Sashe 195
Kundin Qaddarata Final Part Complete Hausa Novel · about 8 min read
A falom ta sameta tana tsaye,idanunta sun kada sunyi ja,tabbas kalaman da ta jiyo suna fita daga bakin almustaphan su suka sata shiga taji me yake gaya mata,kalamai ne masu nauyi dake fita daga ainihin qwaryar zuciya,tana zaton mawuyacine fa idan batayi kuskuren da zai hanata sukuni a rayuwarta ba
"Amm....anty yace ki fito zamu tafi"
"Kije kice masa ba zani ba,fitar min daga daki tun ban zagi uban ubanki ba"ta fada cikin tsawa da hargagi idanu ta daga ta dubeta kawai ta jiya a nutse ta fice,tabbas ba don tana tsoron abinda zai biyo baya ba da babu abinda zai hanata shaqo wuyan sumayyan tayita jibgarta kamar Allah ya aikota har sai taga ita da dan cikin nata sun daina motsi,amma ta tabbatar yin hakan dai dai yake da rasa komai cikin rayuwarta,ciki kuwa harda igiyar aurenta da almustaphan.
A tsayen ta sake taddashi ya tsurawa qofar falon ido,ta iso inda yake ta bude bakinta zata roqeshi yaje yaji damuwar su'ad din sai ya daga mata hannu
"wuce mu tafi"kawai yace da ita yana dubanta,ba musu tayi gaba,duk sanda yake cikin fushi yakan koma mata almustaphan nan data sani a farkon rayuwarta,rufa mata baya yayi suka fice.
Cikin katafaren shagon da sukayi fice wajen samar da kayan jarirai suke zagayawa,tana daukan duk abinda taga yayi mata shima yana tayata,fuskarshi a sakw kaman ba dazun ranshi ya baci ba,kayane masu kyau da tsada wanda jinsin mace ko namiji zai iya sanyawa(unisex).
Daga gefansu kadan idanunta suka dinga mata gizo,kaman nuwaira take hangowa ita da wata mata suna zaban kayan yara maza,sai ta ajjiye rigar dake hannunta ta taka a hankali ta qarasa wajen
"Nuwaira" ta fada a hankali,da sauri ta juyo suka hada ido,take fuskarta ta washe da wani madaukakin murmushi,ba don tsinin cikin data gani jikin sumayya ba ba shakka rungumeta zatayi
"Anty sumayya?.....mama kinga anty sumayya,anty sumayyarmu,wayyo yau su basma zasu ji labari naga anty sumayya,yau ya hajiya zata ji saboda dadi" nuwaira keta jero wannan magana ba tsayawa,matar dake gefanta tana murmushi kawai,wanda duba daya zaka mata kaga tsantsar kaman dake tsakaninsu da nuwaira,kyakkyawar macace blcak beauty,wadda kallo daya zaka mata kasan nutsuwa ta ratsata,tana daukw da tsohon ciki wanda ke nuna alamar haihuwa yau ko gobe
"Oh nuwaira,nutsu mana ku gaisa ko tukunna" murmushi itama sumayyan take bakinta yaqi rufuwa suka soma gaisawa da matar sannan ta gabatar mata da kanta
"Ni sunana rumaisa,nice mamar nuwaira,ke kuwa nasan kece sumayya,matar da lukman ya taba aura haka ne?" Kai sumayya ta kada taba murmushi cikin mamaki
"Hakane,amma yaya akayi kika ganeni?" Murmushi itama tayi
"Dole na ganeki ai,mai gida mamarshi da duka yara kullum sai sunyi maganarki...ashe da rabon zamu hadu"
"wallahi kam" sumayya ta fada tana duban nuwaira
"Nuwaira,kinga yadda kika zama budurwa sosai,lallai aure nan kusa kenan" dariya ta saki cikin jin kunya tace
"Anty maman ce fa ta dawo gidan abba na" kai take gyadawa ko bata fada ba ta tsammaci haka
"Naga alama nuwaira masha Allah,Allah ya bada zama lafiya" hango almustapha tayi yana lalubenta da idanunshi don bai san tayi nan ba
"Ni zan wuce nuwaira ina kukayi masauki?"rumaisa ce tace
"nazo ganin likita ne amma nan da kwana hudu zamu koma,amman ki bani adresa dinki in sha Allah zamu zo har gida,nima naji dadin ganinki don naji dukkan wani qoqari da kikayi kan rayuwar diyata da kuma gidan baki daya,kin cancanci muzo mu gode miki" murmushi kawai tayi sukayi musayar lambar waya,ga rubuta adress din jikin qaramar takarda ta bata sannan sukayi sallama suka rabu.
