Sashe 29
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har ta kammala babu shi babu alamarsa,ta juye ta koma daki da abincinta zuciyarta na raunana,saboda wannan ne karo na farko data taba ganin sauyi daga gareshi har irin haka.
**** ***** ****
Cikin kwanakin wani amarci ta dinga gani cikin gidan wanda bata tsammata ba,baki daya kamar daukar mukhtar din akayi aka sauya mata shi,hutu ya dauka na fita kasuwa har na kwanaki bakwai,ko yaushe suna daki idan kaga fitowarsa salla ce zaya yi,saita wuni sur bata sanyashi cikin idanunta ba,abun na taba ranta saidai bata yarda ta fiya zurfafa lamarin cikin ranta,runda anty dije ta gaya mata dole zata iya ganin wasu sauye sauye duk son da yake mata,amarya kota buzuz ce sai an mata rawar qafa,to bare baya ga wannan babu wani sauyi da ta gani cikin ma'amalarsu shi da ita.
*KUNDIN QADDARA TA*
Kwanaki uku take zaton zaya yiwa zainab din tunda bazawara ce,sai gashi ya shiga cikin kwana na hudu biyar shida har zuwa bakwai.
Ranar kwana na bakwai din a ranar zaya soma fita kasuwa,tana kwance dakinta bayan sha daya na safe taji sallamarsa,sai ta miqe ta zauna tana amsa masa,fuskarta babu yabo babu fallasa,gefanta ya samu ya zauna yana fadin
"Ranki ya dade kinyi wuyar gani" ido ta daga ta dubeshi,lallai ne wai ita za'a yiwa halin maza,magana yake gaya mata a fakaice koko yaya,duk da hakan sai ta dake ta kuma basar ta kaufa zancan ta hanyar fadin
"Ina kwana"
"Lafiya sumy ta,kinga na qarawa zainab kwana ko,kinga baquwace tace kuma tan tsorom zama ita daya" wani haushi ya taso ya turniqeta,budurwa ce zainab din ko yau ta fara zaman gidan aure,ko ko tsabagen rainin wayo ne,wadan nan kalaman takeson gayawa mukhtar din amma girmansa da take gani yasa ta gaza furtasu ta hadiye kayanta sai ta bige da cewa
"Ko,Allah sarki" daga yanayin da tayi maganar kawai ya tabbatar masa cewa ta inda zancansa ya shiga ta nan ya fice.
Kafin su sake cewa wani abu zainab din ta daga labulen dakin ta danno tana fadin
"Dear fito mana na rakaka,ina ta jira fa"
"Ai gani nan" ya fada yana fiddo kudin cefane daga aljihunsa,wani banzan kallo da sumayyan batasan ta iyashi ba sai yau ta jefawa zainab sannan ta miqe zata fice ta bar musu dakin,mukhtar yace
"Ina kuma zaki sumayya bamu gama magana ba"
"Baka shirya yin maganar da ni bane" ta fada tana shigewa toilet abinta ta soma daura alwalar sallar walhar da dama ita take shirib tashi tayi.
Tana jiyosu daga nan zainab din na gaya masa ya qyaleta yazo su tafi,yace a'a taje falo ta jirashi zaya fito yanzu,a bandakin ya cimmata ta gama alwalar tana gyara daurin kallabinta,fuska a hade cikin kakkaurar murya yace mata
"Wai wane irin hali kika koya sumayya wanda ban sanki da shi ba,wannan wannw irin wulaqanci ne ina miki magana kina tafiya gaban zainab salon ki koya mata yadda zata raina ni", tsayawa tayi tana kallon ikon Allah,lallai a daki mutum a kuma hanashi kuka.
" ai tare muka siyi foam din makarantar koyon sabbin halaye ni da kai muka cike,muka kuma fara daukar darasi a ciki"sarai yaso ya fahimceta amma sai ya waske
"Wai duka sumayya don na qarawa zainab kwanaki kike wannan abun,yanzun ban isa da gidana ba kenan?"
