Sashe 145
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 7 min read
A reception ya tsaya ya karbi muqullin motar sannan suka fice tana gaba yana bayanta.
A hankali suke takawa suna wucewa zuwa gurin ajiyar motoci,abun mamaki duk inda suka gifta tun daga cikin hotel din sai sun dauki hankali,tsammata ake wasu shaqiqan masoya ne,yanayin shigar kowannensu ya dace da shi,a haka har suka qarasa wajen motar,da kanshi yau zaiyi driving din saboda haka kai tsaye ya wuce mazaunin driver.
Wani nutststsen tuqi yake yi wanda ke qarawa zuciya da ruhi nutsuwa,bazaiyi qarya ba kam yau wani annushuwa yake ji,hakan kuma yaba tunanin bai rasa nasaba da warwarewar matsalarsa cikin sauqi,shiru kake jin motar,idanunta na bisa titi a fakaice tana qarewa garin kallo,haqiqa yayi matuqar tafiya da ita fiye da uk da ta je,gari ne mai cike da qyale qyale da kayan qawa masu matuqar jan hankali,dan satar kallonta yayin kafin ya maida kanshi bisa titi
"Thanks" taji ya ambata,a hankali ta maida idanunta kanshi wanda titi yake kalla kafin ya dauke kanta,murya qasa tace
"Dame fa?" Shiru ya biyo baya kamar bazai amsa ba,har tayi zaton ma ya bar zancan sai taji ya kuma cewa
"Shukhran alat taujih" sake daga kanta tayi tana dubanshi murmushi na son subuce mata,ta rasa ya akayi yaji larabci haka,wati dazun tayi shuka ne idon makwarwa,ta gode Allah da ba wata magana ta fadi ba,sai ta kauda kanta
"Babu komai,abinda ya kamata ne nayi shi" sosai maganar ta burgeshi,kusan shi daya yake warware matsalolinshi idan sun taso mashi ya riga ya saba,shi yasa wannan karon yake jin tayi mishi wani gagarumin aiki data cancanci a gode mata,ba shakka samun abokin shawara da yin shawara a kuma baka shawarar yana da matuqar muhimmanci kamar yadda ummee ta saba gaya masa
"Ko zaiyiwu na riqeki personal adviser?"
"Aikin kowacce macen gida ce matuqar an lamunce mata hakan" itama ta fada ba tare data dubeshi ba,tana jin qarin mamakinsa cikin ranta,kamar yasha wani abu ne?,wannan ne karon farko tsawon sanayyarta da shi da suka taba zance mai tsahi makamancin hakan,ta nashi bangaren mamakin irin tata baiwa da fasahar yake,yana ganin matan arewa basu da wannan fikirar amma a yanzu yaga guda daya?,haka suke ko kuwa wannan ce kawai?(hmmm,mun wuce haka ma malam almustapha,muje dai zuwa).
Bai tsaya ko ina ba sai zabeel park,tunda suka shiga wajen yayi matuqar qayatar da ita,karon farko a rayuwarra data taba shiga wani park,guri ne da family kan iya zuwa,miji da mata da yaransu,koma miji da mata kawai,a hankali suke takawa jere da juna,saidai idanuwanta na wulqawa ko ina tana kalle kalle abinta cikin hikima ba tare daka fuskanci ta matowa gurin ba,wani sashe daban suka nufa wanda ke dauke da wasu rubuce rubuce na SEASON four dubai garden glow,hakan ke nuna lokaci lokaci wajen ke a bude,gurin biyan kudin shiga ya biya aka nasu ticket sannan suka shige.
