← Book details Waya San Gobe Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 66 OF 84

Sashe 66

Waya San Gobe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

wa junansu A hankali ya soma motsa labbansa da yakejin suna mishi nauyi still idanun nasa na cikin nata yace "please,tell me kina sina baby nah"ta dan lumshe idanun nata tana jin wani shauqi cikin zuciya da gangar jikinta sannan ta sake budesu ta watsa su cikin idon aliyun "bau wasu kalmomi da zasu iya bayyana abinda nake ji cikin zuciyata, I love you more than I did yesterday,and I will love you more tomorrow than I do today,kai na fara so kuma kai zanci gaba da so har qarshen rayuwata,inaji a jikina an halicceni ne kawai saboda kai" jinsa yake tamkar yana yawo a sararin samaniya,yana jin tamakar su dawwama a gun tana ci gaba da bayyana masa irin qaunar da take masa da sweet voice dinta Karo na farko da fadeelah taga dariya mai cakude da murmushi cike da nishadi kwance bisa fuskar aliyyun,har yanzu idanun nasu na manne dana juna "is what I see in your eyes true or the mirror?"gyada kai tayi tana mai bashi tabbaci "its true,da gaskene miji na" "really?" Ya sake tambayarta "yes its real"ta amsa masa tana sake bashi tabbaci,hannayenta ya kamo ya matse cikin nasa tafin hannun,"please ina neman alfarma guda daya" gyada kai tayi alamun tana saurarensa,ya sake matsowa kusa da itan har suna shaqar numfashin juna yana murza tattausan tafin hannunta "ina roqonki fadeelah if u reprimand me hug me and give me bliss and let it to be a loving touch,please na roqeki kada ki sake yin nisa da ni,kada ki kuma barina,kada ki kuma raba ruhina da naki,kimin alqawari fadeelah na,are you promised to do it?"ta gyada kai tana murmushi "yes I promise you" "good and I promise you too....I will never do it again,all I want is to see you smile forever not just for a while...." ya rungumeta tsam yana fadin"am sorry I will never hurt you again" "ya wuce wallahi ya wuce,Allah ma muna masa laifi ya yafe mana" Tsawon mintina yana rungume da ita yaqi sakinta,ita din ma dadin hakan take ji sosai,don ba zata yaudari kanta ba sosai tayi missing soft skin nashi,tayi missing scent nashi masu dadi,kai komai nashi ma tayi missing dinsa,sai gashi lokaci guda Allah ya maido mata da shi da kuma abunda bata taba tsammanin ba ma,duk da ta sani addu'a bata faduwa qasa banza dama,kuma lallai wani jinkirin alkhairi ne,sai da taga lokaci na qoqarin qwace musu gashi bai da niyyar sakinta bare ya tada motar su tafi "lokaci na tafiya fa,kada momy taga ban dawo on time ba"ya dagota yana kallonta"sai kice mata kin sha'afa ne kina tare da lovely husband dinki"ta rufe fuskarta da tafin hannunta "momin zan cema haka?"ya dage girarsa "yes kinga sai tace tattara kayanki kibi mijinki,kinga fine komai yayi kyau ko?",sai ta maida jikinta kan kujerarta tana murmushi qasa qasa,qamshin turarensa da ya manne a mayafinta yana sake yi mata dadi tamkar yau ta sanshi Kusan sai da suka tsaya sau kusan uku kafin sukai gida,kallonta yake ne yaqi maida kanshi yayi tuqin,idan tayi masa qorafin hakan sai ya yace "gaskiya gaskiya bazai iya tuqi baya kallonta ba,saidai a haqura da tuqin idan ya gama kallon nata sa tafi,lokacin da suka isa gida tuni anata tada iqama,tana qoqarin ficewa daga motar ya kamo hannayenta,ta dan fiddo da idanunta tana kallonsa,ta shagwabe fuska kamar