Cikin mota shiru sumayyan tayi,tana tunanin yadda rayuwa take sauyawa bawa a duk sanda Allah yaso,haqiqa rayuwa abar tsoro ce ga dukkan mai tunani,wannan kadai ya isa bawa ishara yasan cewa babu wani abu dake dawwama nan duniya banda ikon Allah,walau dadi ko wuya,komai na wuceea ne tamkar a mafarki,gefw daya tunanin su'ad ya fado mata
"Babyyyyy...." Almustapha ya kira sunanta wanda hakan shi ya sanyata dago kanta ta dubeshi,sai ta dora hannunta saman nashi hannun dake kan giyar motar
"Tunanin me kike yi?" Kai ta kada
"My...meke damun su'ad?" Kai ya kada yana duban titi
"Nima ban sani ba"
"Amma ya kamata ka binciki damuwarta kaji ko?", kusan shekaran jiya abinda yayi kenan,ya tsirata da tambaya,bata da amsa daga bisani ma kuka ta sanya mata tana gaya masa so taje ta gansu daga shi sai ita,duj da akwai wannan cikin zuciyarta amma babban abinda yafi damunta shine ta yaya zata dauki ciki itama kaman sumayyan?,ta samu soyayya tattali da kulawa irin tata?,duk da babu abinda ya rageta da shi
"bansan me take so na mata ba cikin duniya,ban rageta da komai ba,ba abinda ban bata ba babu kuma abinda bana mata,ko yaushe qoqarin tanqwara zuciyata nake don ma saba da halayyarta amma ko da yashe sabon hali take qirqiromin,bana son na aikata mata wani abu da ba dai dai ha ko don mutuncin mahaifinta,ina girmamashi,ina ganin qimarshi....amma ko yaushe kamar ina tunzura ta haka na......" Shiru yayi ba tare daya qarasa ba,ko da can shi bai tattauna matsalar wata cikinsu da wata,ya sani cewa inda hakan me yiwuwa ne sumayya abokiyar shawararshi ce,halayenta sunyi dari bisa darin da ya tabbatar zata iya bashi shawara da mafita kan koma mene ne,shiru itama tayi,ta tabbatat da cewa ya kai maqura shi yasa har yau yake furta wadan nan kalaman,hannunshi take matsawa a tausashe har sai da taji ya saki ajiyar zuciya sannan a hankali ta furta
"Am sorry....Allah ya shiga lamuranmu"
"Amin" ya furta yana jin dadin lafazinta.
Maganar noman audugar da ya sanya ake masa a qasar kano jigawa da zaria ta taso,hakan ya sanya ya shirya zuwa nigeria cikin satin,cikin ikon Allah sai kuma ga haihuwar halima,wadda ta sauka lafiya ta samu namiji,daman can yana da niyyar tafiyar da su don haka ra'ayinshi yake,saboda haka yace su shirya,zasu sauka kano da sumayya,zai barta nan su wuve jigawa da zaria da su'ad tunda ita sumayyan tafiyar zata iya yi mata wahala,hakan itama yayi mata,ko banza tasan zatayi hidimar sunanta hankali kwance,kishin dake damun su'ad cikin zuciyarta tace sam ita ba zata je ba,me zata je yi wani zaria da jigawa?,ta rasa wajen zuwa sai nan?,ranshi ya baci,shima kuma ya motsa qwanjinsa ya nuna mata mazantaka yace sai taje,hakanan ba yadda ta iya ta haqura zata bishin,itakam sumayya ko a jikinta,shiri ta soma yi sosai tana siyan tsaraba,duk da ya hanata fitan tana daga gida take siyayyar ake kawo mata.
