Sashe 71
Karfe A Wuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"To ina zan sani, matarsa dai ta ce ba laifinsa bane ba"
"Please count me out of this please, haka kurum na je fito da shi, 'yan adawa su sami na yi mini yarfe, ace nima safararta nake yi? Dama dai wani rashin jin yayi ba wannan ba, ni fa dama Saboda aikina na cin zaɓe siyasa dole sai da irinsu, shiyasa nake fito da shi, amma ban da haka meye haɗina da shi, zan nemi wani ya cigaba da yi mini ayyukana ni babu ruwana"
P.A ya ce "A'a honorable, wani kaya fa sai amale, wallahi ba kowane matashi ne yake da ƙwarin da yake da shi ba, kar ka yar da shi wani ya ɗaka"
"Ka san dai yanzu bana gari ko, dan Allah ka bar ni, ni yanzu lissafin siyasata na saka a gaba, idan ina buƙatar sa a gaba, na fito da shi" ya kashe wayarsa.
P.A ya kalli Jauhar da jikinta yayi sanyi, mamaki ya cika mata kai da zuciya, wato yana amfani da jini da lafiyar Al'amin ne kawai dan cimma nasa burin, abun ya bata mamaki sosai da sosai.
"Madam, kin ji abinda honorable ya ce, amma ki yi haƙuri zuwa ya dawo, mu gani zan cigaba da lallaɓa shi, kar ki damu da abubuwan da ya faɗa, kansa ne ya ɗauki zafi, amma shi da Aminu ba ta ɓaci, in dai wannan harkar ce, ba shi da sama shi".
Ba ta ce masa uffan ba, ta tashi ta fita, yanayin yadda ta fito ne, ya tabbatar masa da akwia matsala.
Ya ce "Yaya? Wani abun yayi miki ko maganar banza yayi miki, na shiga na ci ubansa"
Ta girgiza masa kai alamar a a.
"To meyafaru?"
"Honorable ɗin ya ce babu ruwansa, ba zai shiga maganar ba saboda kar sunansa ya ɓaci" tayi maganar hawaye yana gangarowa daga idanunta.
Walid ya yi shiru, tare da jinjina kai ya ce "Shikenan, bakomai mu tafi"
Haka suka tafi duk jiki a sanyaye, ta ce "Yanzu shikenan babu abun da za ayi? Haka zai cigaba da zama?"
"A'a zai fito, haryanzu ba a gama shari'ar ba ma, dole za a nemi wata hanyar".
Jauhar ta ce "To shikenan, dan Allah ranar juma'a ka zo ka karɓi kayan da na tara, sai ka kai masa".
Walid ya ce "Shikenan, in sha Allah, amma kar ki je ki saka damuwa a ranki, idan da wata matsala, ki kira ni a wayarki"
Ta girgiza kai ta ce "Bani da waya"
"To ki ara a ta maƙwabta, barinki da wayarsa akwai matsala, haka ya karɓe wayar Viper ya tafi da ita.
Ta cigaba da faÉ—i tashi, wasila ta din ga aiko mata da abinci, sai dai sam jauhar ba ta son hakan.
Aka fara exams, sai dai ba ta iya mayar da hankali wurin yin wani abun kirki, wataran kuÉ—in motar ma gagararta yake yi.
Sai dai tana iya ƙoƙarin ta wurin aro jarumta, da ɓoye damuwarta, idan ta shiga cikin 'yan uwanta ɗalibai.
Sannu a hankali ta fito daga harabar makarantar, ta tarar da yaya saifu.
Murmushi ta yi ta ce "Yaya saifu, kai ne?"
Ya ce "Eh, hau babur ɗin na kai ki gida" cikin murna ta ƙarasa ta rirriƙe shi ta hau, ta ce "Na zo gida sau biyu ban same ka ba".
"Yau ai gani, mu je gidan naki".
Ya ja babur ɗin, ta ce "Allah ya sa ba laifi na yi maka ba, na ganka kamar ranka a ɓace".
Yayi mata shiru, suka ƙarasa gidanta, ta buɗe musu suka shiga.
Ta kawo masa ruwa a jug, dan na rijiya yanzu take sha, ko kuÉ—in sayen ruwa ba ta da shi.
"Waliyiyya"
"Na'am yaya saifu"
"Meyafaru da mijinki?" Tayi shiru ta ƙi magana.
