Sashe 44
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yau sai kusan biyar suka taso,tun daga qofar gidan ta hangi motarsa,a hankali ta dinga takawa jikinta a sanyaye har ta isa gab da motar,qofar mazaunin direba a bude take alamun mamallakin motar yana ciki,tuni abdallah ya gane motar waye,ya zame daga jikinta yayi wajen motar yana kiran abba,hankalin abdur rahman yayo wajen ya waiwayo yana murmushi sannan ya fito ya dage shi sama ya cafe suna dariya,sanye yake da yadi irin na maza blue black,hula da takalminsa sau ciki duka baqi,yayi kyau sosai. Ya sauke idanunshi a kanta yana kallonta
"Yau kam kin dade,kinsan tun nawa nake nan ina jiranki?" Kai ta girgiza ba tare da tace komai ba,yatsun hannunsa ya daga guda hudu ya nuna mata,sannan ya dora da fadin
"Shine yau kika dauke abokin hirar ko?" Kai ta sake kadawa sannan tace
"Shine ya nace yau sai ya biji,nima bana son tafiya da shi"
"Mukam muna maraba da shi ko yaushe,shiga ki kintsa kafin naje can qasan layinku na dawo na baki minti talatin"
"Amma dai da ka shigo ciki ko?"
"Amma dai kinsan gunki nazo ko?"ya bata amsa da salon yadda tayi tata maganar,ta lura jan magana yake ji saboda haka ta sanya kanta gida tana fadin
"A dawo lafiya".
Salla kawai tayi wadda lokacinta ya kubce mata,ko abincin ta kasa ci tanaa zaune tana nazarin hanyar da zata bi abdur rahman ya janye zancansa salin alin ba tare da an kai ruwa rana ba,don gaskiya bata jin zata iya maida kanta cikin familyn su mukhtar,an gudu ba'a tsira ba kenan,ko kuma tsugune bata qare ba?,cikin haka zainab ta shigo dakin ta gaya mata taje ya abdur rahman na waje ta karbi abdallah.
Kamar wancan karon wannan ma haka ya tilasta mata shiga motar tasa,shuru ya ratsa motar na wasu daqiqu ba wanda ya sake cewa uffan bayan abdur rahman ya gama jaddada bayanansa a gareta
"Da farko abinda zan fara cewa shine na gode na gode matuqa,na yaba da qaunata da kace kana yi,har ka nuna sha'awar zamantowa abokiyar rayuwarka duk da ban cancanci wannan darajar ba,amma abdur rahman kayi haquri,bazan iya aurenka ba,saboda wasu dalilai wadanda ni da kai duka mun sansu wasunsu kuma ni da ubangiji na ne kawai muka sansu" kai yake jinjinawa yana dubanta sannan yace
"Ban gamsu da baya nanki ba ko kadan,babu wani abu da zai sanya ni janyewa daga batun neman aurenki sumayya,ina sonki babu wanda zai hanani"so take ya fahinceta bilhaqqi don su bar maganar sun wuce gun,sai ta sake fuskantar sosai wani abu na taba zuciyarta na daga abubuwa da suka faru da ita a baya
" ta yaya abdur rahman kake so na sake komawa cikin danginku,bayan kaima kana daya daga cikin mutanan da zasu shaidi irin rayuwar da nayi a cikinsu,ya kake so ka sake maidani rayuwar baqincikin da nayi bankwana da ita?,ko kuwa zaka sauya dangi ne saboda zaka aureni ni sumayya 'yar gwal,ko ka manta waje mijina na baya,ka manta alaqar da take tsakanin ku,don Allah abdur rahman muci gaba da mutunci mu ajjiye zancan soyayya a gefe"ta qarashe maganar tsohon mikin dake zuciyarta na taso mata,sai ta sanyo qafafunta waje ta fito daga motar,da sauri shima ya fito ya zagayo inda take tsayen,kafin yace mata komai suka ji tsaiwar mota,waiwayawa sukayi dukkansu don ganin waye.
Mukhtar ne,tun yana cikin motar tasa yake qarewa motar kallo,babu shakka wannan motar yake tawan gani a qofar gidan su sumayyan,kenan yau zai ga waye mamallakinta zaiga wake zuwa gunta,amma idan idanuwansa na nuna masa dai dai kamar abdur rahman yake gani tsaye tare da sumayya,to meye yake haka a gidan?,meyw hadinsu?,shine mai motar da yake gani kullum na ficewa daga layin?,don samun amsaoshin tambayoyinsa sai ya balle murfin ya fito bayan ya kashe motar ya nufosu idanuwansa a kansu zuciyarsa na azalzala tare da ayyana masa wani abu wanda baya fatan kasancewaraa.