"Isa kai,tunda gashi ka nuna salon taka isar" ta fada tana kashe famfo tare da qoqarin rabeshi ta wuce,sai ya janyota jikinsa ya matse gam,yasan kan abarsa take ya fara sauke mata fushinta,yayi nasara kam don itama bata bijire masa ba,don babu qarya tayi kewar mijinta sosai.
Ita ta fara zame jikinta sannan tace
"Ka gayawa matarka kada ta sake shigo kin daki kanta tsaye,sabida hakan ya sabawa dokar addinin musulunci idan ita din bata sani ba" sai ya lumshe ido ya dafe kai
"Oh sumayya harda mita ma sai da kika koya,to ayi haquri" daga nan sukayi sallama ya ajjiye mata kudin cefane duk da suna da komai.
Sosai zainab din ta qulu,ta fara lura sumayyan ta shalle zatonta,amma daga yau zata fara dasa bamabamanta cikin gidan,shanye komai tayi ta masa rakiya kamar ta hadeshu,duk yadda ya nuna jin dadinsa a fili amma zuciyarsa ta gaza karbar hakan,a boye ma Allah Allah yake ta koma ya samu ya fice daga gidan.
Da azahar ta shiga kitchen ta musu girkin rana,tana fitowa ta samu zainab din a falon zaune tana kallo,qafarta daya kan daya tana amsa waya,har sumayyan ta gifata ta taji ance
"Ke!" Da fari tayi zatan cikin wayarta ne sai taji ta sake cewa
"Ke dake nake magana sumayyata" waiwayowa tayi tana tsaye daga inda take
"Wai da ni kike?"
"Akwai wata mai sunan ne bayanke a gidan nan,koma ki dauko min abinci na".
Baki ta sake tana kallonta cikin mamaki,ita kuma nata salon kenan,sai ta kada kai kawai tace
" idan kin damu ki shiga da kanki ki dauko"
"Ni kike gayawa wannan maganar,lallai yau zaki gane niba irin sauran kishiyoyinki bane,wallahi yau sai kin gane matsayina gun mukhtar" bata tsaya bi ta kanta ba tayi komawarta daki don tana da abunyi.
Lambar mukhtar ta soma laluba tana huci,yana tsaka da sallamar custumer yaga kiran nata,sai da yaji wani dumm cikin kansa da yaga sunar,ko kadan baiyi farinciki ba amma sai ya gaza share kiran
"Amarya bakya laifi,ya gidan"
"Gida ba lafiya ba,mukhtar na fuskanci ka auroni ne don matarka ta rainani"
"Ya salam,me ya faru me tayi miki?"
"Bazan hanaka sana'a ba kabari idan ka dawo kaji koma mene ne,amma wallahi idan baka dauki mataki ba bazan ci gaba da zama cikin gidan nan ba" sai yaji wata faduwar gaba da sauri yace
"Haba zainab ki daina fadar wannan maganar mana,mai rabu mu ai sai Allah,bari na kira ita sumayyan naji" da sauri ta katseshi don bata son ya mata fadan tun yanzu lamarin ya wuce ba tare data iza wutar tafi haka ba
"A'ah nidai ban saka ba,nace ka bari kawai ka dawo"
"To shikenan sai na dawo din" ya fadi yana sauke wayar,sam jikinsa bai bashi sumayyan zata aikata wani abu na rashin mutunci ga zaina din ba,amma sai ya samu kansa da yarda da duka magan ganun zainab din.
Tun shuda saura ta gama fesa kwalliya tare da bade jikinta da turarenta data tanada na musamman wanda ke hargitsa tunani da lissafin mukhtar ya dinga maida su ba dai dai ba.