"Ki yi mini bayani ina jinki"
Kawai ta fashe da kuka, yayi mata shiru tayi mai isarta, ya koma kusa da ita ya zuba mata ido ya ce "Jauhar, wani irin zama ki ke yi a gidan nan, na san akwai ƙalubale da ki ke fuskanta a gidanmu, amma atleast ai ko ni kya gayawa, sai ji na yi ana zancen an kama shi da cocaine, a tsakar gida ko baba ba ma bai sani ba, da yaya ki ke rayuwa ke kaɗai? Da yaya ki ke samun abun da za ki ci?"
"Yaya saifu, ni cin abinci ko akasin haka bai dame ni ba, fatana da burina ya fito, ba shi da laifi, ko a yaya yake na yadda shi Allah ya zaɓa mini, ba ya dukana ba ya zagina. Ban san dalilin da ya sanya su mama suka zaɓi na aure shi ba, na karɓi ƙaddarata, na je gidan ai, amma yanayin karɓar da na samu na san ba zan yi nasara ba, kuma ban ma samu baba a gida ba".
"Jauhar, a raba auren nan, ni ban ga alamar za a samu É—a mai ido ba a auren nan ba, rannan fa cewa aka yi sai da ya zo ya tafi da ke, 'yan daba za su saraki, wace irin rayuwa ce haka? Ko khul'i ayi a raba auren nan"
Tayi shiru ta sunkuyar da kanta.
"Yaya ki ka yi shiru? Ko kina son shi ne?"
Ta girgiza masa kai alamar a'a.
"To kin amince a raba auren?" Nan ma ta girgiza kai.
"Ki yi mini magana jauhar, idan kin amince in yi wa baba magana, a raba auren nan"
"Dan Allah kar a raba, ni dai a fito mini da shi dan Allah"
Saifu ya ce "Wai son shi ki ke yi ne?"
Cikin kuka ta ce "Idan aka raba auren za ace mini bazawara"
"To a kanki aka fara? Ba sai ki koma makarantar ki ki yi a tsanake ba?"
Ta girgiza kai ta ce "Dan Allah ni dai yaya saifu kar a kashe mini aure, duk abun da yake yi zai daina a hankali, sharri ake yi masa ba ya ta'amalli da hodar iblis" saifu yayi shiru yana kallon ta, ya fara tunanin any ba son shi take yi ba, ya ma kasa gane me take nufi.
"Shikenan, ƙyale baban ma, yanzu da an yi magana da shi, sai ya gaya wa matansa, wace kotun ake yi masa shari'a? Akwai wani baban abokina, sai na yi wa abokin nawa magana a san abun yi"
Cikin murna ta ce "Na gode sosai yaya, ban san wace kotun ba ce ba, wai ya hana a kai ni, amma akwai lambar abokinsa, da tare muke up and down, ka ga daga nan ma sai mu je na ganshi".
"No, tun da ya ce kar ki je, ba sai kin je ba, duk abun da ake ciki, zan din ga sanar miki, amma ki kwantar da hankalinki dan waliyiyya, tun da kin na ce, ke uwar soyayya Allah ya bar ƙauna, amma wallahi na tsani mijin nan naki"
Ta ce "Dan Allah ka daina faÉ—a, ba zan ji daÉ—i ba, a din ga yi mana addu'a, ba na jin daÉ—i idan aka aibata shi"
Ya ce "Iyee lallai waliyiyya baki ya buÉ—e, ki na so dai ki gaya mini ki na son mijinki maybe ma fiye da ni, to wallahi ki fi so na a kansa"
Ta ɓoye fuskarta tana dariya ta ce "Wallahi yaya tausayi yake bani kawai, idan aka raba auren nan, akwai damuwa, kuma ina saka ran komai zai zama tarihi in sha Allah"
Ya ce "Tafi can, kya ma faÉ—i gaskiya, kuma ko ba yau ba, kar ki sake wani ma ya san na shiga maganar nan, ai mu na da alfarma shige-shige yayi mana rana" jauhar tayi murmushi, ya bata kuÉ—i ya tafi.
Kusan sati ba ta ƙara jin ɗuriyar saifu ba, ga babu su walid balle ta ji wani abu daga gare su, sai da ta ari wayar wasila, ta kira walid ta ce ya zo ya karɓi kayan da zai kai wa master.
Ta saya masa maggi, mai, da sauran ɗan abun da ba a rasa ba, da prisoner zai buƙata.
Ya karɓa tare da ƙara bata haƙuri, da ba ta tabbacin, yana nan suna ƙoƙarin fitar da Mijinta.