Sallamarsa ita ta katse abdur rahman daga kallon sumayya da tuni idanunta suka cika da qwalla,sannan suka katse shi dag fadar abinda yake shirin fada,dukkansu waiwaya suka yi suka dubeshi,fuskar abdur rahman din dauke da murmushi ya miqawa mukhtar hannu yana fadin
"Ah,ya mukhtar kai ne?" Baiqi miqa masa nasa hannun ba suka yi musabaha yana fadi tare da tsareshi da wani irin kallo
"Eh,ya kawu da sauren mutanen gidan"
"Duka lafiya alhamdulillahi" ya fada yana sakin hannun mukhtar din sannan ya juya ga sumayya
"Ki nazari a nutse,kada ki ruda kanki,kada ki cuci kanki ki cuceni,gobe in sha Allah zan dawo" ya fada yana juyawa zuwa wajen motarsa,dukkansu ita da mukhtar din suka yi masa rakiyar idanuwa,saidai kowa da abinda ke kai kawo cikin zuciyarsa,ya bude motar ya shiga bayan ya bawa abdallah 'yar madaidaiciyar baqar leda cike da biscuite da choculet ya saukeshi ya tada motar ya wuce.
Busy kuyi haquri da wannan
*mrs muhammad ce*
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
4⃣0⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*innal laha la yugayyiru maa bi qaumin hatta yugayyiru ma bi'an fusihim*
_haqiqa Allah baya canzawa mutane(halin ko yanayin da suke ciki)har sai sun canza da kansu_
______________________________
Ungawa ce mai matuqar kyau da tsari,akwai nauikan mutane daban daban cikinta,saidai akasarin mzauna cikinta din masu hannu da shuni ne da kuma masu rufin asiri ko wadanda suke ma'aikatan gwamnatin tarayya ta basu gida su zauna kamar su anty dije.
Sai da mansur ya fidda kayanta baki daya ya shigar mata cikin gidan ta masa godiya sosai sannan ya ja motarsa ya shige wani katafare kuma hamshaqin gida dake kallon nasu.
Dukka yaran gidan na nan kasancewar ranar qarshen mako ce,laila ita ce babba,sai hafiz mai bi mata,sannan khalifa sai nasir sai auta amina minal,a qalla laila zata yi shekaru goma sha hudu,ita ta fara ganin shigowar sumayya falon,ihu ta sanya wanda ya janyo hankalin 'yan uwanta ta nufi sumayya ta rungumeta,haka sauran suka baibayeta wanda ya janyo musu faduwa a qasa dukansu suna dariya,da qyar ta samu suka dagata suka koma saman kujera sannan ta soma tambayarsu anty dijen don bata ji motsinta ba,dining laila ta nuna wa sumayyan tana cewa
"Kinga yaya sumayya can duka abincinki ne,tun dazu mama ke jiranki baku iso ba har ta gaji ta shiga gidan daddy prof,amma bari naje na kirata" ta fada tana yafa dan yalolon mayafinta tayi waje da sauri,khalifa sumayya tasa ya fara nuna mata toilet ta shiga tayi alwala,tana kammala alwalar anty dije na shigowa
"Sai yanzu?,gaskiya kunyi nauyi a hanya kamar wadanda suka hau motar haya inji hajiya bilki" murmushi sumayya tayi tana duban anty dije wadda ta sake gogewa bisa dukkan alamu zaman garin ya karbeta matuqa,ta kuma zama 'yar gayu ita da yaranta baki daya
"Wallahi anty sai da muka biya kasuwa muka karbo wasu kaya sannan har mun dau hanya wani oga ko yallabai ya maida ku zoo road karbo dinki"
"Eh inaga man ne dinkunan su'ad ce,maza yi sallar kizo kici abinci kafin mu zauna hirar yashe gamo" ta fada tana sanya su laila dauke akwatunta zuwa wani daki da aka tanada saboda baqi irinta.
