← Book details Bibiyata Yake Yi Part Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 69 OF 106

Sashe 69

Bibiyata Yake Yi Part Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sassafe natashi na shirya kayan makaranta muka fice da Maryam zamu bi gidan su ta saka uniform tukunna. yaya Habibu yakaimu bayan gaisawa da mukayi da Ummi Maryam ta shirya taÉ—auki Bag É—inta muka wuce school. Gabaki É—aya zaman school nayishine da tunanin Hammood cike araina inata duba wayata ko zai kira ko message amma babu ko É—aya. Dake friday ne bamu daÉ—e a school É—inba muka dawo gida. Maryam tawuce gidansu Nima nawuce gida. Mama tanata jira taji ko zanyi mata magana amma banyiba haka ta zubamin ido kawai.

ƙarfe biyu Aysha taji Hamma shiru Baizo ba baikuma ko yimata waya yace ya yarda a ɗauko Marmeeyn ba ko maryam ya kawo mata idan bai yarda da Marmeeyn ba dan tasan idan jiya ya iya yimata haƙuri to yau bazaiyiba. Tun kafin dare yayi gara ta sake masa tuni.
ÆŠaukan wayarta tayi tashiga contact tayi dialing number É—insa bugu biyu ya É—auka. Bayan tayi sallama ya amsa.

"Hamma najika shiru bakace komai akan É—aukan Marmeeyyn ba"

"Kishirya zanzo muje gidan sai muyi musu magana" tayi murna sosai dan zata jefi tsuntsu uku da dutse ɗaya nafarko zata sanya Marmeeyy tasan irin muhimmanci da mace take dashi gun mijinta na biyu dole ta nemo hanyar cirewa Hamma shima Marmeeyyn aransa na uku zata samu sauƙi daga jarabar Hamma.

Alokacin tatashi ta shirya cikin doguwar rigar lace ta sanya turare da Humra ta ɗauko jaka da gyale harda takalmi ta kima ɗaurin ƙwali tazauna tana jiransa. Har tagaji ta sunce ɗaurin baizo ba aka kira la'asar tatashi tayi sallah tana zaune taji shugowarsa. Ta turo baki yana ganinta yagane abunda take nufi amma ya share yazo ya zauna ƙamshin turaren da ta sanya yana fisgarsa.

"Hamma amma fa cemin kayi na shirya gaka nan zuwa shine bakazoba sai yanzu?" tafaɗa a shagwaɓe. Ya dubeta da tana shagwaɓar tayi kyau amma sai dai ta nemi data zaune tsaye. Kawarda kansa yayi gefe bayaso daga yau yafara saɓawa maganarsa na cewar zai barta ta huta"

"Eh nace ki shirya amma ai bance miki yanzu zanzo ba. Kitashi ki canja kayan turaren jikinki yayi ƙamshi dayawa yana sauƙarmin da kasala karki saka turare" miƙewa tayi jin abunda yake faɗa da sauri tayi ɗaki saida tayi wanka ta wanke turaren sannan ta canja kayan ta saka sabo dall wanda sam babu ƙamshi a jikinsa saina sabuntar kaya. Ta shirya tafito tsaff da ita a yanda tabarshi ana ta sameshi ta ƙarasa kusa dashi.

"Hamma na fito muje" ya buɗe idanuwansa a kasalance ya dubeta harsun canja kala a hankali ya sanya hannu ya jawota tafaɗo jikinsa. Dasauri tafara ƙoƙarin ƙwacewa zuciyarta na bugu da ƙarfi.

"Menene hakan Hamma? Dan Allah kabari kaga fa banda lafiya" tafaɗa tana fashewa da kuka. Dan tuna irin azabarda takesha idan ya riƙeta.

"Shhhss is okay, ba wani da zafi zanyi miki ba kuma iya na yanzu ne kaɗai ba gashi zanje na ɗauko miki Marmeeyy ba sai kwana biyu kafin tatafi ke bazakiji tausayina ba tsawon lokacin da zan ɗauka batareda keba? Haka ya lallameta da baki da sakar masa jikinda saida ya sanyata danasanin tausaya masa da tayi. Yamma tayi liƙis amma haka ya ɗauketa ya kaita a ƙofar gida ya ajiye ta yace idan zai dawo ɗaukarta zai shiga tafara yimusu maganar amma kafin yazo. ɗaukin zuwa gidane kawai ya sanyata fita amma idanba haka ba babu abunda zaisa tafita a yanda takejin jikinta. Tunda tayi arba da gida taji shawararta ta canja yanzu zama zatayi agida har sai ta warke"

A hankali ta shiga har cikin gida tana zuwa tawuce É—akin Mama kai tsaye ana shirin yin magrib Mama taji shigowar Aysha.