Bata taba ganin abubuwan data gani cikin garden din ba,wani irin garden ne da aka baje fasaha wajen yinsa,kowa na harkarshi cikin wajen,kama da yara qananu da matsakaita,maza da mata,masoya gasunan birjik kowa na baje kolin tashi soyayyar,wani guri na musamman suka yi mazauni sanda wayarshi ta fara ruri ya cirota yana qoqarin amsawa yayin da ita kuma taci gaba da bawa idanunta abinci,a hankali idanuwanta suka sauka kan wani family,miji da mata ke sai yaransu uku,mace babba sai mai bi mata namiji sai qaramin shima namiji,a yadda suke raha kana kallonsu kasan banu abinda ya shafi rayuwarsu,sisai yaron suka burgeta kasancewarta mutum mai son yara qwarai,suna ta wasanninsu suna kaiwa suna kawowa wajen iyayensu,ta sake dauke idanunta ta maida kan wasu matasa biyu mace da namiji,namijin ke bawa macen ice cream yana ta faman lallabata ya kasa ya tsare,tayasu dariya tayi ta hanyar sakin murmushi sanda ya dangwala kata shi kan hancinta sanyinsa ya ratsata ta fidda idanuwa,abinda bata sani ba duk abinda take almustaphan na ankare da ita,har ya kammala wayar bata sani ba,maidata aljihu yayi ya hade hannayensa waje guda yana nazarin yadda annuri ke fita daga fuskarta,take ya sake karantar yanayinta na tsantsar son yara,ta sake maida idanunta wajen wasu yara dake daura da su wajen su biyar da wata 'yar matashiya tsakiyarsu da alama ita ta kawosu,wasa sukeyi abinsu na buya,yarinyar dake cikinsu wadda bata wuce shekara uku ba ta taho a guje ba tare data lura da sumayyan ba ta boye bayan kujerar da take zaune tana fadi cikin harshen larabci
"Ki boyeni",murmushi ya qwacewa sumayyan sai ta sake bude doguwar rigarta ta boye yarinyar ga sake lafewa tana sakin dariya irinta quruciya,nemanta suka shiga yi wanda dariyar da take qyalqyalawa ya sanya suka gano inda taje,sai ta cukuikuye sumayya tana dariya tare da kifa kanta acinyarta,daukanta tayi itama tana murmushi sannan ta miqe sanda yaran suka qaraso ta ajjiye musu ita,sake diba sukayi da gudu ta koma ta zauna tana binsu da kallo tana murmushi.
A nutse suka ci gaba da takawa suna qarewa kyawun wajen da tsarinsa kallo,har yanzu murmushu bai bar fuskarta ba,zuciyarta fes,Allah ya sani tana son yara
"Allah ka bani yara da yawa"ta furta can qasa sosai lebanta na motsawa
"Da wa?" Zuciyarta ta tambayeta,,matuqar yaran takeso saidai tare da mustapha fa kenan,a hankali ta daga kai ta dubi mustapha,sai suka hada idanuwa,tare kowa ya dauke kanshi,kaifin ji gareshi kamar me,yaji sanda tayi addu'ar,shirun minti wajen biyar tsakani taji ya jeho mata tambayar da bata san amsarta ba
"Haihuwa kike so kenan?" Sosai tambayar ta doketa,ya akayi tayi maganar yadda zaya ji,sai ya tsaya cak da tafiyar ya kafeta da idanu ta cikin gilashinsa,bata ce komai ba sai dauke kanta da tayi
"Uhummm,ki amsa mana,kina so ki samu ciki ne ki haihu?" Gani take kamar ma wani nishadi yake yana son qureta,hakan ya sanya ta cire kunya ba tare data dubeshi ba tace
"Kuskure ne?,kai din baka so?,shekarunka nawa a duniya?,ina tsammanin zuwa yanzu zaka yi kwadayin samun diyan kanka" shi din ma ba qaramin dukanshi furucin yayi ba,amma ya sai ya tsinci kansa qaramin murmushi na subuce masa,ya lura qarfin hali tayi ta furta maganar,yana son mutum mai confidence qwarai,zaya so kacici kacicin nasu ya dore saboda haka yace
"Why zan qi hakan,ina so,but bani da matar da zata haifa min.....ko ke zaki iya?" Waiwayowa tayi da hanzari ta dubeshi,sai ta sake kasa ci gaba da jurewa kallon nasa,ta kuma juya baya tana harde da hannayenta a qirji,yayin da,nashi hannayen ke zube a aljihu yana dubanta,yana son qure confidence din da take ji tana da shi,kai ta girgiza bayan ta samo amsar bashi
"A'ah ni a su wa,ban shirya ba,after all ma bazan iya ba" ta fada tana watsa hannuwanta,dariyarshi ya danne don ya hango karaya muraran a kalamanta
"Me zaya hana ne wai?,ai sai an gwada aka san na qwarau,if u can try u can do it" ya fada yana kama qugunta da hannayenshi tare da mannata a jikinsa,har ga Allah yayi da wasa don kuma ya qureta,saidai yaji a jikinsa fiye da yadda ita taji,don ita tsoro ne ya lullubeta,dakiya da taurin zuciya ya hanashi sakinta,sai da yace
"Tunda kika fada dole ki gwada,sai an banbance aya da tsakuwa tukunna" sannan ya saketa,da hanzari tayi baya tana jingina da jikin wasu qarafuna dake tsaye wanda aka yiwa ado saboda yadda qafafunta sukayi sanyi,tsahon mintina qirjinta na bugawa ta rasa ta cewa,batasan sanda ya sayi ice cream din ba ta dai ga yana miqo mata,a sanyaye ta saka hannu ta amsa.
