← Book details Waya San Gobe Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 50 OF 84

Sashe 50

Waya San Gobe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

yake rayawa cikin zuciyarsa,ya sashi cikin wani yanayi nason kasacewa tare da ita fiye da tsammaninsa, Bai damu da dan banzan zafin coffee din ba ya daga kai ya kwankwade tayi saurin amshe cup din ta hada kayan ta maida kitchen ta dawo dauke da cup da gorar ruwa ta dora kan bedside,sai ta tsinci kanta cikin damuwa da cutar yasa duk da bai buda baki yace mata komai game da lalurar tasa ba tasan yana jin jiki,tuni ya kwanta a daya side na gadon ya juya wa ragowat sararin dake bayansa baya A hankali ta haye gadin gami da debe qafafunta ta maida su saman gadon ta rungume gwiwoyinta da hannayenta tana kallon bayansa,tana iya ganin yadda numfashinsa ke sauka a hankali,jikinta ya soma saki bacci ya kamata batasan sadda ta zame ta kwanta ba _*2:30 pm*_ Can cikin tsakiyar baccinta taji ayi mata wani irin mugun riqo,nishi take ji cikin kunnuwanta sama sama dumin numfashin na dukan wuyanta,a firgice ta farka amma ta kasa tashi sabida namijin riqon da yayi mata gaba daya ya cukuikuyeta,da qyar ta samu ta juya tana fuskantarsa,murqususu sosai yake yana hada gumi numfashinsa ke fita da sauri da sauri,tuni ta gigice ganin yadda yana yinsa ya sauya gaba daya,ta tashi ta zauna dirshan hannunsa na riqe da cikinsa idanunsa adamqe daya hannun kuma ita ya zagaye da shi,sosai ta rikice babu abinda yake fadi sai *"ya Allah"* Kimanin minti goma ta shude a haka ta rasa ya zatayi,tunaninta suna da first aid kit a gidan?to koda ma akwai din bazai qyaleta ta tashi ta dauko ba don gaba daya a kanainaye yake ajikinta,dabara ta zo mata da sauri ta miqa hannu ta dauko robar ruwanan da cuo din da dazu ta shigo da su,ta tsiyaya ruwan sannan ta sa bakinta ta tofa masa ayatush shifa ta hada masa da _*allahumma rabbin nas,azhibul ba'asi,wash fi antash shafi,la shifa'u illa shifa'uk,shifa'an la yugadiru saqama*_ Ta dan kalli fuskarsa da tayi ja har yanzu idon ke rufe yana hada gumi "pls can you take it?" Ya dan motsa kadan tasa masa cup din abaki yasha kuwa fiye da rabi Cikin ikon Allah da taimakon ayoyin al qur'ani sai mutsu mutsun da yake ya soma raguwa,riqon tsaurin da yayi mata ya fara sassauta,sai ajiyar zuciya da yakej saki kadan kadan,bata samu sukuni ba sai da taji numfashinsa ya soma daidaita,a hankali jikinsa yayi weak bacci sosai ya daukeshi Ta saki ajiyar zuciya tana kallin irin yanda ya zagayeta da hannunsa,ta tabbatar da a hayyacinsa yake bazai yi hakan ba,gumin fuskarsa har yanzu da saura,tasa lallausan tafin hannunta tana share masa kadan kadan gami da bin fuskarsa da kallo ganin yadda tayi ja alamun wahala,tayi tayi ta janyeshi daga jikinta cikin dabara saidai abun ya faskara yayi mata nauyi ahaka itama baccin yayi awon gaba da ita *THIS IS THE BEGINNING OF*............ *mrs muhammad ce* [10/16, 1:59 PM] Salma *WA YASAN GOBE?...