Ana gobe su nuwaira zasu tafi suka kawo mata ziyara,tana daki kwance aka shaida mata tana da baqi,ta miqe cikin farinciki ta tar besu har zuwa falonta,duk da nauyin data yi bata zauna ba sai data tana dar musu komai,zata dora abinci rumaisa tace a'a sam,itama tana fama da kanta ne,suma kuma a qoshe suke snack din kawai ya isa,bata rabo da kayan snacks zuwa su dambun nama saboda almustapha,wani lokaci su kadai yake ci a matsayin abinci,hakan ya sanya take yinsu ta saka su a freezer sanda zaici sai ta dauko idan na soyawa ne ta soya masa,idan na gasawa ne ta gasa masa.
Hira suke wadda kusan rabinsu da nuwaira suke yinta,jifa jifa rumaisa ke saka musu baki
"Ina maman naku karima ne?" Murmushi nuwaira tayi
"Daddy ya saketa ta koma garinsu,yanzu kullum bakiga yadda take masa naci ya maidata ba wai ta tuba hajiya tace sam bata dawowa wa,yanzu ma wai ta kusa aure a can" kai sumayya ke jinjinawa,abinda ya faru shine,baki daya rayuwan yaran da mai gidan komawa tayi wajen hajiya,sai kariman ta koma tamkar wata saniyar ware a cikinsu,suna sashen hajiya suna walwalarsu tana vangarenta ita kadai kamar mayya,duk wani qoqari na dawo da yaran rayuwarta da mai gidan amma abu yaci tura,a hankali karima ta soma fita daga kansa,a lokacinne ita kuma ta soma gane kurenta,tayi laqwas ta soma biyayyar qarfi sa yaji saboda ta fuskanci ba wata mafita gareta,saidai ina tunu ta gama fita akan lukman din baki daya,bare hajiya wadda tayi shiru ne kawai saboda darajar yaran da kariman ke da su,uwa uba kuma tayi alqawarin ba zata sake saka dan nata ya saki wata cikin matanshi ba har abada,don taga ishara,Allah ya kawo qarshen zaman nasu,hajiya ta wayi gari lukman ya saki karima har saki biyu,qememe yace bazai maidata ba,don ya kamata da kanshi tana zuba wani abu cikin abincin hajiyan,wanda magani ne qarshe aka bata matuqar baiyi aiki ya dawo mata da rayuwar gidanta yadda take ba daa to malamin nata ya gaya mata tayi haquri kawai,sai gashi bata zuba a sa'a ba ya zama silar tsinkewar igiyar aurenta.
Bayan mutuwar auren da wasu watanni hajiya ta soma sha'awar dawowar rumaisa mahaifiyar nuwaira gidan,wadda ita daya ce ta haihu da lukman,macen kuma data fi duka saurab matan da ya taba aura tsantsar haquri da biyayya,faduwa tazo daidai da zama,don shi dinma rumaisan ke kai kawo cikin ranshi,tunda ya tabbatar da ceea ya rasa sumayya,wadda kabatin aurenta a abuja ya gigitashi fiye da zato,ya soma binciken wanda ta aura,sanda yaci karo da labarin cewa doctor muhammad almustapha mukhtar gombe ne tilas ya aro haquri ya yafawa kanshi,saboda ya kwana da sanin babban goro ne sai magogin qarfe,hakanan bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane,bayan sun rabu da karima sun hadu da rumaisan kusan sau uku a gurare daban daban,saidai ko dubanshi bata yiba bare ya samu fuskar tunkararta,soyayyar da sukayi bata zaci zai rabu da ita haka da wuri ba ba laifin tsaye ba na zaune,ya karbi umarni kawai daga mahaifiyarsa,da qyar aka shawo kanya harda hajiyan wajen lallashi sannan ta yarda aka maida aurensu,wanda dawowarta ya sake dawo da walwalar gidan kaman zamanin da sumayya kenan,duk da hakan basu manta da ita ba kullum kwanan duniya su da hajiya sai sunyi zancanta,wanda har rumaisa ta saba da ji,takan zauba ta tayasu wani lokaci,ko daya rumaisa bata bari abinda karima ta yiwa diyarta yayi tasiri a ranta ba har ta rama kan yaranta guda hudu data bari,ta hadasu ta rungume kamar ita ta haifesu,sannan taci gana da dorawa kan tarbiyyar da sumayya ta azasu wanda hakan yayi mata dadi sosai.
