cewa bisa dukkan alamu addu'ar da yake binsu da ita dare da rana zatayi tasiri a kansu,sun jima sosai suna hira da malam har kusan sha daya na dare,shi da kansa ya sake warware mata abinda ya faru na danqa masa gidajen gonakinsa da baba yayi,wanda har yau basu ma je na wasu garuruwan ba,addu'a sosai ta yiwa baban malam na amsawa.
Washegari tare suka karya ita da malam din da abdallah,wanda abdur rahman yace a barshi yaga mamanshi har sanda zata tafi,shi kansa abdur rahman din tsokanarta ya dinga yi yana cewa manyanmuyaya sumayya,raha suka yi sosai kamar babu wani abu da ya taba faruwa tsakaninsu,dariya ta dinga kawai,shi kansa ya sauya ya sake zama magidanci,alamun hutu da kwanciyar hankali baki daya sun bayyana tattare da shi,cikin zuciyarta tana gode ma Allah,tasan ko ba komai 'yar uwarta na cikin rayuwar jin dadi da walwala kamar yadda take fata.
Kwalayen jiya ta bude ta duba,uwar tsaraba ce a ciki,akwai wasu dake nannade da sunayen malam da baba,bata taba ba ta miqa musu cikin mamaki,sai take jin wata qimarsa cikin ranta
(Gareku maza,abune mai kyau ka dinga kyautatawa iyaye da 'yan uwan matarka,don haka na qara qimarka a idanunsu da idanun matar taka gaba daya,ko yaya alkhairi yake dadi gareshi,Allah ya hore ya kuma bada iko amin),sai data gama sannan ta shirya zuwa gidan zainab,ranan can ta wuni baki daya,ta sameta cikin kyakkyawan yanayi itama kamar 'yar uwarya,jikin nata ma ya warware gaba daya,washegari kuma gidan yaya yahanasu ta wuni,kallonta yayan ta dinga tana qarawa,har sai data kasa shiru
"Allah qadiran ala may yasha'u,ashe sumayya ke din rabon wani ce da muntarinmu ba,kowanne bawa da kalar tashi qaddarar" ta fada tana matse hawaye,hakan ya sosa tabon dake zuciyar sumayyan,duk da haka sai ita ta lallashi yaya yahanasun,sai la'asar taje ta gaida hajiyan bahijja da abdur rahman,sosai taji dadin ganin sumayyan,ita ta tsaidata ma bata wuce gida ba sai magariba.
Again washegari kuma gidan yaya abubkar ta wuni,amina ta rasa inda zata sanyata saboda murna,itama dubanta take kamar yadda kowa kallonta,sosai sumayyan ta sauya mata cikin 'yan watanni
"Masha Allah sumayya masha Allah,dama haka almustaphan naki ya iya kiwo?"
"Kai anty kai" ta fada tana qyalqyala dariyar irin yadda meena tayi maganar.
****** ******* *******
Qarfe sha daya na dare ya dawo daga office din,baki daya ranar ya maida kanshi busy,sosai ya tsaya da kanshi cikin kamfanin yana zagayawa waje waje yana ganin yadda ma'aikatan ke gudanar da aikinsu,abinda tunda suka taho tare da sumayyan baiyi ba,baisan me ya hanashi ba,daga qarshe ya tuqe a warehouse nasu,hamza ne ya dubeshi a gajiye
"Gaskiya maan na gaji gida zan wuce,magariba fa ta gota,na tabbata abida na can na zuba ido" cikin ko in kula yana duban bangaren da suke ajjiye kayan aikinsu yace
"Wani ya hanaka tafiya?"
"Ok,dama kai na tsaya,na lura kuma kai yau aikin naka ba mai qarewa bane,ko don yau gauro kake?" A nutse ya waiwayo ya maka masa harara
"Ba yau na fara ba bare ka gaya min ba dadi" dariya hamza ya saka
"Gaskiya ne wannan,ko zaka zo mu wuce tare kaci abinci wajena?"
"Bana buqata" ya fada yana ci gaba da takawa hannunsa zube a aljihu,haka kawai yake jin sam baida sha'awa ko karsashin komawa hotel din,a haka hamza ya juya ya fice ya barshi a wajen,yasan tunda yace bashi zuwa to bazashi din ba.