Sai da taci ta qoshi sannan suka baje a falon ana hiran yaushe gamo,kusan haka suka qarar da wunin ranar,ko da malamar lesson din yaran ma tazo guduwa sukayi suka qi zuwa sai tafiya tayi,da dare ma yayi da qyar suka tafi dakinsu don cewa sukayi tare da sumayyan zasu kwana,saida anty dije ta korasu saboda tana son suyi zance,sosai suka sake kuwa don mai gidan ta baya nan sun tafi semina lagos,sosai anty dije ta sake kwantar mata da hankali tare da bata shawarwari ta rufe da fadi cikin sigar tsokana
"Duk da nasan sumayyan tawa zuwa yanzu ta fara girma,hankali ya fara zuwa mata" itama dariya tayi,sai wajen sha daya da rabi sannan ta fita ta barta,to nan din ma lukman bai barta ba da hira sai data ce tana jin bacci sannan yace
"Ki kula min da kanki to na baki amanar kanki my dear kinji"ajiyar zuciya ta saki sannan ta amsa masa ta katse kiran,taso kiran halina taji ya abdallah yake,amma ganin dare yayi nisa ya sanyata ta haqura ta barwa gobe,duk sai taji tana kewar yaron nata.
****** ****** ******
Kwanakin da tayi a garin kwanaki ke da suka yi mata dadi sosai,kullum yaran na nanuqe da ita suna hira,sauqin abun sun gama jarabawa hutu kawai suke jira,wani lokaci da yammaci anty dije kan debe su da motar mai gidan da ya barta a gida ta kaisu park su dan sha iska suyi ciye ciye su dawo,hakan na yiwa sumayya dadi,lallai ko yaya ka motsa daga wani gu zuwa wani gu zaka samu sauyi zuciyarka zata yi dadi.
Duk wani abu da ya kamata a yiwa amarya anty dije da kanta ta yiwa sumayya,cikin kwana goma ta hadata tsaf.
Ana ya gobe zasu koma kanon laila na kwance kan cinyar sumayya sumayyan na tsefe mata kitsonta zasu wankin gashi da yamma anty dije ta fito ta dubesu
"zan dan shiga gidan daddy prof zamuyi sallama da su,Allah baiyi da ni za'a yi sunan nan ba"sumayya ta daga kai ta dubi anty dije
" au haihuwa akayi halan?"
"Sai yau zaki tambaya kenan,kwana na nawa ina leqa su amma baki taba karar ki shiga ku gaisa da mutanen ba,direban gidan ya dauko ki daga kano fa,surukar gidan ce ta haihu" murmushi sumayya tayi
"To ai ban sansu bane anty"
"Ni ai na sansu kuma gashi na gaya miki,mutanen akwai tsabar mutunci da karrama mutum,duk yadda Allah ya musu tsabar arziqi amma basu raina na qasansu,mai gidan bakiga yadda ya dauki abban khalifa ba kamar dan cikinsa,su khalifa kuwa ya maidasu tamkar jikokinsa" jinjina kai sumayya keyi sannan tace
"Allah ya saka musu da alkhairi,kice ina musu barka"
"Zasuji tunda ba zaki din ba" inji anty dije ta fice tana mita sumayya ta bita da dariya.
"Yau kam kin dade,kinsan tun nawa nake nan ina jiranki?" Kai ta girgiza ba tare da tace komai ba,yatsun hannunsa ya daga guda hudu ya nuna mata,sannan ya dora da fadin
"Shine yau kika dauke abokin hirar ko?" Kai ta sake kadawa sannan tace
"Shine ya nace yau sai ya biji,nima bana son tafiya da shi"
"Mukam muna maraba da shi ko yaushe,shiga ki kintsa kafin naje can qasan layinku na dawo na baki minti talatin"
"Amma dai da ka shigo ciki ko?"
"Amma dai kinsan gunki nazo ko?"ya bata amsa da salon yadda tayi tata maganar,ta lura jan magana yake ji saboda haka ta sanya kanta gida tana fadin
"A dawo lafiya".
Salla kawai tayi wadda lokacinta ya kubce mata,ko abincin ta kasa ci tanaa zaune tana nazarin hanyar da zata bi abdur rahman ya janye zancansa salin alin ba tare da an kai ruwa rana ba,don gaskiya bata jin zata iya maida kanta cikin familyn su mukhtar,an gudu ba'a tsira ba kenan,ko kuma tsugune bata qare ba?,cikin haka zainab ta shigo dakin ta gaya mata taje ya abdur rahman na waje ta karbi abdallah.