"A'a wa nake gani kamar Aysha? Ke waya faÉ—a miki ana fita aure sati guda? Matsashi kikayi kenan ya kawoki?" Aysha taturo baki.

"Mama ai dai zaki bari na zauna kafin kifara min faÉ—a natafi gida kwana 6 bananan amma bakuyi kewata ba ina zuwa za'a faramin faÉ—a" tafaÉ—a tana tura baki.

"Toh ai abunne aysha baiyi tsari ba sati É—aya fa? Aidan kinsan Babanku bamai faÉ—a bane ba da sai yayi miki faÉ—a amma koshi yaji bazaiji daÉ—i ba"

"Nifa Mama banda lafiyane nazo gida"

"Subhanallahi toh Allah ya sauwake" Mama taja baki tayi shiru dan batason ƙarin wani zancen da za'a sakata jin kunya. Ta gaisheda Mama. mama ta amsa tana tambayar jiki tace.

"Dasauki Mama amma wallh ni kinganni yanzu nadawo gida kenan saina warke na koma"

"Zanga yanda za'ayi haka ta yiwu"

"Allah mama dagaske nake" toh kawai Mama tace ganin zancen bana masu hankali bane. Nikuwa bansan da zuwanta ba ina wajan Mummy muda Anty fadeelah acan mukayi sallah. Itama Aysha a É—akin Mama tayi sallah saida Mama taga batada niyyar fita sannan tace.

"Aysha tashi kije ki gaida mutanen Sauran mutanne gidan"

"Nasan yanzu Baba bai dawo ba sai yayi isha'i Anty ce idan nafita gaida Baba saimu gaisa wallh banjin daÉ—ine banso nayi tafiya biyu"

"Allah yasauwake amma ai Mummynku ma tananan sai kije ki gaisheta itama"

"Dama Mummy tana gari? Rabona da waya da ita tun washe garin ranarda aka ƙwantarda ni a asibiti ni naɗaukama tatafi dannasan bata wasa da business ɗinta dan yafi mata komai." Dan ƙwalo Mama tayi mata.

" ungo naki Mummyn naku kike faɗawa Haka? Toh ki tashi kije wajanta kuma Mummynku ta dawo nan da zama kenan" Zaro ido tayi da Mamaki abunda bata taɓa zato ba tayi murna sosai harta manta dawani rashin lafiya kai tsaye tatashi tayi ɗakin Mummy. Sallama kawai tayi tafaɗa ciki. Bulum kawai mukaji shigowarta kamar wata wlkiya.

"Mummy wai dagaske kin dawo kenan? Bazaki koma abuja ba?

"Waya faÉ—a miki haka?"

"Mama ce ta faÉ—amin"

"Mamarku ta faÉ—a miki bayan kinji bakinta shine kuma kike sake tambaya ta?"

"Uhmm mummy abunne wallh yabani Mamaki bantaɓa zaton zaki dawo nan ba naɗauka kin zauna a abuja kenan"

"Mamaki ma yabaki bakiji daÉ—i ba kenan? Tukunna ma waye ya kawoki? Waya ce miki ana zuwa gida daga aure biki ko sati baiyiba? Tsabar rashin hankali ki kamo hanya ki taho gida?" bata kaiga cewa akomai ba Yaya Ahmad yayi sallama. Muka amsa Mummy tabashi izinin shugowa. Da mamaki yake kallon Aysha.

"Kekuma me kikeyi a gida?"

"Banda lafiya nefa shine ya kawoni gida" tafaÉ—a tana tura baki.

"Allah ya kyauta" kawai mummy tace. Muka gaisarda Yaya Ahmad ya amsa sannan ya zauna.

"Mummy yaushe zaki tafi ne?" da mamaki na kalli Mummy ina mamakin ashe bata gayawa Ya Ahmad tadawo kenan ba.

"Ahmad korata ma kakeyi? Cikinku Marmeeyy ce kawai ta roƙi nazauna karna tafi. Fadeela kanma bansan stand ɗinta ba san bata taɓa cemin komai ba ga Aysha wai Mamaki takeyi Akan taji nazo kenan bazan tafi ba"

"Wai dagaske Mummy bazaki koma ba?"