Saifu ya sake komawa makaranta ya sameta, cikin murna ta hau tambayar sa, ya ake ciki?.
"Ke mijinki abun da aka yi masa shiri ne kawai, na bibiyi abun ni da abokina, zaki sha mamaki idan na gaya miki an yi wani mugun sara a kan gaɓa, amma ba zan gaya miki ba, in je zaƙin soyayya ya ja ki ki gaya masa ba idan ya fito, ki haddasa husuma, baban abokin nawa yayi magana, sun ce ayi haƙuri ya ƙarasa wata ɗaya, kotu za ta wanke shi ya fito, ashirin da biyu ga watan gobe za a sake shi"
"Wayyo Allah, yaya saifu kusan watanni uku fa kenan zai yi a prison?"
"Au baki gode ba kenan?"
Jiki a sanyaye ta ce "A'a na gode sosai yayana, Ubangiji Allah ya saka maka da gidan aljanna, to zaka kai ni na ganshi?"
Ya ce "Amin ya rabb, yana prison na ciki gari, kuma ban ce ki je ba, kar ki kuskura ki je, kin ji na gaya miki"
"Amma yaya meyasa?"
Saifu ya ce "Saboda haka na ce miki, kuma ke ma kin ce ya ce kar ki je, kar kuma gaya wa wani gashi zai fito shi ma bai sani ba".
Jauhar ta ce "To shikenan, na gode Allah ya saka maka da mafificin alkhairi"
"Amin ki koma gida, ki cigaba da exams É—inki, idan da wani abu, ki neme ni a waya, kar ma ki sake zuwa gidan nan da wani batu a kan aurenki, tun da ki na son abun ki ki yi zamanki"
Tayi murmushi ta ce "Ban san menene son ba dai yaya, ban san me ake ji ba, da farko dai na san ina jin tsoronsa sosai, amma yanzu kuma tausayin sa nake ji"
Yayi murmushi ya ce "Ga kuÉ—in mota, ki sauka lafiya, yau ba zan je gidanki ba"
Ta karɓa cikin murna tayi masa godiya, ta tafi gida.
Ta ji sanyi a ranta jin cewar zai fito, sai dai tana cikin damuwa na rashin sanin halin da yake ciki, ya ji sauƙi ko kuwa, yana samun abinci ko kuwa?"
"Please count me out of this please, haka kurum na je fito da shi, 'yan adawa su sami na yi mini yarfe, ace nima safararta nake yi? Dama dai wani rashin jin yayi ba wannan ba, ni fa dama Saboda aikina na cin zaɓe siyasa dole sai da irinsu, shiyasa nake fito da shi, amma ban da haka meye haɗina da shi, zan nemi wani ya cigaba da yi mini ayyukana ni babu ruwana"
P.A ya ce "A'a honorable, wani kaya fa sai amale, wallahi ba kowane matashi ne yake da ƙwarin da yake da shi ba, kar ka yar da shi wani ya ɗaka"
"Ka san dai yanzu bana gari ko, dan Allah ka bar ni, ni yanzu lissafin siyasata na saka a gaba, idan ina buƙatar sa a gaba, na fito da shi" ya kashe wayarsa.
P.A ya kalli Jauhar da jikinta yayi sanyi, mamaki ya cika mata kai da zuciya, wato yana amfani da jini da lafiyar Al'amin ne kawai dan cimma nasa burin, abun ya bata mamaki sosai da sosai.
"Madam, kin ji abinda honorable ya ce, amma ki yi haƙuri zuwa ya dawo, mu gani zan cigaba da lallaɓa shi, kar ki damu da abubuwan da ya faɗa, kansa ne ya ɗauki zafi, amma shi da Aminu ba ta ɓaci, in dai wannan harkar ce, ba shi da sama shi".
Ba ta ce masa uffan ba, ta tashi ta fita, yanayin yadda ta fito ne, ya tabbatar masa da akwia matsala.
Ya ce "Yaya? Wani abun yayi miki ko maganar banza yayi miki, na shiga na ci ubansa"
Ta girgiza masa kai alamar a a.
"To meyafaru?"
"Honorable ɗin ya ce babu ruwansa, ba zai shiga maganar ba saboda kar sunansa ya ɓaci" tayi maganar hawaye yana gangarowa daga idanunta.
Walid ya yi shiru, tare da jinjina kai ya ce "Shikenan, bakomai mu tafi"
Haka suka tafi duk jiki a sanyaye, ta ce "Yanzu shikenan babu abun da za ayi? Haka zai cigaba da zama?"