Kamar wancan karon wannan ma haka ya tilasta mata shiga motar tasa,shuru ya ratsa motar na wasu daqiqu ba wanda ya sake cewa uffan bayan abdur rahman ya gama jaddada bayanansa a gareta
"Da farko abinda zan fara cewa shine na gode na gode matuqa,na yaba da qaunata da kace kana yi,har ka nuna sha'awar zamantowa abokiyar rayuwarka duk da ban cancanci wannan darajar ba,amma abdur rahman kayi haquri,bazan iya aurenka ba,saboda wasu dalilai wadanda ni da kai duka mun sansu wasunsu kuma ni da ubangiji na ne kawai muka sansu" kai yake jinjinawa yana dubanta sannan yace
"Ban gamsu da baya nanki ba ko kadan,babu wani abu da zai sanya ni janyewa daga batun neman aurenki sumayya,ina sonki babu wanda zai hanani"so take ya fahinceta bilhaqqi don su bar maganar sun wuce gun,sai ta sake fuskantar sosai wani abu na taba zuciyarta na daga abubuwa da suka faru da ita a baya
" ta yaya abdur rahman kake so na sake komawa cikin danginku,bayan kaima kana daya daga cikin mutanan da zasu shaidi irin rayuwar da nayi a cikinsu,ya kake so ka sake maidani rayuwar baqincikin da nayi bankwana da ita?,ko kuwa zaka sauya dangi ne saboda zaka aureni ni sumayya 'yar gwal,ko ka manta waje mijina na baya,ka manta alaqar da take tsakanin ku,don Allah abdur rahman muci gaba da mutunci mu ajjiye zancan soyayya a gefe"ta qarashe maganar tsohon mikin dake zuciyarta na taso mata,sai ta sanyo qafafunta waje ta fito daga motar,da sauri shima ya fito ya zagayo inda take tsayen,kafin yace mata komai suka ji tsaiwar mota,waiwayawa sukayi dukkansu don ganin waye.
Mukhtar ne,tun yana cikin motar tasa yake qarewa motar kallo,babu shakka wannan motar yake tawan gani a qofar gidan su sumayyan,kenan yau zai ga waye mamallakinta zaiga wake zuwa gunta,amma idan idanuwansa na nuna masa dai dai kamar abdur rahman yake gani tsaye tare da sumayya,to meye yake haka a gidan?,meyw hadinsu?,shine mai motar da yake gani kullum na ficewa daga layin?,don samun amsaoshin tambayoyinsa sai ya balle murfin ya fito bayan ya kashe motar ya nufosu idanuwansa a kansu zuciyarsa na azalzala tare da ayyana masa wani abu wanda baya fatan kasancewaraa.
Sallamarsa ita ta katse abdur rahman daga kallon sumayya da tuni idanunta suka cika da qwalla,sannan suka katse shi dag fadar abinda yake shirin fada,dukkansu waiwaya suka yi suka dubeshi,fuskar abdur rahman din dauke da murmushi ya miqawa mukhtar hannu yana fadin
"Ah,ya mukhtar kai ne?" Baiqi miqa masa nasa hannun ba suka yi musabaha yana fadi tare da tsareshi da wani irin kallo
"Eh,ya kawu da sauren mutanen gidan"
"Duka lafiya alhamdulillahi" ya fada yana sakin hannun mukhtar din sannan ya juya ga sumayya
"Ki nazari a nutse,kada ki ruda kanki,kada ki cuci kanki ki cuceni,gobe in sha Allah zan dawo" ya fada yana juyawa zuwa wajen motarsa,dukkansu ita da mukhtar din suka yi masa rakiyar idanuwa,saidai kowa da abinda ke kai kawo cikin zuciyarsa,ya bude motar ya shiga bayan ya bawa abdallah 'yar madaidaiciyar baqar leda cike da biscuite da choculet ya saukeshi ya tada motar ya wuce.
Busy kuyi haquri da wannan
*mrs muhammad ce*
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
4⃣0⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*innal laha la yugayyiru maa bi qaumin hatta yugayyiru ma bi'an fusihim*
_haqiqa Allah baya canzawa mutane(halin ko yanayin da suke ciki)har sai sun canza da kansu_
______________________________
Ungawa ce mai matuqar kyau da tsari,akwai nauikan mutane daban daban cikinta,saidai akasarin mzauna cikinta din masu hannu da shuni ne da kuma masu rufin asiri ko wadanda suke ma'aikatan gwamnatin tarayya ta basu gida su zauna kamar su anty dije.
Sai da mansur ya fidda kayanta baki daya ya shigar mata cikin gidan ta masa godiya sosai sannan ya ja motarsa ya shige wani katafare kuma hamshaqin gida dake kallon nasu.