Cikin izza da isa ta fito daga dakin nata hannunta dauke da jug na kwalba wanda ta cikashi da lemin zobo da cups dinsa,tana tafe tana murmushin tarkon data d'ana ta ratso ta falo don fita harabar gidan,so take mukhtar din ya fara karo da ita kafin kowa saboda abinda ta tsara ya tafi dai dai ba tare da mishkila ba,idanunta ne suka sauka kan sumayya tada tsume cikin tata kwalliyar,wani irin material ne mai santsi kamar yanayin shufom saidai ya fishi kauri da aka matsawa dinkin wata shegiyar gown wadda ta fidda duk wata qira tata,kalar pink(ruwan hoda) ne mai turuwa,tayi amfani da dankunne da siririyar sarqa fashion baqaqe,hakanan abun hannunta zuwa zobe,take farincikin dake ranta ya ja baya ta raina tata kwalliyar data hasko farar fata ta hadu da pink da baqi,kishi ya sake taso mata,ya zama lallai kota halin qaqa tayi rugu rugu da gwamnatin sumayyan cikin zuciyar mukhtar ya zama tata ke wannan tashen,ta yadda zata yaga yarinyar yadda taga dama,yarinyar na neman fin qarfin zatonta,don ba'a rufe awa ba taga yadda ta tashi hankalin gidan da qamshin girkin abincin dare,ranta na suya ta fuce fuuu wanda sumayya bata ma lura da ita ba sai ficewarta ta gani kamar guguwa.
_tofa,yanzu ake yinta,muje zuwa_
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
2⃣6⃣
_______________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wa may yattaqil laha yaj'al lahu min amrihi yusrah*
_duk wanda yaji tsoron Allah Allah zai sanya masa sauqi cikin lamuransa_
_______________________
Su biyun ne zaune cikin falon kowa na sabgar gabanta,sumayya na guga saboda socket dinta ya lalace ya tilasta mata fitowa falon don yin gugar,yayin da zainab ke zaune saman kujera qafa daya kan daya kamar yadda ta saba zama kenan cikin izza da nuna ita watace,gama share falon da mopping dinta kenan ga zauna don ta huta,duk wanda ke da girki shike wannan aikin,ba laifi zainab din nada tsafta dai dai gwargwado.
Sallamar da ake zabgawa daga harabar gidan shi yaja hankalinsu,zainab ce ta miqe tare da ajjiye remote din hannunta ta bude qofar ta fita,fadima ce ita da jamila diyar yaya yahanasu,bakinsu a washe suka soma takowa zuwa inda take
"Ku tsaya daga nan da Allah ku cire takalmanku kada ku batawa mutane waje yanzu na gama mopping" da fari jamila tayi dum amma ganin fadima ta tsugunna ta cire nata ya sanya itama dole ta cire,juyawa tayi fuska a cusgune su kuma suka bi bayanta.
Zama tayi kan kujerar ta maida qafarta yadda take,suna shirin zama saman kujerar da sauri tace
"A'ah,da Allah ku zauna a qasa,ai carfet ne,idan kuma baku iyawa ku tafi can ga nata kujerun can ku zauna a kai" tsabar qin da suka yiwa sumayyan suka gwammaci zama a qasa,suka gaidata ta amsa da qyar,ko kusa baau dubi sumayya dake guga ba,haka suma ko qurar data kwasosu bata kalla ba
"Dama yaayaa ce ta aiko mu gun yaya muntari" inji fadima,wani kallo ta watsa musu
"Bacci yake,ku fadi saqon sai na gaya masa idan ya tashi" shiru suka dan yi sannan suka dubi juna alamar basu son fada,hakan yasa ta dubesh kai tsaye
"Sai ku tashi ku koma da saqonku,ko kuma wadda ta aiko kun tazo da kanta"
"Yaaya yahanasun?" Suka fada tare cikin mamaki
"Eh,ita din mana,to meye?,kunga ku tashi ku bani guri da Allah,muta ne sai shegen binbinin tsiya haba" ta fada tana jan tsaki tare da mai da kanta gun t.v.