"A'a zai fito, haryanzu ba a gama shari'ar ba ma, dole za a nemi wata hanyar".
Jauhar ta ce "To shikenan, dan Allah ranar juma'a ka zo ka karɓi kayan da na tara, sai ka kai masa".
Walid ya ce "Shikenan, in sha Allah, amma kar ki je ki saka damuwa a ranki, idan da wata matsala, ki kira ni a wayarki"
Ta girgiza kai ta ce "Bani da waya"
"To ki ara a ta maƙwabta, barinki da wayarsa akwai matsala, haka ya karɓe wayar Viper ya tafi da ita.
Ta cigaba da faÉ—i tashi, wasila ta din ga aiko mata da abinci, sai dai sam jauhar ba ta son hakan.
Aka fara exams, sai dai ba ta iya mayar da hankali wurin yin wani abun kirki, wataran kuÉ—in motar ma gagararta yake yi.
Sai dai tana iya ƙoƙarin ta wurin aro jarumta, da ɓoye damuwarta, idan ta shiga cikin 'yan uwanta ɗalibai.
Sannu a hankali ta fito daga harabar makarantar, ta tarar da yaya saifu.
Murmushi ta yi ta ce "Yaya saifu, kai ne?"
Ya ce "Eh, hau babur ɗin na kai ki gida" cikin murna ta ƙarasa ta rirriƙe shi ta hau, ta ce "Na zo gida sau biyu ban same ka ba".
"Yau ai gani, mu je gidan naki".
Ya ja babur ɗin, ta ce "Allah ya sa ba laifi na yi maka ba, na ganka kamar ranka a ɓace".
Yayi mata shiru, suka ƙarasa gidanta, ta buɗe musu suka shiga.
Ta kawo masa ruwa a jug, dan na rijiya yanzu take sha, ko kuÉ—in sayen ruwa ba ta da shi.
"Waliyiyya"
"Na'am yaya saifu"
"Meyafaru da mijinki?" Tayi shiru ta ƙi magana.
"Ki yi mini bayani ina jinki"
Kawai ta fashe da kuka, yayi mata shiru tayi mai isarta, ya koma kusa da ita ya zuba mata ido ya ce "Jauhar, wani irin zama ki ke yi a gidan nan, na san akwai ƙalubale da ki ke fuskanta a gidanmu, amma atleast ai ko ni kya gayawa, sai ji na yi ana zancen an kama shi da cocaine, a tsakar gida ko baba ba ma bai sani ba, da yaya ki ke rayuwa ke kaɗai? Da yaya ki ke samun abun da za ki ci?"
"Yaya saifu, ni cin abinci ko akasin haka bai dame ni ba, fatana da burina ya fito, ba shi da laifi, ko a yaya yake na yadda shi Allah ya zaɓa mini, ba ya dukana ba ya zagina. Ban san dalilin da ya sanya su mama suka zaɓi na aure shi ba, na karɓi ƙaddarata, na je gidan ai, amma yanayin karɓar da na samu na san ba zan yi nasara ba, kuma ban ma samu baba a gida ba".
"Jauhar, a raba auren nan, ni ban ga alamar za a samu É—a mai ido ba a auren nan ba, rannan fa cewa aka yi sai da ya zo ya tafi da ke, 'yan daba za su saraki, wace irin rayuwa ce haka? Ko khul'i ayi a raba auren nan"
Tayi shiru ta sunkuyar da kanta.
"Yaya ki ka yi shiru? Ko kina son shi ne?"
Ta girgiza masa kai alamar a'a.
"To kin amince a raba auren?" Nan ma ta girgiza kai.
"Ki yi mini magana jauhar, idan kin amince in yi wa baba magana, a raba auren nan"
"Dan Allah kar a raba, ni dai a fito mini da shi dan Allah"
Saifu ya ce "Wai son shi ki ke yi ne?"
Cikin kuka ta ce "Idan aka raba auren za ace mini bazawara"
"To a kanki aka fara? Ba sai ki koma makarantar ki ki yi a tsanake ba?"
Ta girgiza kai ta ce "Dan Allah ni dai yaya saifu kar a kashe mini aure, duk abun da yake yi zai daina a hankali, sharri ake yi masa ba ya ta'amalli da hodar iblis" saifu yayi shiru yana kallon ta, ya fara tunanin any ba son shi take yi ba, ya ma kasa gane me take nufi.