"Amm....anty yace ki fito zamu tafi"
"Kije kice masa ba zani ba,fitar min daga daki tun ban zagi uban ubanki ba"ta fada cikin tsawa da hargagi idanu ta daga ta dubeta kawai ta jiya a nutse ta fice,tabbas ba don tana tsoron abinda zai biyo baya ba da babu abinda zai hanata shaqo wuyan sumayyan tayita jibgarta kamar Allah ya aikota har sai taga ita da dan cikin nata sun daina motsi,amma ta tabbatar yin hakan dai dai yake da rasa komai cikin rayuwarta,ciki kuwa harda igiyar aurenta da almustaphan.
A tsayen ta sake taddashi ya tsurawa qofar falon ido,ta iso inda yake ta bude bakinta zata roqeshi yaje yaji damuwar su'ad din sai ya daga mata hannu
"wuce mu tafi"kawai yace da ita yana dubanta,ba musu tayi gaba,duk sanda yake cikin fushi yakan koma mata almustaphan nan data sani a farkon rayuwarta,rufa mata baya yayi suka fice.
Cikin katafaren shagon da sukayi fice wajen samar da kayan jarirai suke zagayawa,tana daukan duk abinda taga yayi mata shima yana tayata,fuskarshi a sakw kaman ba dazun ranshi ya baci ba,kayane masu kyau da tsada wanda jinsin mace ko namiji zai iya sanyawa(unisex).
Daga gefansu kadan idanunta suka dinga mata gizo,kaman nuwaira take hangowa ita da wata mata suna zaban kayan yara maza,sai ta ajjiye rigar dake hannunta ta taka a hankali ta qarasa wajen
"Nuwaira" ta fada a hankali,da sauri ta juyo suka hada ido,take fuskarta ta washe da wani madaukakin murmushi,ba don tsinin cikin data gani jikin sumayya ba ba shakka rungumeta zatayi
"Anty sumayya?.....mama kinga anty sumayya,anty sumayyarmu,wayyo yau su basma zasu ji labari naga anty sumayya,yau ya hajiya zata ji saboda dadi" nuwaira keta jero wannan magana ba tsayawa,matar dake gefanta tana murmushi kawai,wanda duba daya zaka mata kaga tsantsar kaman dake tsakaninsu da nuwaira,kyakkyawar macace blcak beauty,wadda kallo daya zaka mata kasan nutsuwa ta ratsata,tana daukw da tsohon ciki wanda ke nuna alamar haihuwa yau ko gobe
"Oh nuwaira,nutsu mana ku gaisa ko tukunna" murmushi itama sumayyan take bakinta yaqi rufuwa suka soma gaisawa da matar sannan ta gabatar mata da kanta
"Ni sunana rumaisa,nice mamar nuwaira,ke kuwa nasan kece sumayya,matar da lukman ya taba aura haka ne?" Kai sumayya ta kada taba murmushi cikin mamaki
"Hakane,amma yaya akayi kika ganeni?" Murmushi itama tayi
"Dole na ganeki ai,mai gida mamarshi da duka yara kullum sai sunyi maganarki...ashe da rabon zamu hadu"
"wallahi kam" sumayya ta fada tana duban nuwaira
"Nuwaira,kinga yadda kika zama budurwa sosai,lallai aure nan kusa kenan" dariya ta saki cikin jin kunya tace
"Anty maman ce fa ta dawo gidan abba na" kai take gyadawa ko bata fada ba ta tsammaci haka
"Naga alama nuwaira masha Allah,Allah ya bada zama lafiya" hango almustapha tayi yana lalubenta da idanunshi don bai san tayi nan ba
"Ni zan wuce nuwaira ina kukayi masauki?"rumaisa ce tace
"nazo ganin likita ne amma nan da kwana hudu zamu koma,amman ki bani adresa dinki in sha Allah zamu zo har gida,nima naji dadin ganinki don naji dukkan wani qoqari da kikayi kan rayuwar diyata da kuma gidan baki daya,kin cancanci muzo mu gode miki" murmushi kawai tayi sukayi musayar lambar waya,ga rubuta adress din jikin qaramar takarda ta bata sannan sukayi sallama suka rabu.
