Sashe 34
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Anty dije taji dadin ganinta sosai,nan suka wuni suna hira,ta tayata hada ragowar kayayyakin da bata kammala hada kansu ba,tuni yaranta sunyi gaba don su qarasa kammale gidan kafin isowar maman tasu. Suna hada kayan tana mata nasiha mai ratsa jiki,idanun sumayyan ya hada qwalla har ta kai ga gangarowa,ta share qwallar tana fadin
"Yanzu shikenan anty?,gurin wa zan dinga zuwa" sosai ta bata tausayi,yarinyar da dududu bata wuce shekara sha tara ba amma ta hadu da kaidin kishiyoyi kala kala,sai ta saki abinda take ta koma gefanta ta zauna
"Kina da Allah sumayya,baya ga haka akwai waya hannunki,duk abinda ya shige miki duhu ki kirani ki tambayeni,koda babu kudi a ciki kimin plashing zan kiraki da yardar Allah,ki ninka haqurinki kawai,domin duk wata mace da kika ga ta zama wata gidan mijinta ki tambayeta wanne irin haquri ta hadiya kafin ta kai ga cimma wannan matakin"
"To anty na gode"
"Babu godiya,ke diyata ce kamar su yasmin kike a gurina.....amma sumayya yanayin jikinki kamar ya sauya?,ko baki kula ba?" Ta fada tana kallonta
"Me kika gani anty?"
"Bakya jin wani sauyi a jikinki?"
"Babu abinda nake ji" ta fada tana kallon anty,shiru ta danyi sannan tace
"Shikenan.....koyaya kika ji wani abu kada ki zauna,kije asibiti"duk da bata fahimci abinda take nufi ba amma ta amsa mata da to.
Ana gab da sallar magariba ta koma gida,a gajiye ta koma,bandaki kawai ta fara shiga tayi wanka ya daura alwala,sai da ta kammala sallahr magariban sannan ta fita,cikin kitchen taji motsinta sai ta tura qofar ta shiga,tana tsaye tana hada food flask na abincin mukhtar,qarasawa tayi kusa da ita ta mata sallama,kai kawai ta daga ta dubeta ta maida kai taci gaba da abinda take ba tare data amsa ba,ita din ma bata damu data amsa ba kai tsaye ta jeho mata tambayar da ta fito da ita
"ina abincina zainab,banga flask dina ba"
Dagowa tayi sosai ta sake kallonta,sai ta saka wata dariya data sanya dole sumayyan ta tsaya tana kallonta cike da alamar tambaya,sai da ta tsagaita don kanta sannan tace
"Ince ko baki samu labarin baki da abinci a gidan nan ba" jin maganar tayi banbarakwai,ba kuma ta fahimci inda ta sa gaba ba,saboda haka taci gaba da kallonta,dauke kai tayi daga bisani sai ta nufi dan qaramin store din dake kitchen din da niyyar fiddo da ko indomie ce ta tafasa,sai ta tarad da store din a garqame da kwado,waiwayowa tayi ta sake duban zainab din
"Naga alamun baki fahimta ba,amma bari nayi miki bayani dalla dalla,mukhtar ya soke baki abincinsa,walau ni na dafa ko ke kika dafa kin fahimta ai yanzu ko?" Sosai maganar ta daketa,sai ta kasa furta komai baya ga wani abu da ya tokare maqoshinta,bata fahimci me hakan ke nufi,tilas ta jira dawowarsa tunda shi ya ajiyeta ba zainab ba,wannan maganar ba tata bace. Wuce zainab din tayi ta nufi sashenta ta dauki tukunya ta tari ruwa ta dora kan gas tare da jefa lipton,tilas ta sanya wani abu a cikinta ba don haka ba abinda take ji cikin zuciyarta bata jin wani abu mai suna abinci zai iya wucewa ta maqogoronta.
Hannayenta ta harde saman qirjinta tana jiran ruwan ya tafasa,tamkar zata fadi haka take ji,ga yunwa ga bacin rai,tana kammalawa ta juye a cup ta nufi daki,bata ko bi ta kan qananun habaicin da zainab keta jefawa cikin waqe,don yanzu bata ita take ba ta kanta take. Tea ta hada da kayan shayinta wanda dama a dakin suke.