**** ***** ****
Cikin kwanakin wani amarci ta dinga gani cikin gidan wanda bata tsammata ba,baki daya kamar daukar mukhtar din akayi aka sauya mata shi,hutu ya dauka na fita kasuwa har na kwanaki bakwai,ko yaushe suna daki idan kaga fitowarsa salla ce zaya yi,saita wuni sur bata sanyashi cikin idanunta ba,abun na taba ranta saidai bata yarda ta fiya zurfafa lamarin cikin ranta,runda anty dije ta gaya mata dole zata iya ganin wasu sauye sauye duk son da yake mata,amarya kota buzuz ce sai an mata rawar qafa,to bare baya ga wannan babu wani sauyi da ta gani cikin ma'amalarsu shi da ita.
*KUNDIN QADDARA TA*
Kwanaki uku take zaton zaya yiwa zainab din tunda bazawara ce,sai gashi ya shiga cikin kwana na hudu biyar shida har zuwa bakwai.
Ranar kwana na bakwai din a ranar zaya soma fita kasuwa,tana kwance dakinta bayan sha daya na safe taji sallamarsa,sai ta miqe ta zauna tana amsa masa,fuskarta babu yabo babu fallasa,gefanta ya samu ya zauna yana fadin
"Ranki ya dade kinyi wuyar gani" ido ta daga ta dubeshi,lallai ne wai ita za'a yiwa halin maza,magana yake gaya mata a fakaice koko yaya,duk da hakan sai ta dake ta kuma basar ta kaufa zancan ta hanyar fadin
"Ina kwana"
"Lafiya sumy ta,kinga na qarawa zainab kwana ko,kinga baquwace tace kuma tan tsorom zama ita daya" wani haushi ya taso ya turniqeta,budurwa ce zainab din ko yau ta fara zaman gidan aure,ko ko tsabagen rainin wayo ne,wadan nan kalaman takeson gayawa mukhtar din amma girmansa da take gani yasa ta gaza furtasu ta hadiye kayanta sai ta bige da cewa
"Ko,Allah sarki" daga yanayin da tayi maganar kawai ya tabbatar masa cewa ta inda zancansa ya shiga ta nan ya fice.
Kafin su sake cewa wani abu zainab din ta daga labulen dakin ta danno tana fadin
"Dear fito mana na rakaka,ina ta jira fa"
"Ai gani nan" ya fada yana fiddo kudin cefane daga aljihunsa,wani banzan kallo da sumayyan batasan ta iyashi ba sai yau ta jefawa zainab sannan ta miqe zata fice ta bar musu dakin,mukhtar yace
"Ina kuma zaki sumayya bamu gama magana ba"
"Baka shirya yin maganar da ni bane" ta fada tana shigewa toilet abinta ta soma daura alwalar sallar walhar da dama ita take shirib tashi tayi.
Tana jiyosu daga nan zainab din na gaya masa ya qyaleta yazo su tafi,yace a'a taje falo ta jirashi zaya fito yanzu,a bandakin ya cimmata ta gama alwalar tana gyara daurin kallabinta,fuska a hade cikin kakkaurar murya yace mata
"Wai wane irin hali kika koya sumayya wanda ban sanki da shi ba,wannan wannw irin wulaqanci ne ina miki magana kina tafiya gaban zainab salon ki koya mata yadda zata raina ni", tsayawa tayi tana kallon ikon Allah,lallai a daki mutum a kuma hanashi kuka.
" ai tare muka siyi foam din makarantar koyon sabbin halaye ni da kai muka cike,muka kuma fara daukar darasi a ciki"sarai yaso ya fahimceta amma sai ya waske
"Wai duka sumayya don na qarawa zainab kwanaki kike wannan abun,yanzun ban isa da gidana ba kenan?"