Cikin mota shiru sumayyan tayi,tana tunanin yadda rayuwa take sauyawa bawa a duk sanda Allah yaso,haqiqa rayuwa abar tsoro ce ga dukkan mai tunani,wannan kadai ya isa bawa ishara yasan cewa babu wani abu dake dawwama nan duniya banda ikon Allah,walau dadi ko wuya,komai na wuceea ne tamkar a mafarki,gefw daya tunanin su'ad ya fado mata
"Babyyyyy...." Almustapha ya kira sunanta wanda hakan shi ya sanyata dago kanta ta dubeshi,sai ta dora hannunta saman nashi hannun dake kan giyar motar
"Tunanin me kike yi?" Kai ta kada
"My...meke damun su'ad?" Kai ya kada yana duban titi
"Nima ban sani ba"
"Amma ya kamata ka binciki damuwarta kaji ko?", kusan shekaran jiya abinda yayi kenan,ya tsirata da tambaya,bata da amsa daga bisani ma kuka ta sanya mata tana gaya masa so taje ta gansu daga shi sai ita,duj da akwai wannan cikin zuciyarta amma babban abinda yafi damunta shine ta yaya zata dauki ciki itama kaman sumayyan?,ta samu soyayya tattali da kulawa irin tata?,duk da babu abinda ya rageta da shi
"bansan me take so na mata ba cikin duniya,ban rageta da komai ba,ba abinda ban bata ba babu kuma abinda bana mata,ko yaushe qoqarin tanqwara zuciyata nake don ma saba da halayyarta amma ko da yashe sabon hali take qirqiromin,bana son na aikata mata wani abu da ba dai dai ha ko don mutuncin mahaifinta,ina girmamashi,ina ganin qimarshi....amma ko yaushe kamar ina tunzura ta haka na......" Shiru yayi ba tare daya qarasa ba,ko da can shi bai tattauna matsalar wata cikinsu da wata,ya sani cewa inda hakan me yiwuwa ne sumayya abokiyar shawararshi ce,halayenta sunyi dari bisa darin da ya tabbatar zata iya bashi shawara da mafita kan koma mene ne,shiru itama tayi,ta tabbatat da cewa ya kai maqura shi yasa har yau yake furta wadan nan kalaman,hannunshi take matsawa a tausashe har sai da taji ya saki ajiyar zuciya sannan a hankali ta furta
"Am sorry....Allah ya shiga lamuranmu"
"Amin" ya furta yana jin dadin lafazinta.
Maganar noman audugar da ya sanya ake masa a qasar kano jigawa da zaria ta taso,hakan ya sanya ya shirya zuwa nigeria cikin satin,cikin ikon Allah sai kuma ga haihuwar halima,wadda ta sauka lafiya ta samu namiji,daman can yana da niyyar tafiyar da su don haka ra'ayinshi yake,saboda haka yace su shirya,zasu sauka kano da sumayya,zai barta nan su wuve jigawa da zaria da su'ad tunda ita sumayyan tafiyar zata iya yi mata wahala,hakan itama yayi mata,ko banza tasan zatayi hidimar sunanta hankali kwance,kishin dake damun su'ad cikin zuciyarta tace sam ita ba zata je ba,me zata je yi wani zaria da jigawa?,ta rasa wajen zuwa sai nan?,ranshi ya baci,shima kuma ya motsa qwanjinsa ya nuna mata mazantaka yace sai taje,hakanan ba yadda ta iya ta haqura zata bishin,itakam sumayya ko a jikinta,shiri ta soma yi sosai tana siyan tsaraba,duk da ya hanata fitan tana daga gida take siyayyar ake kawo mata.