Ko rabi bata sha ba ta soma yunqurin dawo da shi,sai data amayar da shi tas sannan ta dawo ta zube qasan carfet din dakin cikinta naci gaba da juyawa,rasa abinda ke mata dadi tayi,fashewa tayi da kuka tana kiran sunan Allah.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
3⃣1⃣
________________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wa bashshiris sabirin,Allazi a iza asabathum musibatun qalu innalillahi wa inna ilaihi raji'un*
_ka yiwa(ya annabin Allah) masu haquri bushara,sune wadanda idan musiba ta samesu suke fadin daga Allah muke kuma gareshi zamu koma_
*Allah ka sanya mu cikin wadanda zaka yiwa kyakkyawan sakamako sanadiyyar fadan wannan kalma*
_________________________________
Zainab qanwarta ce akan gaba,sai mama da yaya abubakar halima na biye da shi,umma sadiya qanwar babansu na biye da su
"Yaya sannu yanzu muka ga ya mukhtar din ma ai ya fita" ta fada ba tare da sun ankara baki daya da yanayinda take ciki ba,haka ma basu lura da zainab dake tsaye gefe ba tana tsuma tare da kallon fitsarin da ya gama wanke mata qafafu. Kallo daya mamanta ta yi mata ta fuskanci ba dai dai taje ba duk da cewa akwai ciwo tattare da ita.
Da idanu kawai take binsu tana fata ta farka daga mummunan mafarkin da takeyi,sai da maman ta qarasa gefan gadon ta zauna ta soma yi mata sannu sannan sumayya ta tabbatarwa kanta idanuntq biyu,a zahiri komai ke faruwa,wata cukuikuya ta yiwa maman nata tana sauke wata ajiyar zuciya tare da fadin
"Ya sakeni mama,ya rabu da ni bayan bani da wani laifi",cikin rudani suke kallonta duk suna zaton zafin ciwo ne
"Sumayya zafin ciwo ne duka hakan?" Sai ta fashe da wani kuka mai azabar cin rai tana maimaita fadin
"Walllahi mama ya sakeni,yanzun nan da kuka ganshi ya fita sakina yayi mama" salati suka saka baki daya wanda ya dawo da zainab hayyacinta
"Allah ya isa 'yarku ta jawo min masifa,ta jawo min zawarci kashi na biyu garin qoqarin zubar da cikinta" ta fada tana wucewa fuuuu ta bar dakin.
Shiru ya ratsa dakin,babu wani abu dake tashi sai shashsheqar kukan sumayya wanda zainab da halima ke tayata saboda tsantsar tausayin 'yar uwarsy,yayin da zuciyoyin sauran ke quna,zancan zainab kuma ke musu kai kawo
"Mama har saki uku yaya mukhtar ya yimin,mama wallahi ban aikata ba,na fishi son naga na haihu mama ki......." Sai ta fara jan numfashi da qyar wanda hakan ya sanya su sake rudewa,da sauri yaya abubakar ya nufi reception don kiran nurse ko likita,cin qanqanin lokaci sai gashi tare da likita wanda yake gab da tashi Allah yasa bai fita ba,waje ya fid dasu baki daya sannan ya rufe dakin,take suka rude da koke koke cike da tashin hankali.
Kusan mintina talatin sannan likitan ya fito bayan ya gama dubata ya mata allurar bacci tare da sanya mata wani ruwan,ya sanar musu bata buqatar hayaniya,sannan don Allah su guji tada mata hankali idan baso suke ta hadu da hawan jini ba,don ko a yanzun jini nata ya fara sama,bugu da qari kuma ta zubda jini mai yawa,godiya suka yi masa sannan suka koma dakin kowa ya samu gu ya zauna zugum,dukkansu da abinda suke saqawa zukatansu,daga bisani yaya abubakar ya fice dan yi musu siyesiyen abubuwan da zasu buqata kafin suga yadda hali zaiyi.
Tun a hanya take sumbatu,ko da wasa bata taba zaton ramin da ta haqa zai rufta da ita ba,bata taba ganin masifa irin wannan ba,taga samu taga rashi,gidan da takewa kanta hasashen samun abun duniya yau dare daya an rabata da shi
"Ina!!!,wlh sam bazai yiwu ba,mukhtar ko baka qaunar Allah sai ka ci gaba da zama da ni,babu wanda zan sanarwa ma ka yimin saki uku,wallahi yanzu na fara aurenka" maganar da tayi kenan wadda ta sanya mai adaidaitam juyowa ya dubeta,banda kayan jikinta da basu nuna alamun akwai hauka tattare da ita ba da babu abinda zai hana yace mahaukaciya ce,a qofar gidansu ya sauketa ya juya ya kama gabansa.