"Isa kai,tunda gashi ka nuna salon taka isar" ta fada tana kashe famfo tare da qoqarin rabeshi ta wuce,sai ya janyota jikinsa ya matse gam,yasan kan abarsa take ya fara sauke mata fushinta,yayi nasara kam don itama bata bijire masa ba,don babu qarya tayi kewar mijinta sosai.
Ita ta fara zame jikinta sannan tace
"Ka gayawa matarka kada ta sake shigo kin daki kanta tsaye,sabida hakan ya sabawa dokar addinin musulunci idan ita din bata sani ba" sai ya lumshe ido ya dafe kai
"Oh sumayya harda mita ma sai da kika koya,to ayi haquri" daga nan sukayi sallama ya ajjiye mata kudin cefane duk da suna da komai.
Sosai zainab din ta qulu,ta fara lura sumayyan ta shalle zatonta,amma daga yau zata fara dasa bamabamanta cikin gidan,shanye komai tayi ta masa rakiya kamar ta hadeshu,duk yadda ya nuna jin dadinsa a fili amma zuciyarsa ta gaza karbar hakan,a boye ma Allah Allah yake ta koma ya samu ya fice daga gidan.
Da azahar ta shiga kitchen ta musu girkin rana,tana fitowa ta samu zainab din a falon zaune tana kallo,qafarta daya kan daya tana amsa waya,har sumayyan ta gifata ta taji ance
"Ke!" Da fari tayi zatan cikin wayarta ne sai taji ta sake cewa
"Ke dake nake magana sumayyata" waiwayowa tayi tana tsaye daga inda take
"Wai da ni kike?"
"Akwai wata mai sunan ne bayanke a gidan nan,koma ki dauko min abinci na".
Baki ta sake tana kallonta cikin mamaki,ita kuma nata salon kenan,sai ta kada kai kawai tace
" idan kin damu ki shiga da kanki ki dauko"
"Ni kike gayawa wannan maganar,lallai yau zaki gane niba irin sauran kishiyoyinki bane,wallahi yau sai kin gane matsayina gun mukhtar" bata tsaya bi ta kanta ba tayi komawarta daki don tana da abunyi.
Lambar mukhtar ta soma laluba tana huci,yana tsaka da sallamar custumer yaga kiran nata,sai da yaji wani dumm cikin kansa da yaga sunar,ko kadan baiyi farinciki ba amma sai ya gaza share kiran
"Amarya bakya laifi,ya gidan"
"Gida ba lafiya ba,mukhtar na fuskanci ka auroni ne don matarka ta rainani"
"Ya salam,me ya faru me tayi miki?"
"Bazan hanaka sana'a ba kabari idan ka dawo kaji koma mene ne,amma wallahi idan baka dauki mataki ba bazan ci gaba da zama cikin gidan nan ba" sai yaji wata faduwar gaba da sauri yace
"Haba zainab ki daina fadar wannan maganar mana,mai rabu mu ai sai Allah,bari na kira ita sumayyan naji" da sauri ta katseshi don bata son ya mata fadan tun yanzu lamarin ya wuce ba tare data iza wutar tafi haka ba
"A'ah nidai ban saka ba,nace ka bari kawai ka dawo"
"To shikenan sai na dawo din" ya fadi yana sauke wayar,sam jikinsa bai bashi sumayyan zata aikata wani abu na rashin mutunci ga zaina din ba,amma sai ya samu kansa da yarda da duka magan ganun zainab din.
Tun shuda saura ta gama fesa kwalliya tare da bade jikinta da turarenta data tanada na musamman wanda ke hargitsa tunani da lissafin mukhtar ya dinga maida su ba dai dai ba.