zata yi masa kuka " please ka sakemin hannu muna cikim gida ne fa yanzun,it can be possible wani ya fito ya gan mu a....." kanta qarasa tuni ya janyota jikinsa daidai lokacin uncle abba ya fito daga cikin gidan hannunsa dauke da carbi da alamu masallaci zashi Sarai ya gansu amma sai ya dauke kai tamkar bai kula da su agun ba,farinciki yaji sosai cikin zuciyarsa "alhamdulillah"kawai yaje fadi cikin ransa,bisa dukkan alamu sun sasanta kansu kenan,yanzu yake ji a zuciyarsa zai iya maida fadilan gidan aliyyu,don duka alamu sun nuna na qauna da soyayyar da suke ma juna,fadila ce ta soma ganin abban lokacin har ya basu baya,ta zare jikinta da sauri tana gyara yafen mayafinta zuciyarta na bugawa tace "innalillahi" aliyu ya kalleta"lafiya baby?" Uncle abba ta nuna masa da yatsa tuni idanunta suka cicciko da qwalla "ya ganmu wallahi,sai da nace ka bari ka bari fa" Dariya ya saki cikin nishadi "to mene ne?,kinga addu'ata ta karbu kenan,kuma ma baby naga da mijinki ya ganki fa mene na rudewa har irin haka?" Ya jawo hannunta yana goge mata qwallar da ta soma gangaro mata "calm down my unique,don't cry again,kin gama kuka a duniya ai matuqar ina tare da ke,I will never let your tears to fall down again.....muje ma raka ki ciki"sai taga tunda abba ma ya riga ya gansu a dazun don rakata ma cikin gida ba komai bane,abun kunyar dai an riga an gama tafka shi,tayi tayi da shi ya bata jakarta ta riqe yaqi yace sai ya kaita har ciki,sai da yace idan ma ta fiya matsawa zai goyata ne ya kaita har cikin gidan,tasan kadan ne daga aikinsa,tilas ta bar masa tayi gaba yana take mata baya...... *Mrs muhammad ce* [10/16, 2:15 PM] Salma *WA YASAN GOBE?....* *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* *PART 3* Ai kuwa sukayi kyakkyawan gani cikin parlour,momi ce da iftihal dukkansu suna zaune kan kujera sanye da hijabi da alama sallah suka idar,karatun qur'ani iftihal keyi da ka momi na gyara mata kura kurenta,kallo momin ta bisu da shi daga bisani sai kuma ta dauke kanta tamkar bata gansu ba,ya miqawa fadila jakarta da take ta Allah Allah ta bar falon kunya gaba daya ta rufeta,gogan harda hadawa da hannunta lokacin da zai miqa matan,ta zame hannun nata da sauri ta haye sama inda dakinsu yake,ya wani bita da kallo ko kunya baiji ba,sai da ta qare hawa sannan ya janye idonsa ya juya da niyyar gaida momi Ashe idanunta na kansa take suka hada ido,sai yaji wata kunya ta kamashi,yasa tsinin key din motarsa yana sosa tsakiyar kansa irin najin kunya,yakoma gefe ya tsugunna yana gaidata yayin da tuni iftihal tayo qaura gurinsa,maimakon momin ta amsa sai tace "rasa kunya beran tanka,tashi ka bani guri,kada na kuma ganin kana takura mata daga yau,na gaya maka ka qyaleta tayi hukunci da qashin kanta,idan ba haka ba tamu ce ni da kai"ya miqe yana murmushi lokacin da yake maida iftihal kan kujerar kusa da momin,abinka da wanda bai iya qarya ba sai yace "momi ba takura mata nake ba,ai tama gama yanke hukuncin,mun gama magana da ita momi"baki sake ta bishi da kallo lokacin da ga fara tattaki zai bar falon "iye?,me kace?" "A'ah momi bari inje nayi sallah"shima ya fada yana waiwayo wa gami da sakin dariya wa momin har ta fice "Ja'iri ka maida ni kakar ka ko?" "Momi ai dama kakarsa ce ke"inji iftihal dake faman wasa da bezar hijabinta,duk sai suka bata dariya 'yar da uban,cikin zuciyarta tqna addu'ar Allah