Dukka yaran gidan na nan kasancewar ranar qarshen mako ce,laila ita ce babba,sai hafiz mai bi mata,sannan khalifa sai nasir sai auta amina minal,a qalla laila zata yi shekaru goma sha hudu,ita ta fara ganin shigowar sumayya falon,ihu ta sanya wanda ya janyo hankalin 'yan uwanta ta nufi sumayya ta rungumeta,haka sauran suka baibayeta wanda ya janyo musu faduwa a qasa dukansu suna dariya,da qyar ta samu suka dagata suka koma saman kujera sannan ta soma tambayarsu anty dijen don bata ji motsinta ba,dining laila ta nuna wa sumayyan tana cewa
"Kinga yaya sumayya can duka abincinki ne,tun dazu mama ke jiranki baku iso ba har ta gaji ta shiga gidan daddy prof,amma bari naje na kirata" ta fada tana yafa dan yalolon mayafinta tayi waje da sauri,khalifa sumayya tasa ya fara nuna mata toilet ta shiga tayi alwala,tana kammala alwalar anty dije na shigowa
"Sai yanzu?,gaskiya kunyi nauyi a hanya kamar wadanda suka hau motar haya inji hajiya bilki" murmushi sumayya tayi tana duban anty dije wadda ta sake gogewa bisa dukkan alamu zaman garin ya karbeta matuqa,ta kuma zama 'yar gayu ita da yaranta baki daya
"Wallahi anty sai da muka biya kasuwa muka karbo wasu kaya sannan har mun dau hanya wani oga ko yallabai ya maida ku zoo road karbo dinki"
"Eh inaga man ne dinkunan su'ad ce,maza yi sallar kizo kici abinci kafin mu zauna hirar yashe gamo" ta fada tana sanya su laila dauke akwatunta zuwa wani daki da aka tanada saboda baqi irinta.
Sai da taci ta qoshi sannan suka baje a falon ana hiran yaushe gamo,kusan haka suka qarar da wunin ranar,ko da malamar lesson din yaran ma tazo guduwa sukayi suka qi zuwa sai tafiya tayi,da dare ma yayi da qyar suka tafi dakinsu don cewa sukayi tare da sumayyan zasu kwana,saida anty dije ta korasu saboda tana son suyi zance,sosai suka sake kuwa don mai gidan ta baya nan sun tafi semina lagos,sosai anty dije ta sake kwantar mata da hankali tare da bata shawarwari ta rufe da fadi cikin sigar tsokana
"Duk da nasan sumayyan tawa zuwa yanzu ta fara girma,hankali ya fara zuwa mata" itama dariya tayi,sai wajen sha daya da rabi sannan ta fita ta barta,to nan din ma lukman bai barta ba da hira sai data ce tana jin bacci sannan yace
"Ki kula min da kanki to na baki amanar kanki my dear kinji"ajiyar zuciya ta saki sannan ta amsa masa ta katse kiran,taso kiran halina taji ya abdallah yake,amma ganin dare yayi nisa ya sanyata ta haqura ta barwa gobe,duk sai taji tana kewar yaron nata.
****** ****** ******
Kwanakin da tayi a garin kwanaki ke da suka yi mata dadi sosai,kullum yaran na nanuqe da ita suna hira,sauqin abun sun gama jarabawa hutu kawai suke jira,wani lokaci da yammaci anty dije kan debe su da motar mai gidan da ya barta a gida ta kaisu park su dan sha iska suyi ciye ciye su dawo,hakan na yiwa sumayya dadi,lallai ko yaya ka motsa daga wani gu zuwa wani gu zaka samu sauyi zuciyarka zata yi dadi.
Duk wani abu da ya kamata a yiwa amarya anty dije da kanta ta yiwa sumayya,cikin kwana goma ta hadata tsaf.
Ana ya gobe zasu koma kanon laila na kwance kan cinyar sumayya sumayyan na tsefe mata kitsonta zasu wankin gashi da yamma anty dije ta fito ta dubesu
"zan dan shiga gidan daddy prof zamuyi sallama da su,Allah baiyi da ni za'a yi sunan nan ba"sumayya ta daga kai ta dubi anty dije
" au haihuwa akayi halan?"
"Sai yau zaki tambaya kenan,kwana na nawa ina leqa su amma baki taba karar ki shiga ku gaisa da mutanen ba,direban gidan ya dauko ki daga kano fa,surukar gidan ce ta haihu" murmushi sumayya tayi
"To ai ban sansu bane anty"
"Ni ai na sansu kuma gashi na gaya miki,mutanen akwai tsabar mutunci da karrama mutum,duk yadda Allah ya musu tsabar arziqi amma basu raina na qasansu,mai gidan bakiga yadda ya dauki abban khalifa ba kamar dan cikinsa,su khalifa kuwa ya maidasu tamkar jikokinsa" jinjina kai sumayya keyi sannan tace
"Allah ya saka musu da alkhairi,kice ina musu barka"
"Zasuji tunda ba zaki din ba" inji anty dije ta fice tana mita sumayya ta bita da dariya.