Tunda ya bar asibitin gida ya wuce kansa tsaye tamkar wani mahaukacu,kuka yake wiwi da haka ya kashe motarsa qofar gidan ba tare da ya samu qwarin gwiwar tura dan matsakaicin get din ba bare ya iya shiga da ita,dakinsa ya wuce ya fada saman gado yana dafe da kansa,me yasa sumayya zata yi masa haka?,wanne abu ya mata da zata saka masa da wannan?,zata rabashi da gudan jininsa,sata rabashi da burin rayuwarsa,shin ta manta cewa samun d'a shine CUKAR BURINSU shi da ita?,wani kukan ya sake saki kamar qaramin yaro,sai a lokacin ya fara ambaton sunayen Allah daya bayan daya,sannu a hanakali nutsuwa ta fara saukar masa,yabar tumurmusa gadon da yake yayi luf saman gadom cikin yanayin na kwanciyar rub da ciki idanunsa na ci gaba da fidsa qwalla masu zafi.
**** ***** *****
Kwana daya rak amma sunfi kwanaki dubu ciwo da wahala a rayuwarta,baki daya ta sauya kamar ba sumayya ba,tayi wani mugun dashewa wanda ya sanya nurses suka soma tunanin tana buqatar qarin jini ko babu jini jikinta,da likita ya duba sai yaga magungunan qarin jini ma kadai sun isheta sai maida kai gun cin abin mai lafiya.
Ko kallon abincin bata yi bare ta kai ga ci,ko ruwa bata iya kurba a bakinta,ki da yaushe tana kwance idanunta rufe kamar mutum mutumi,sai da malam yazo shi daya ya shiga dakin sukayi magana ta tsawon mintina kusan ashirin shi da ita sannan aka fara samun salama,takan karbi duk abinda aka bata taci koda zata yi amansa,hakan ba um ba um um sai zubda hawaye tamkar qwayar idonta zai tsiyaye,kusan kowa tausaya mata yake tare da girgiza da al'amarin,duk da cewa har yau malam kawai ta iya yiwa bayanin abinda ya faru shi kuma ya sanar da abubakar da umma sadiya,sosai umma sadiyan ta fusata qwarai tace sam ba zasu yarda ba tilas su maka mukhtar a kotu shi da zainab din baki daya,baisan halin sumayyan bane?,yarinyar da kusan shi ya qarasa yi mata tarbiyya,malam ne ya hana yace sam hakan baida amfani,tunda koda sun aikata hakan ba zasu iya maida hannun agogo baya ba,ba zasu iya gyara lamarin ba tunda abinda zai faru ya riga da ya farun,da wannan zancan suka rufe batun suka maida hankali wajen kula da lafiyar sumayyan.
"Yanzu shikenan anty?,gurin wa zan dinga zuwa" sosai ta bata tausayi,yarinyar da dududu bata wuce shekara sha tara ba amma ta hadu da kaidin kishiyoyi kala kala,sai ta saki abinda take ta koma gefanta ta zauna
"Kina da Allah sumayya,baya ga haka akwai waya hannunki,duk abinda ya shige miki duhu ki kirani ki tambayeni,koda babu kudi a ciki kimin plashing zan kiraki da yardar Allah,ki ninka haqurinki kawai,domin duk wata mace da kika ga ta zama wata gidan mijinta ki tambayeta wanne irin haquri ta hadiya kafin ta kai ga cimma wannan matakin"
"To anty na gode"
"Babu godiya,ke diyata ce kamar su yasmin kike a gurina.....amma sumayya yanayin jikinki kamar ya sauya?,ko baki kula ba?" Ta fada tana kallonta
"Me kika gani anty?"
"Bakya jin wani sauyi a jikinki?"
"Babu abinda nake ji" ta fada tana kallon anty,shiru ta danyi sannan tace
"Shikenan.....koyaya kika ji wani abu kada ki zauna,kije asibiti"duk da bata fahimci abinda take nufi ba amma ta amsa mata da to.
