← Book details Waya San Gobe Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 84

Sashe 59

Waya San Gobe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

mai zan samu?" Ta tabe baki sannan tace "ba komai tunda ai ba yau kace zaka dawo ba ganinka kawai mukayi tsakar rana,ni ta window ma na hageka ka fice" "ni din ma haka dawowar ta zo min" cikin son bin qwaqwafi tace "ko fadilan ce ta takura sai andawo?" "Eh"kawai yace mata cikin som kashe maganar don tamkar allura ce akan qurji idan aka tada masa da zancan fadila, "but ban gata ba kuma ma bangaren ta akle yake" "eh"ya kuma cewa dai bai buqatar taci gaba da yin maganar Shiru ya dan ratsa dakin kanta na jingine a kafadarsa,kishin fadilan duk ya cikata gani take kamar wani gun ya kuma kaita don ta huta,samira ta danno kai harda sallamarta kamar gaske kai a sunkuye,duk da haka saboda tsabar neman bala'i sai da ta gasawa salima hara ra,ai kuwa itama bata yi qasa agwiwa ba ta rama don ba qaramin adashen tsiya suka dinga shukawa ba sanda baya nan,kullum sai an raba gari a gidan saidai idan garin Allah bai waye ba,amma kwana suke su wuni suna abu guda kamar karnuka,suna hada ido da aliyyu ya bata tasa hararar tayi saurin sadda kai qasa,gefansa ta zauna cikin tausasa murya tace masa "sannu da zuwa an dawo lafiya?" "Lafiya"yace mata a taqaice,duk sai taji ta muzanta,tafi kowa sanin laifinta,gargadi mai zafi babu irin wanda bai musu ba kafin ya tafi kan fice fice,duk da yau ma tsautsayine amma ta kwan biyu bata saci fita din ba,wannan ne satar fitarta ta hudu salima tayi biyu tana tsammanin tayi na qarshe tunda ya kusa dawowa qasar bata san yau ya dawo ba Shiru ya gauraye falon kowa da abinda yake saqawa cikin zuciyarsa,aliyyu yafi kowa nisan kiwo cikin duniyar tunani,"dear ya kamata muje ku kwanta ko?"salima ta fada tana kashe masa idanu,da sauri samira ta dago "kamar yaya?"cikin daga murya samira ta tambayeta,itama ta dubeta ta mayar mata "kamar yadda kika kunnuwanki suka ji nace"da sauri ta nunata da yatsa "baki isa ba wallahi kinyi kadan don yadda kike buqatarsa nima hakan take.....ke bari ma nayi miki dalla dalla...yadda kike a matse ni nama fiki matsuwa"ta fada tana wani gayara zama,sai kuwa cece kuce ya barke dama kadan kowacce take jira 'yar uwarta ta tabo ta,sak yayi yana kallonsu,sai ya zama kamar wani mutum mutumi,babu wadda tayi masa wani abu na azo a gani a matsayinsa na matafiyin da yayi wata judu bai cikin iyalinsa yanzu ya dawo musu,shegiya shinkafa fara sol da yaji babu wadda ta turo masa tace gashi,amma aqalla ai ko tsakar dare ya dawo idan da tunani sa tashi su sama masa wani abu ko drink ne,to amma ga drink din ma jibge a freezer dinsa su dauko ma su hada masa da cup suce masa gashi babu wadda ta iya yin hakan,babu wani welcoming na arziqi,amma ko wacce burinta ya kwanta da ita ya biya mata buqata kamar wani inji Ganin abun nasu ma shirin wuce makadi da rawa don har an fara 'yar lakace lakacen hanci yasa ya dakatar da su ta hanyar daka musu tsawa don idan ba tsawar ya musu ba yadda suka kacame babu wadda zata iya jiyo shi"bana buqatar kowa cikinku,duk ku tashi ku bani waje,tunda ku baku iya kwantarwa da mutum hankali ba saidai ku tayar masa,ko