* *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* *PART 2* Yau kam sun makara sosai suka makara don ko sallar daren babu wanda yayi a cikinsu sakamakon bacci da basu samu ba jiya,shi ya fara farkawa ganinta cikin jikinsa ya bashi mamaki,kamar ta san me yake faruwa ta farka itama fuskarsu cikin ta juna,kamar hadin baki da sauri kowa ya janye jikinsa suka miqe a tare,shi ya fara shigewa toilet ita kuma ta shiga na parlour Ta rigashi idarwa tana zaune tana azkar har ya idar,tana zaune har ya kammala nasa addu'o'insa, tadan waiga kadan tana duben gefansa tace "ina kwana" kamar yadda ta saba ba tare da neman amsa ba tunda ta sani ba masawar zaiyi ba don bai taba amsawa din ba,saidai idan yaga dama ya daga mata hannu kawai,saidai yau ga tarin mamakinta karo na farko sai taji ya amsa da "lafiya",ta sake cewa "ya jiki?" Kai ya daga mata,ta tabe baki ta miqe cikin zuciyarta tana cewa"hmm an ma yi yau abun arziqi" tana kallonsa ya sake komawa gado ya duqunqune Bai dade da kwanciya ba wayoyinsa dake gefan gadon suka hau ruri,hannu yasa ya debo su bai daga kiran ba hakanan ba tare da ya duba mai kiran ba ya kashesu duka sannan ya maida su kan side drower hadi da jan bargonsa ya sake rufa Tana kitchen tana hada breakfast tajiyo muryarshi cikin parlour yana amsa waya,saidai muryan tayi qasa sosai alamun bai cikin jin dadinsa don bata iya jin abinda yake cewa,cikin rarraba hankalinta da takeyi ne ta yanke hannunta da wuqar da take rarraba kazar da take so tayi masa pepper chicken ba tare da ta sani ba,wuqar ta shigeta sosai don yankan ba qarami bane,zafin ya ratsa ta har cikin qwaqwalwarta batasan sanda ta saki razananniyar qara ba,jini ne sosai ke zuba ta runtse idonta tana jin azabar yankan Ta bude idonta a hankali suka sauka kansa lokacin da yake shigowa kitchen din cikin sauri,hannun nata da yake digar jini yake bi da kallo,da sauri taga ya ajjiye wayar saman freezer,hannun nata dake digar jini ya riqe yana kalla,wani yarrr fadila ke ji har cikin jininta,shi din ma haka,lallausan tafin hannunta yaso haddasa masa wata sabuwar fitinar cikin jikinsa,yayi saurin sakin tafin hannun nata ya kama tsintsiyar hannun Janta yayi zuwa gaban sink ya kunna famfo ya tara hannun sannan ya barta gaban famfon ya fice da sauri,cikin 'yan sakanni sai gashi dauke da first aid kit,abunda tayi ta tunanin ina yake jiya,spirit ya fito da shi ya janye hannunta daga famfon ya dangwala a auduga ya soma wanke mata kan yankar,zafi sosai take ji yana ci gaba da ratsata ta runtse ido tana dan yin baya da hannun,cak ya tsaya da wanke matan da yake don spirit din baya samun inda yake so,fuskarta da idanunta ke rufe ya zubama ido har wani abu yaso shagaltar da shi Jin shiru ya daina sawa ya sanyata bude ido,idonta ya shiga cikin nasa suka hadu,wani magnet ya hadu da qamshin turarenta yaso rikita aliyyu ya manta da abinda yake,amma sai yaso nuna mazantaka ya dake har da qarfin halin kaurara muryarsa "stop it,idan baki buqata zan hada kayana,kau da kai tayi don bazata iya jurar kallon qwayar idanunsa ba,ya duqar da kai yaci gaba da wanke mata daga bisani ya rufe mata da bandage don kada datti ya dinga shiga Yana maida kayan cikin akwati ta dan motsa labbanta tace "thanks" "for what" ya fadi ba tare da ya dago kai ba bai kuma tsaya da rufe akwatin ba,she became speechless don haka ta zabi yi masa shiru kawai,haka shima bai sake cewa komai ba har ya kammala rufe akwatin ya dauki wayarsa ya fice Da hannu daya ta qarasa aikin don haka kafin ta kammala duk ta jagwalgwale hannun jinin da ya tsayar mata tuni