Ana gab da sallar magariba ta koma gida,a gajiye ta koma,bandaki kawai ta fara shiga tayi wanka ya daura alwala,sai da ta kammala sallahr magariban sannan ta fita,cikin kitchen taji motsinta sai ta tura qofar ta shiga,tana tsaye tana hada food flask na abincin mukhtar,qarasawa tayi kusa da ita ta mata sallama,kai kawai ta daga ta dubeta ta maida kai taci gaba da abinda take ba tare data amsa ba,ita din ma bata damu data amsa ba kai tsaye ta jeho mata tambayar da ta fito da ita
"ina abincina zainab,banga flask dina ba"
Dagowa tayi sosai ta sake kallonta,sai ta saka wata dariya data sanya dole sumayyan ta tsaya tana kallonta cike da alamar tambaya,sai da ta tsagaita don kanta sannan tace
"Ince ko baki samu labarin baki da abinci a gidan nan ba" jin maganar tayi banbarakwai,ba kuma ta fahimci inda ta sa gaba ba,saboda haka taci gaba da kallonta,dauke kai tayi daga bisani sai ta nufi dan qaramin store din dake kitchen din da niyyar fiddo da ko indomie ce ta tafasa,sai ta tarad da store din a garqame da kwado,waiwayowa tayi ta sake duban zainab din
"Naga alamun baki fahimta ba,amma bari nayi miki bayani dalla dalla,mukhtar ya soke baki abincinsa,walau ni na dafa ko ke kika dafa kin fahimta ai yanzu ko?" Sosai maganar ta daketa,sai ta kasa furta komai baya ga wani abu da ya tokare maqoshinta,bata fahimci me hakan ke nufi,tilas ta jira dawowarsa tunda shi ya ajiyeta ba zainab ba,wannan maganar ba tata bace. Wuce zainab din tayi ta nufi sashenta ta dauki tukunya ta tari ruwa ta dora kan gas tare da jefa lipton,tilas ta sanya wani abu a cikinta ba don haka ba abinda take ji cikin zuciyarta bata jin wani abu mai suna abinci zai iya wucewa ta maqogoronta.
Hannayenta ta harde saman qirjinta tana jiran ruwan ya tafasa,tamkar zata fadi haka take ji,ga yunwa ga bacin rai,tana kammalawa ta juye a cup ta nufi daki,bata ko bi ta kan qananun habaicin da zainab keta jefawa cikin waqe,don yanzu bata ita take ba ta kanta take. Tea ta hada da kayan shayinta wanda dama a dakin suke.
Ko rabi bata sha ba ta soma yunqurin dawo da shi,sai data amayar da shi tas sannan ta dawo ta zube qasan carfet din dakin cikinta naci gaba da juyawa,rasa abinda ke mata dadi tayi,fashewa tayi da kuka tana kiran sunan Allah.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
3⃣1⃣
________________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wa bashshiris sabirin,Allazi a iza asabathum musibatun qalu innalillahi wa inna ilaihi raji'un*
_ka yiwa(ya annabin Allah) masu haquri bushara,sune wadanda idan musiba ta samesu suke fadin daga Allah muke kuma gareshi zamu koma_
*Allah ka sanya mu cikin wadanda zaka yiwa kyakkyawan sakamako sanadiyyar fadan wannan kalma*
_________________________________
Zainab qanwarta ce akan gaba,sai mama da yaya abubakar halima na biye da shi,umma sadiya qanwar babansu na biye da su
"Yaya sannu yanzu muka ga ya mukhtar din ma ai ya fita" ta fada ba tare da sun ankara baki daya da yanayinda take ciki ba,haka ma basu lura da zainab dake tsaye gefe ba tana tsuma tare da kallon fitsarin da ya gama wanke mata qafafu. Kallo daya mamanta ta yi mata ta fuskanci ba dai dai taje ba duk da cewa akwai ciwo tattare da ita.
Da idanu kawai take binsu tana fata ta farka daga mummunan mafarkin da takeyi,sai da maman ta qarasa gefan gadon ta zauna ta soma yi mata sannu sannan sumayya ta tabbatarwa kanta idanuntq biyu,a zahiri komai ke faruwa,wata cukuikuya ta yiwa maman nata tana sauke wata ajiyar zuciya tare da fadin
"Ya sakeni mama,ya rabu da ni bayan bani da wani laifi",cikin rudani suke kallonta duk suna zaton zafin ciwo ne
"Sumayya zafin ciwo ne duka hakan?" Sai ta fashe da wani kuka mai azabar cin rai tana maimaita fadin
"Walllahi mama ya sakeni,yanzun nan da kuka ganshi ya fita sakina yayi mama" salati suka saka baki daya wanda ya dawo da zainab hayyacinta
"Allah ya isa 'yarku ta jawo min masifa,ta jawo min zawarci kashi na biyu garin qoqarin zubar da cikinta" ta fada tana wucewa fuuuu ta bar dakin.
Shiru ya ratsa dakin,babu wani abu dake tashi sai shashsheqar kukan sumayya wanda zainab da halima ke tayata saboda tsantsar tausayin 'yar uwarsy,yayin da zuciyoyin sauran ke quna,zancan zainab kuma ke musu kai kawo
"Mama har saki uku yaya mukhtar ya yimin,mama wallahi ban aikata ba,na fishi son naga na haihu mama ki......." Sai ta fara jan numfashi da qyar wanda hakan ya sanya su sake rudewa,da sauri yaya abubakar ya nufi reception don kiran nurse ko likita,cin qanqanin lokaci sai gashi tare da likita wanda yake gab da tashi Allah yasa bai fita ba,waje ya fid dasu baki daya sannan ya rufe dakin,take suka rude da koke koke cike da tashin hankali.