Ana gobe su nuwaira zasu tafi suka kawo mata ziyara,tana daki kwance aka shaida mata tana da baqi,ta miqe cikin farinciki ta tar besu har zuwa falonta,duk da nauyin data yi bata zauna ba sai data tana dar musu komai,zata dora abinci rumaisa tace a'a sam,itama tana fama da kanta ne,suma kuma a qoshe suke snack din kawai ya isa,bata rabo da kayan snacks zuwa su dambun nama saboda almustapha,wani lokaci su kadai yake ci a matsayin abinci,hakan ya sanya take yinsu ta saka su a freezer sanda zaici sai ta dauko idan na soyawa ne ta soya masa,idan na gasawa ne ta gasa masa.
Hira suke wadda kusan rabinsu da nuwaira suke yinta,jifa jifa rumaisa ke saka musu baki
"Ina maman naku karima ne?" Murmushi nuwaira tayi
"Daddy ya saketa ta koma garinsu,yanzu kullum bakiga yadda take masa naci ya maidata ba wai ta tuba hajiya tace sam bata dawowa wa,yanzu ma wai ta kusa aure a can" kai sumayya ke jinjinawa,abinda ya faru shine,baki daya rayuwan yaran da mai gidan komawa tayi wajen hajiya,sai kariman ta koma tamkar wata saniyar ware a cikinsu,suna sashen hajiya suna walwalarsu tana vangarenta ita kadai kamar mayya,duk wani qoqari na dawo da yaran rayuwarta da mai gidan amma abu yaci tura,a hankali karima ta soma fita daga kansa,a lokacinne ita kuma ta soma gane kurenta,tayi laqwas ta soma biyayyar qarfi sa yaji saboda ta fuskanci ba wata mafita gareta,saidai ina tunu ta gama fita akan lukman din baki daya,bare hajiya wadda tayi shiru ne kawai saboda darajar yaran da kariman ke da su,uwa uba kuma tayi alqawarin ba zata sake saka dan nata ya saki wata cikin matanshi ba har abada,don taga ishara,Allah ya kawo qarshen zaman nasu,hajiya ta wayi gari lukman ya saki karima har saki biyu,qememe yace bazai maidata ba,don ya kamata da kanshi tana zuba wani abu cikin abincin hajiyan,wanda magani ne qarshe aka bata matuqar baiyi aiki ya dawo mata da rayuwar gidanta yadda take ba daa to malamin nata ya gaya mata tayi haquri kawai,sai gashi bata zuba a sa'a ba ya zama silar tsinkewar igiyar aurenta.
Bayan mutuwar auren da wasu watanni hajiya ta soma sha'awar dawowar rumaisa mahaifiyar nuwaira gidan,wadda ita daya ce ta haihu da lukman,macen kuma data fi duka saurab matan da ya taba aura tsantsar haquri da biyayya,faduwa tazo daidai da zama,don shi dinma rumaisan ke kai kawo cikin ranshi,tunda ya tabbatar da ceea ya rasa sumayya,wadda kabatin aurenta a abuja ya gigitashi fiye da zato,ya soma binciken wanda ta aura,sanda yaci karo da labarin cewa doctor muhammad almustapha mukhtar gombe ne tilas ya aro haquri ya yafawa kanshi,saboda ya kwana da sanin babban goro ne sai magogin qarfe,hakanan bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane,bayan sun rabu da karima sun hadu da rumaisan kusan sau uku a gurare daban daban,saidai ko dubanshi bata yiba bare ya samu fuskar tunkararta,soyayyar da sukayi bata zaci zai rabu da ita haka da wuri ba ba laifin tsaye ba na zaune,ya karbi umarni kawai daga mahaifiyarsa,da qyar aka shawo kanya harda hajiyan wajen lallashi sannan ta yarda aka maida aurensu,wanda dawowarta ya sake dawo da walwalar gidan kaman zamanin da sumayya kenan,duk da hakan basu manta da ita ba kullum kwanan duniya su da hajiya sai sunyi zancanta,wanda har rumaisa ta saba da ji,takan zauba ta tayasu wani lokaci,ko daya rumaisa bata bari abinda karima ta yiwa diyarta yayi tasiri a ranta ba har ta rama kan yaranta guda hudu data bari,ta hadasu ta rungume kamar ita ta haifesu,sannan taci gana da dorawa kan tarbiyyar da sumayya ta azasu wanda hakan yayi mata dadi sosai.