Basu bar wajen ba sai wajen takwas na dare,duj wata kewa da takura na tsahon satittikan sun baje sunyi nasu guri a park din,don ma baki daya ta kasa ci gaba da sakewa tun maganar da sukayi da shi,kunya nauyi da tsoro sun cikata duk da bai sake dubanta ba bare yace mata wani abu,har suka koma gida yayi wanka yayi shirin bacci tana takure guri daya,tuni yayi luf saman gado,ta qididdige lokutan data saba bashi ja zatonta cewa yayi bacci sannan ta miqe ta shiga toilet tayi wanka ta sauya kayan baccinta,kusan tuni ya haddace sanda take sauya kayan,hakan ya sanya ma yau bacci bai daukeshi ba,tamkar mai jira yaga fitowarta din kuwa sai gata ta fito,a gajiye take don haka a sannu take takawa cikin kayan baccin riga da wando ne,rigar iya cinya wando kuma ya wuce gwiwarta iya qauri,idanunsa ya lumshe yana ajiyar numfashi kadan kadan,kansa ya wani sara mishi,sunan Allah ya ambata tare da addu'ar kada ya zamana ciwon kansa ke shirin tashi,yau yayi surutu ta waya da yawa,ga inda suka je din akwai hayaniya ba laifi,bugu da qari jiya bai samu isashshen bacci ba saboda wannan matsalar,a haka ciwon kan ya dinga sakadarshi har kuaa da asuba kafin ya samu bacci.
****** ****** *******
A hankali suke takawa suna wucewa zuwa gurin ajiyar motoci,abun mamaki duk inda suka gifta tun daga cikin hotel din sai sun dauki hankali,tsammata ake wasu shaqiqan masoya ne,yanayin shigar kowannensu ya dace da shi,a haka har suka qarasa wajen motar,da kanshi yau zaiyi driving din saboda haka kai tsaye ya wuce mazaunin driver.
Wani nutststsen tuqi yake yi wanda ke qarawa zuciya da ruhi nutsuwa,bazaiyi qarya ba kam yau wani annushuwa yake ji,hakan kuma yaba tunanin bai rasa nasaba da warwarewar matsalarsa cikin sauqi,shiru kake jin motar,idanunta na bisa titi a fakaice tana qarewa garin kallo,haqiqa yayi matuqar tafiya da ita fiye da uk da ta je,gari ne mai cike da qyale qyale da kayan qawa masu matuqar jan hankali,dan satar kallonta yayin kafin ya maida kanshi bisa titi
"Thanks" taji ya ambata,a hankali ta maida idanunta kanshi wanda titi yake kalla kafin ya dauke kanta,murya qasa tace
"Dame fa?" Shiru ya biyo baya kamar bazai amsa ba,har tayi zaton ma ya bar zancan sai taji ya kuma cewa
"Shukhran alat taujih" sake daga kanta tayi tana dubanshi murmushi na son subuce mata,ta rasa ya akayi yaji larabci haka,wati dazun tayi shuka ne idon makwarwa,ta gode Allah da ba wata magana ta fadi ba,sai ta kauda kanta
"Babu komai,abinda ya kamata ne nayi shi" sosai maganar ta burgeshi,kusan shi daya yake warware matsalolinshi idan sun taso mashi ya riga ya saba,shi yasa wannan karon yake jin tayi mishi wani gagarumin aiki data cancanci a gode mata,ba shakka samun abokin shawara da yin shawara a kuma baka shawarar yana da matuqar muhimmanci kamar yadda ummee ta saba gaya masa
"Ko zaiyiwu na riqeki personal adviser?"