wani ya soma tsatsatsafowa ta bandejin da ya sa mata,sai da ta gama serving dinsa sannan ya ankara da girkinta ashe ta ci gaba da yi,ya dago ya dubeta tana ta faman hurawa yatsan iskar bakinta,baice mata komai ba ya tashi ya sauka a dining din sai gashi dauke da first aid kit,ta zaro ido cikin tsorata tana tunanin mai kuma zai mata yanzu Sosai ya riqe hannunta gam tana qoqarin zamewa saboda azabar yadda yake daye bandage din da ya sa mata dazun zai canza mata sabo,sai da ya cire tas ya sake wanke mata ya saka mata sabo sannan ya maida kayansa ya kwashe mai jinin ya sauka da su Ya dawo ya soma cin abincinsa yana kallonta time to time yadda take ta qwalla "ko da yaushe kina acting kamar baby" hakanan taji ya fada can qasan maqoshinsa,sai da ya kammala cin nasa taga ya ja plate ya zuba mata komai ya tura mata gabanta, "oya" yace hadi da yi mata nuni da plate din da ido fuskarsa a hade,ta dan langabar da kai gefe don bata marmarin cin komai yanzu sai ta tashi a lecture "am ok,na qoshi" kallon nan nasa ya tsareta da shi cikin tsare gida,ta fuskanci hukuntata yake sonyin da ido,tayi saurin janye idanun ta hadi da sake jan plate da cup din gabanta ta soma ci tana yamutsa fuska cikin zuciyarta tana mitar "ya wani tsare mutane sai sunci abinci sai kace wani abbana lokacin da ina gida" "Good haka abban ke miki saboda baki jin magana kan cin abinci ko?"ya fadi yana fuska a hade yana daga girarsa,da sauri ta dago ta kalleshi batasan sanda tea din da ta kurba a bakinta ya dawo ba,batasan ya akayi yaji abinda take fada ba,anya wannan mutumin ba maye bane?, "am talking to you kin qwalalomin idanunkin nan masu girman tsiya"(lol aliyyu ) ya fada cikin dan daga murya,kai kawai take girgizawa don babu bakin cewa wani abu,minti biyu tsakani yace "shi yasa kullum store da freezer dinki ke acike kenan basuyin qasa ko?good.....to ni a gidana dole adinga cin abinci.....oya....bismillah ina son naga plate empty" Daga haka ya maida kansa gun wayarsa dake ruri ya fara amsa wayar mr lien,ci take amma sam bata so,da zarar kuma ta tsaya suke hada ido dole take ci gaba da ci,sai gashi taci abinci mai yawa wanda ita kanta ta jima rabon data ci,ta ture plate din tana dan taba cikinta da taji yayi fam tana yatsina fuska yayi mata wani irin qabe qabe babu dadi, "I think u filled your stomach,let me see" ya fadi yana qarashe kashe wayar"qwalalo ido tayi tana tunanin anya kan aliyyu daya?ciwon cikinsa na jiya kodai ya taba shi?,she dont know why he behaving like dis?,cikin nata zaya ce ta ta yaye rigarta ta nuna masa?,ta dawo cikin hayyacinta lokacin da ya zare mata ido yace "aha show me" ba shiri cikin sanyin jiki ta dage rigar sanyin hadi da shirt din dake ciki,cikinta ya bayyana, ashafe yake tamkar zai hade da bayanta,ya zuba mishi ido,soft skin tata ta bayyana kanta ko ba'a fada maka,wani irin magnet ke fusgarsa,ya dubeta ta tsira mata ido duk a rude take,muryarsa can qasan maqoshinta yace "up" yana ci gaba da kallon cikin,a zaton ta bai gani bane sosai ta dan sake janye masa rigar "up again" ya sake fada,sai ta tsorata don dukka cikin nata ya fito waje da zarar ta sake janye rigar qirjinta(breast) ne zai bayyana Ganin bata sake dagewarba yasa ya dauje idanunsa daga kallon
Chapter 50 · 0% Book details