Kusan mintina talatin sannan likitan ya fito bayan ya gama dubata ya mata allurar bacci tare da sanya mata wani ruwan,ya sanar musu bata buqatar hayaniya,sannan don Allah su guji tada mata hankali idan baso suke ta hadu da hawan jini ba,don ko a yanzun jini nata ya fara sama,bugu da qari kuma ta zubda jini mai yawa,godiya suka yi masa sannan suka koma dakin kowa ya samu gu ya zauna zugum,dukkansu da abinda suke saqawa zukatansu,daga bisani yaya abubakar ya fice dan yi musu siyesiyen abubuwan da zasu buqata kafin suga yadda hali zaiyi.
Tun a hanya take sumbatu,ko da wasa bata taba zaton ramin da ta haqa zai rufta da ita ba,bata taba ganin masifa irin wannan ba,taga samu taga rashi,gidan da takewa kanta hasashen samun abun duniya yau dare daya an rabata da shi
"Ina!!!,wlh sam bazai yiwu ba,mukhtar ko baka qaunar Allah sai ka ci gaba da zama da ni,babu wanda zan sanarwa ma ka yimin saki uku,wallahi yanzu na fara aurenka" maganar da tayi kenan wadda ta sanya mai adaidaitam juyowa ya dubeta,banda kayan jikinta da basu nuna alamun akwai hauka tattare da ita ba da babu abinda zai hana yace mahaukaciya ce,a qofar gidansu ya sauketa ya juya ya kama gabansa.
Tunda ya bar asibitin gida ya wuce kansa tsaye tamkar wani mahaukacu,kuka yake wiwi da haka ya kashe motarsa qofar gidan ba tare da ya samu qwarin gwiwar tura dan matsakaicin get din ba bare ya iya shiga da ita,dakinsa ya wuce ya fada saman gado yana dafe da kansa,me yasa sumayya zata yi masa haka?,wanne abu ya mata da zata saka masa da wannan?,zata rabashi da gudan jininsa,sata rabashi da burin rayuwarsa,shin ta manta cewa samun d'a shine CUKAR BURINSU shi da ita?,wani kukan ya sake saki kamar qaramin yaro,sai a lokacin ya fara ambaton sunayen Allah daya bayan daya,sannu a hanakali nutsuwa ta fara saukar masa,yabar tumurmusa gadon da yake yayi luf saman gadom cikin yanayin na kwanciyar rub da ciki idanunsa na ci gaba da fidsa qwalla masu zafi.
**** ***** *****
Kwana daya rak amma sunfi kwanaki dubu ciwo da wahala a rayuwarta,baki daya ta sauya kamar ba sumayya ba,tayi wani mugun dashewa wanda ya sanya nurses suka soma tunanin tana buqatar qarin jini ko babu jini jikinta,da likita ya duba sai yaga magungunan qarin jini ma kadai sun isheta sai maida kai gun cin abin mai lafiya.
Ko kallon abincin bata yi bare ta kai ga ci,ko ruwa bata iya kurba a bakinta,ki da yaushe tana kwance idanunta rufe kamar mutum mutumi,sai da malam yazo shi daya ya shiga dakin sukayi magana ta tsawon mintina kusan ashirin shi da ita sannan aka fara samun salama,takan karbi duk abinda aka bata taci koda zata yi amansa,hakan ba um ba um um sai zubda hawaye tamkar qwayar idonta zai tsiyaye,kusan kowa tausaya mata yake tare da girgiza da al'amarin,duk da cewa har yau malam kawai ta iya yiwa bayanin abinda ya faru shi kuma ya sanar da abubakar da umma sadiya,sosai umma sadiyan ta fusata qwarai tace sam ba zasu yarda ba tilas su maka mukhtar a kotu shi da zainab din baki daya,baisan halin sumayyan bane?,yarinyar da kusan shi ya qarasa yi mata tarbiyya,malam ne ya hana yace sam hakan baida amfani,tunda koda sun aikata hakan ba zasu iya maida hannun agogo baya ba,ba zasu iya gyara lamarin ba tunda abinda zai faru ya riga da ya farun,da wannan zancan suka rufe batun suka maida hankali wajen kula da lafiyar sumayyan.