"Aikin kowacce macen gida ce matuqar an lamunce mata hakan" itama ta fada ba tare data dubeshi ba,tana jin qarin mamakinsa cikin ranta,kamar yasha wani abu ne?,wannan ne karon farko tsawon sanayyarta da shi da suka taba zance mai tsahi makamancin hakan,ta nashi bangaren mamakin irin tata baiwa da fasahar yake,yana ganin matan arewa basu da wannan fikirar amma a yanzu yaga guda daya?,haka suke ko kuwa wannan ce kawai?(hmmm,mun wuce haka ma malam almustapha,muje dai zuwa).
Bai tsaya ko ina ba sai zabeel park,tunda suka shiga wajen yayi matuqar qayatar da ita,karon farko a rayuwarra data taba shiga wani park,guri ne da family kan iya zuwa,miji da mata da yaransu,koma miji da mata kawai,a hankali suke takawa jere da juna,saidai idanuwanta na wulqawa ko ina tana kalle kalle abinta cikin hikima ba tare daka fuskanci ta matowa gurin ba,wani sashe daban suka nufa wanda ke dauke da wasu rubuce rubuce na SEASON four dubai garden glow,hakan ke nuna lokaci lokaci wajen ke a bude,gurin biyan kudin shiga ya biya aka nasu ticket sannan suka shige.
Bata taba ganin abubuwan data gani cikin garden din ba,wani irin garden ne da aka baje fasaha wajen yinsa,kowa na harkarshi cikin wajen,kama da yara qananu da matsakaita,maza da mata,masoya gasunan birjik kowa na baje kolin tashi soyayyar,wani guri na musamman suka yi mazauni sanda wayarshi ta fara ruri ya cirota yana qoqarin amsawa yayin da ita kuma taci gaba da bawa idanunta abinci,a hankali idanuwanta suka sauka kan wani family,miji da mata ke sai yaransu uku,mace babba sai mai bi mata namiji sai qaramin shima namiji,a yadda suke raha kana kallonsu kasan banu abinda ya shafi rayuwarsu,sisai yaron suka burgeta kasancewarta mutum mai son yara qwarai,suna ta wasanninsu suna kaiwa suna kawowa wajen iyayensu,ta sake dauke idanunta ta maida kan wasu matasa biyu mace da namiji,namijin ke bawa macen ice cream yana ta faman lallabata ya kasa ya tsare,tayasu dariya tayi ta hanyar sakin murmushi sanda ya dangwala kata shi kan hancinta sanyinsa ya ratsata ta fidda idanuwa,abinda bata sani ba duk abinda take almustaphan na ankare da ita,har ya kammala wayar bata sani ba,maidata aljihu yayi ya hade hannayensa waje guda yana nazarin yadda annuri ke fita daga fuskarta,take ya sake karantar yanayinta na tsantsar son yara,ta sake maida idanunta wajen wasu yara dake daura da su wajen su biyar da wata 'yar matashiya tsakiyarsu da alama ita ta kawosu,wasa sukeyi abinsu na buya,yarinyar dake cikinsu wadda bata wuce shekara uku ba ta taho a guje ba tare data lura da sumayyan ba ta boye bayan kujerar da take zaune tana fadi cikin harshen larabci
"Ki boyeni",murmushi ya qwacewa sumayyan sai ta sake bude doguwar rigarta ta boye yarinyar ga sake lafewa tana sakin dariya irinta quruciya,nemanta suka shiga yi wanda dariyar da take qyalqyalawa ya sanya suka gano inda taje,sai ta cukuikuye sumayya tana dariya tare da kifa kanta acinyarta,daukanta tayi itama tana murmushi sannan ta miqe sanda yaran suka qaraso ta ajjiye musu ita,sake diba sukayi da gudu ta koma ta zauna tana binsu da kallo tana murmushi.