"A'a ƙarya" tafaɗa a daƙile yaya Ahmad na ganin haka ya kama kansa dan yasan ba komai Mummy take ɗaukana ysnxu cemata zallan wai dagaske da yayi saita ɗauki hakan raini"

"Toh hakan yayi kyau Mummy Allah ya kaÉ—e fitina ya zaunar daku lafiya gabaki É—aya"

"Amin ta amsa"

"Ko Yaushe zaku fara buÉ—emin cikinku matsayina na mahaifiyarku?" sungane abunfa take Nufi dan haka anty fadeelah tayi saurin faÉ—in.

"Wallh Mummy munyi murna sosai ni murnar cema ta hanani cewa komai mungode da kika dawo zaki zauna damu duk da babu abunda muka nema wajan Mama muka rasa abunda baƙya mana ma tanayi mana amma dole muna buƙatarki kusa damu Allah yasaka miki da alkhairi" Amin muka amsa dukanmu.

"Nimafa murnar ce tasani shugowa da sauri da Mama ta faÉ—amin naji daÉ—i sosai"

"Toh Alhamdulillhi tunda kunji daɗi Allah yayi muku albarka muduka muka amsa. Aysha tafito waje ta kira Hamma yana ɗauka ta marairaice murya akan zazzaɓi ya rufeta batada lafiya yabarta taƙwana kawai gobe sai yazo sutafi. Jin muryarsa ysa yayi tunanin tana shan wahala sosai. Bai kawo komai aransa da tace batajin daɗi ba dan yaga yanayinda tafita yayi mata Allah ya sauwaks sannan sukayu sallama.

Cousins É—in su Anty fadeelah tunda nadawo daga school ban gansu ba kuma da alamu ba tafiya sukayi ba amma sunbar gidan. Ban danu sana tambayi yanda sukaje ba san inada cikinsu dama."

"Palourn Baba muka dawo gabaki ɗayanmu dayake Baba ya dawo daga masallaci. Baba saida yayi magana dayaga Aysha haka ta marairaice batada lafiya ta nemi kujera ta ƙwanta tayi luff wai zazzaɓi takeji tanaso idan tatashi cewa bazata tafi ba ayi saurin barinta.

Anan muke zaune munata hira har Baba yace na shirya zanyi baƙo dan sunyi waya yace masa gobe zai koma. Na miƙe nakoma ɗakin Mama nayi wanka na shirya. Ina zaman jiran isowar Hammood."

Kuyi hakuri kwana biyu haka zakuna ganin typing É—in sai ahankali test nake tayi ga exams dole nayi karatu nabi komai saisa-saisa.

PAID BOOK

Littafin BIBIYATA YAKEYI (WAYE SHI) na kudine ki biya Naira Dari uku 300 Domin kisha karatunki hankaki kwance,
account 0003075326
Zainab  m Bawa JAIZ BANK Ko katin MTN ta wannna lambar 08161146563 shaidar biya Ta 08161146563 da zarar kin biya Hankli kwance  zaki samu damar karanta wannan labarin ku shigo daga ciki kar ayi babu ku domin wannan
tafiyace wanda salonta da tsarinta ya bambamta da ko wace irin tafiya karki bari ayi babu ke."
Idan Kuma kina bukatar Aringa tura miki pc kullum Dari hudu 400 kacal zaki biya batareda an Sanyaki cikin group ba zaizo ya sameki har yanda kike."

ZAYNAB ALABURA
Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun bankina Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya

Wajajan ƙarfe tara Baba yadubi Aysha.

"Aysha dare yayi shi mijin naki bazaizo kutafi bane? Naga bakyajin daÉ—i basai kutafi dawuri ba?" ta maraimarice murya.

"Baba munyi waya dashi zan ƙwana anan kawai dan yanzuma zazzaɓi ke rufata"

"A'a aysha ina kika taɓajin anyi haka? Aure ƙwana shida kice zaki ƙwana gida?"

"Baba ai dolece tasaka wallh banajin daɗi sosai gara na zauna anan kawai Zuwa gobe saimu tafi" baƙin cikine ya kama Mumny ita sam batason sanyin halin Baba ta amshe maganar.
Chapter 69 · 0% Book details