"Shikenan, ƙyale baban ma, yanzu da an yi magana da shi, sai ya gaya wa matansa, wace kotun ake yi masa shari'a? Akwai wani baban abokina, sai na yi wa abokin nawa magana a san abun yi"
Cikin murna ta ce "Na gode sosai yaya, ban san wace kotun ba ce ba, wai ya hana a kai ni, amma akwai lambar abokinsa, da tare muke up and down, ka ga daga nan ma sai mu je na ganshi".
"No, tun da ya ce kar ki je, ba sai kin je ba, duk abun da ake ciki, zan din ga sanar miki, amma ki kwantar da hankalinki dan waliyiyya, tun da kin na ce, ke uwar soyayya Allah ya bar ƙauna, amma wallahi na tsani mijin nan naki"
Ta ce "Dan Allah ka daina faÉ—a, ba zan ji daÉ—i ba, a din ga yi mana addu'a, ba na jin daÉ—i idan aka aibata shi"
Ya ce "Iyee lallai waliyiyya baki ya buÉ—e, ki na so dai ki gaya mini ki na son mijinki maybe ma fiye da ni, to wallahi ki fi so na a kansa"
Ta ɓoye fuskarta tana dariya ta ce "Wallahi yaya tausayi yake bani kawai, idan aka raba auren nan, akwai damuwa, kuma ina saka ran komai zai zama tarihi in sha Allah"
Ya ce "Tafi can, kya ma faÉ—i gaskiya, kuma ko ba yau ba, kar ki sake wani ma ya san na shiga maganar nan, ai mu na da alfarma shige-shige yayi mana rana" jauhar tayi murmushi, ya bata kuÉ—i ya tafi.
Kusan sati ba ta ƙara jin ɗuriyar saifu ba, ga babu su walid balle ta ji wani abu daga gare su, sai da ta ari wayar wasila, ta kira walid ta ce ya zo ya karɓi kayan da zai kai wa master.
Ta saya masa maggi, mai, da sauran ɗan abun da ba a rasa ba, da prisoner zai buƙata.
Ya karɓa tare da ƙara bata haƙuri, da ba ta tabbacin, yana nan suna ƙoƙarin fitar da Mijinta.
Saifu ya sake komawa makaranta ya sameta, cikin murna ta hau tambayar sa, ya ake ciki?.
"Ke mijinki abun da aka yi masa shiri ne kawai, na bibiyi abun ni da abokina, zaki sha mamaki idan na gaya miki an yi wani mugun sara a kan gaɓa, amma ba zan gaya miki ba, in je zaƙin soyayya ya ja ki ki gaya masa ba idan ya fito, ki haddasa husuma, baban abokin nawa yayi magana, sun ce ayi haƙuri ya ƙarasa wata ɗaya, kotu za ta wanke shi ya fito, ashirin da biyu ga watan gobe za a sake shi"
"Wayyo Allah, yaya saifu kusan watanni uku fa kenan zai yi a prison?"
"Au baki gode ba kenan?"
Jiki a sanyaye ta ce "A'a na gode sosai yayana, Ubangiji Allah ya saka maka da gidan aljanna, to zaka kai ni na ganshi?"
Ya ce "Amin ya rabb, yana prison na ciki gari, kuma ban ce ki je ba, kar ki kuskura ki je, kin ji na gaya miki"
"Amma yaya meyasa?"
Saifu ya ce "Saboda haka na ce miki, kuma ke ma kin ce ya ce kar ki je, kar kuma gaya wa wani gashi zai fito shi ma bai sani ba".
Jauhar ta ce "To shikenan, na gode Allah ya saka maka da mafificin alkhairi"
"Amin ki koma gida, ki cigaba da exams É—inki, idan da wani abu, ki neme ni a waya, kar ma ki sake zuwa gidan nan da wani batu a kan aurenki, tun da ki na son abun ki ki yi zamanki"
Tayi murmushi ta ce "Ban san menene son ba dai yaya, ban san me ake ji ba, da farko dai na san ina jin tsoronsa sosai, amma yanzu kuma tausayin sa nake ji"
Yayi murmushi ya ce "Ga kuÉ—in mota, ki sauka lafiya, yau ba zan je gidanki ba"
Ta karɓa cikin murna tayi masa godiya, ta tafi gida.
Ta ji sanyi a ranta jin cewar zai fito, sai dai tana cikin damuwa na rashin sanin halin da yake ciki, ya ji sauƙi ko kuwa, yana samun abinci ko kuwa?"