A nutse suka ci gaba da takawa suna qarewa kyawun wajen da tsarinsa kallo,har yanzu murmushu bai bar fuskarta ba,zuciyarta fes,Allah ya sani tana son yara
"Allah ka bani yara da yawa"ta furta can qasa sosai lebanta na motsawa
"Da wa?" Zuciyarta ta tambayeta,,matuqar yaran takeso saidai tare da mustapha fa kenan,a hankali ta daga kai ta dubi mustapha,sai suka hada idanuwa,tare kowa ya dauke kanshi,kaifin ji gareshi kamar me,yaji sanda tayi addu'ar,shirun minti wajen biyar tsakani taji ya jeho mata tambayar da bata san amsarta ba
"Haihuwa kike so kenan?" Sosai tambayar ta doketa,ya akayi tayi maganar yadda zaya ji,sai ya tsaya cak da tafiyar ya kafeta da idanu ta cikin gilashinsa,bata ce komai ba sai dauke kanta da tayi
"Uhummm,ki amsa mana,kina so ki samu ciki ne ki haihu?" Gani take kamar ma wani nishadi yake yana son qureta,hakan ya sanya ta cire kunya ba tare data dubeshi ba tace
"Kuskure ne?,kai din baka so?,shekarunka nawa a duniya?,ina tsammanin zuwa yanzu zaka yi kwadayin samun diyan kanka" shi din ma ba qaramin dukanshi furucin yayi ba,amma ya sai ya tsinci kansa qaramin murmushi na subuce masa,ya lura qarfin hali tayi ta furta maganar,yana son mutum mai confidence qwarai,zaya so kacici kacicin nasu ya dore saboda haka yace
"Why zan qi hakan,ina so,but bani da matar da zata haifa min.....ko ke zaki iya?" Waiwayowa tayi da hanzari ta dubeshi,sai ta sake kasa ci gaba da jurewa kallon nasa,ta kuma juya baya tana harde da hannayenta a qirji,yayin da,nashi hannayen ke zube a aljihu yana dubanta,yana son qure confidence din da take ji tana da shi,kai ta girgiza bayan ta samo amsar bashi
"A'ah ni a su wa,ban shirya ba,after all ma bazan iya ba" ta fada tana watsa hannuwanta,dariyarshi ya danne don ya hango karaya muraran a kalamanta
"Me zaya hana ne wai?,ai sai an gwada aka san na qwarau,if u can try u can do it" ya fada yana kama qugunta da hannayenshi tare da mannata a jikinsa,har ga Allah yayi da wasa don kuma ya qureta,saidai yaji a jikinsa fiye da yadda ita taji,don ita tsoro ne ya lullubeta,dakiya da taurin zuciya ya hanashi sakinta,sai da yace
"Tunda kika fada dole ki gwada,sai an banbance aya da tsakuwa tukunna" sannan ya saketa,da hanzari tayi baya tana jingina da jikin wasu qarafuna dake tsaye wanda aka yiwa ado saboda yadda qafafunta sukayi sanyi,tsahon mintina qirjinta na bugawa ta rasa ta cewa,batasan sanda ya sayi ice cream din ba ta dai ga yana miqo mata,a sanyaye ta saka hannu ta amsa.
Basu bar wajen ba sai wajen takwas na dare,duj wata kewa da takura na tsahon satittikan sun baje sunyi nasu guri a park din,don ma baki daya ta kasa ci gaba da sakewa tun maganar da sukayi da shi,kunya nauyi da tsoro sun cikata duk da bai sake dubanta ba bare yace mata wani abu,har suka koma gida yayi wanka yayi shirin bacci tana takure guri daya,tuni yayi luf saman gado,ta qididdige lokutan data saba bashi ja zatonta cewa yayi bacci sannan ta miqe ta shiga toilet tayi wanka ta sauya kayan baccinta,kusan tuni ya haddace sanda take sauya kayan,hakan ya sanya ma yau bacci bai daukeshi ba,tamkar mai jira yaga fitowarta din kuwa sai gata ta fito,a gajiye take don haka a sannu take takawa cikin kayan baccin riga da wando ne,rigar iya cinya wando kuma ya wuce gwiwarta iya qauri,idanunsa ya lumshe yana ajiyar numfashi kadan kadan,kansa ya wani sara mishi,sunan Allah ya ambata tare da addu'ar kada ya zamana ciwon kansa ke shirin tashi,yau yayi surutu ta waya da yawa,ga inda suka je din akwai hayaniya ba laifi,bugu da qari jiya bai samu isashshen bacci ba saboda wannan matsalar,a haka ciwon kan ya dinga sakadarshi har kuaa da asuba kafin ya samu bacci.
****** ****** *******