Cikin izza da isa ta fito daga dakin nata hannunta dauke da jug na kwalba wanda ta cikashi da lemin zobo da cups dinsa,tana tafe tana murmushin tarkon data d'ana ta ratso ta falo don fita harabar gidan,so take mukhtar din ya fara karo da ita kafin kowa saboda abinda ta tsara ya tafi dai dai ba tare da mishkila ba,idanunta ne suka sauka kan sumayya tada tsume cikin tata kwalliyar,wani irin material ne mai santsi kamar yanayin shufom saidai ya fishi kauri da aka matsawa dinkin wata shegiyar gown wadda ta fidda duk wata qira tata,kalar pink(ruwan hoda) ne mai turuwa,tayi amfani da dankunne da siririyar sarqa fashion baqaqe,hakanan abun hannunta zuwa zobe,take farincikin dake ranta ya ja baya ta raina tata kwalliyar data hasko farar fata ta hadu da pink da baqi,kishi ya sake taso mata,ya zama lallai kota halin qaqa tayi rugu rugu da gwamnatin sumayyan cikin zuciyar mukhtar ya zama tata ke wannan tashen,ta yadda zata yaga yarinyar yadda taga dama,yarinyar na neman fin qarfin zatonta,don ba'a rufe awa ba taga yadda ta tashi hankalin gidan da qamshin girkin abincin dare,ranta na suya ta fuce fuuu wanda sumayya bata ma lura da ita ba sai ficewarta ta gani kamar guguwa.
_tofa,yanzu ake yinta,muje zuwa_
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[27/12, 22:44] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
2⃣6⃣
_______________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wa may yattaqil laha yaj'al lahu min amrihi yusrah*
_duk wanda yaji tsoron Allah Allah zai sanya masa sauqi cikin lamuransa_
_______________________
Su biyun ne zaune cikin falon kowa na sabgar gabanta,sumayya na guga saboda socket dinta ya lalace ya tilasta mata fitowa falon don yin gugar,yayin da zainab ke zaune saman kujera qafa daya kan daya kamar yadda ta saba zama kenan cikin izza da nuna ita watace,gama share falon da mopping dinta kenan ga zauna don ta huta,duk wanda ke da girki shike wannan aikin,ba laifi zainab din nada tsafta dai dai gwargwado.
Sallamar da ake zabgawa daga harabar gidan shi yaja hankalinsu,zainab ce ta miqe tare da ajjiye remote din hannunta ta bude qofar ta fita,fadima ce ita da jamila diyar yaya yahanasu,bakinsu a washe suka soma takowa zuwa inda take
"Ku tsaya daga nan da Allah ku cire takalmanku kada ku batawa mutane waje yanzu na gama mopping" da fari jamila tayi dum amma ganin fadima ta tsugunna ta cire nata ya sanya itama dole ta cire,juyawa tayi fuska a cusgune su kuma suka bi bayanta.
Zama tayi kan kujerar ta maida qafarta yadda take,suna shirin zama saman kujerar da sauri tace
"A'ah,da Allah ku zauna a qasa,ai carfet ne,idan kuma baku iyawa ku tafi can ga nata kujerun can ku zauna a kai" tsabar qin da suka yiwa sumayyan suka gwammaci zama a qasa,suka gaidata ta amsa da qyar,ko kusa baau dubi sumayya dake guga ba,haka suma ko qurar data kwasosu bata kalla ba
"Dama yaayaa ce ta aiko mu gun yaya muntari" inji fadima,wani kallo ta watsa musu
"Bacci yake,ku fadi saqon sai na gaya masa idan ya tashi" shiru suka dan yi sannan suka dubi juna alamar basu son fada,hakan yasa ta dubesh kai tsaye
"Sai ku tashi ku koma da saqonku,ko kuma wadda ta aiko kun tazo da kanta"
"Yaaya yahanasun?" Suka fada tare cikin mamaki
"Eh,ita din mana,to meye?,kunga ku tashi ku bani guri da Allah,muta ne sai shegen binbinin tsiya haba" ta fada tana jan tsaki tare da mai da kanta gun t.v.