ya daidaita ya sake tsakaninsu Kowa ya hallara a dining har aliyyu da yaqi tafiya amma qememe fadila taqi saukowa,ita kam ba zata iya ba,bala'in kunyarsu abban take ji don aliyyu ya gama kunya tata,kuma ta sani ko da ta sauko din tunda aliyun na gun ta tabbata sai ya sake kunyatata kafin a tashi,haka abban yace a qyaleta don yasan me take yiwa kunyar,sam sai yaji abincin bai masa dadi don mafi rinjayen zaman cin abincin nasa saboda ita ne,suna tsaka da cin abincin ya soma tari kamar ya qware,sai yaqi daukan ruwan dake kan table din yayi hanyar kitchen su abba na masu sannu,ganin idon kowa bai kanshi sai kawai ya haye matattakalar sadaf sadaf yayi sama,momin ce ta soma ganoshi ta dan tabo uncle abba yadda su sumayya ba zasu gani ba ta nuna masa aliyyun,dariya uncle abban ya saki shida momin duka, Tana zaune dirshan tsakiyar gadon,gabanta system ce a bude tana faman aiki cikinta,doguwar rigar yellow din material mai santsi ce a jikinta,mai tankakken hannu ne dinkin ,babu abinda ta shafa illa man lebe da ya qarawa lips dinta taushi,sai jikinta dake tashin qamshin turaren asaal,kyakkaywan gashinta baqi sidik mai tsawo da qyalli yasha gayara ta tajeshi ta daure shi da qaramin ribbon yellow ya sauka gadon bayanta yana reto,hundred percent hankalinta na kan system din,alewar mints ce a bakinta tana tsotsa a hankali,sai da ya gama qare mata kallo iya son ranshi "unique lady"ya fada cikin ransa,komai nata mai aji ne,yanayin zaman nata bisa gadon sai ya zamewa aliyyu abun sha'awa,lallabawa yayi ya haye gadon ta bayanta,sai jinta kawai tayi rungume jikin mutum,a dan firgice ta waiwayo ya manna mata kiss a goshinta tare da sakin murmushi"me yasa kika qi saukowa kici abinci bayan kin sani bazan iya tafiya ba tare da na kalli wannan kyakkyawar fuskar taki ba"ya qarashe maganar yana shafa gashinta da ya qayatar da shi Zumburo baki tayi kamar na shagwababbun yara tana dan kici kicin qwace kanta "haba mana dear dakinsu sumayya ne fa,suna iya shigowa su ganmu"daga hannunwansa yayi yana murmushi "is ok,indai so kike na qyaleki sai idan kin yarda zaki bani hot kisses a matsayin sallamarmu ta yau"sak tayi ta kuma yo kicin kicin da fuska,murmushinsa ya dadu yace "uhm,am waiting dear"nan ma shiru,ya dora kansa saman kafadarta yana leqen fuskarta,saura kadan ya fashe da dariya yadda yaga tana zare idanu,ta gintse dariyar yaba cewa "don't mind dear,if you are not ready kinga sai muyi zaman mu a haka ko?"da sauri ta noqe kafada "no am ready,but.....Please ja rufe idanunka" "ok....ok" ya fadi yana cikata gamida rufe idanun Shiru yaji hadi da qarar qofa,da sauri ya bude Idanun nasa,ta qarasa sa key din qofar toilet tana qyakqyala masa dariya,sai ya harde hannayensa ya zubawa qofar ido fuskar sa qunshe da murmushi"no baby,kin karya agreement,kisses sun qara nukuwa,sun zama double yanzu,ko ki fito ki bani ko in kunce gidan key din yanzun nan in shigo toilet din"dariyarnan tata mai saurin shagaltar da shi taci gaba da yi Sai da taji sukur sukur dinshi jikin qofar sannan ya sata nude qofar da sauri,wayo dama ya mata ba wani gidan muqulli da zai kwance,ya cafkota ta fado jikinsa suna dariya,dariyar tasu ta tsaya lokacin da wayarsa ta soma ruri,ya cirota daga aljihunsa yana dubawa,salima ke kira don itace da girki dama yau zata fita,ya kara a kunnensa,da qorafi ta fara
Chapter 66 · 0% Book details