kwana daya banyi ba cikin gidana amma kun fara samin bacin rai?" Tuni samira ta miqe,salima ta rausayar da kai tana cewa "amma aliyu ......." "amma me?Please stay away" ya fada yana nuna mata hanya,samira ta sheqe da dariya tana cewa "ato saiki taso ai mu daye,ki daina naci haka kowa sai ya riqe kwadayinsa tunda yace bai yi" wani banzan kallo alin ya watsawa samiran yana cewa "kin sanni,kada ki bari muyi arangama dake bani da kyau!"tasan hakan kuwa tuni tayi gaba salima ta bita a baya,yan jiyo kici kicin kokawarsu a bakim part din nasa,yayi banza da su _*12 PM*_ Sha biyu na dare ya dinga gwada maqullan hannunsa a qofar har ya samu na qofar tata,ya tura ya shiga ya haska makunnin fitila ya danna dukka qwayayen suka kama bangaren ya cika da haske,qamshi falon yake tamkar tana nan,kamar bata yi tafiya ba na tsawon watanni hudu ba,hakanan komai akillacensa,kai tsaye ya shige bedroom dinta,shima dai kamar falon cikin qamshi yake da tsafta,gadonta a dame yake komai ajere,pant da brassier dinta ne kawai a gefan pillow,ya qarasa ahankali ya haye gadon hadi da kwanciya pillow din ya janyo hadi da rungumeahi tsam tsam a qirjinsa,qamshi pillow din yake kamar a shafa masa turare ne,ya sake miqa hannu ya dago pant and brassier din farare qal ya zuba musu ido,a hankali ya mannaau a hancinsa yana sheqar qamahin turarenta na shamsul imaraat A hankali ya shiga sosai cikin zurfin tunani,yanayinta,halayenta,dabi'unta,haquri irin nata kawaici da yakanah,bai taba ganin ta tana fada irin nasu samira ba,bai taba ganinta tana koda sa'insa da daya daga cikinsu ba,duk wata sabga tasu bata ciki,shi da kansa alokutan baya har haushi yake ji idan yaga bata damu da fadan kishi ba,ashe so ne?,ashe haushi yake ji yana ganin kamar bata sonshi ne? Juyi kawai yake samar gadon,jinsa yake tamkar wani maraya,wani irin kewa yakeji mai zafi da radadi tana kamashi,ya riga da ya saba da kwana jikinsu na gogayya da na juna,ya saba da sheqar qamshinta,sosai ya sake rungume pillow yana sakin numfaahi sama sama,yafi awa biyu kafin wani wahalallen bacci awon gaba da shi ,ko cikin baccin ma bata qyaleshi ya huta ba sai da ta jawo masa yin wanka,ya dawo bakin gadon yq zauna yana tsane jikinsa da towel dinta,idanunsa ya sauka kan wani dan kyakkyawan madaidaicin frame da yake zaune dirshan bisa side bed,yasa hannu a hankali ya dauki hoton ya zuba masa ido yana kallonta,murmushi take yi sosai,fararen haqoranta jerarru reras sun bayyan,yar lobawar dake tsakiyar habarta ta fito sosai,ya sanya bakinshi saitin lips nata yayi kissing,murya qasa qasa yace "I love you"ya dan manna hoton a qirjinshi Sai da yayi sallar asuba sannanya baro bangaren har ya fito ya manta bai dauko hoton ba ya koma ya dauko abinsa,kan side drower dinshi ya kafa sa,yana shiryawa yana kallon hoton har ya kammala shirinsa tsaf cikin shadda fara tas mai asalin tsadar sai maiqo take da daukan idanu,yayi masifar kyau saidai fuskarnan na kirtibe,qarfe bakwai ga fito ya soma da sashen samira don itace a damansa,yana tura qofar ta bude alamuna bude ta kwana,kai tsaye ya zarce bedroom din ta don yasan tana ciki,yana tafiya yana bin falon da kallo tamkar dakin ajiyar shirgi haka ta maidashi Dai dai ya sameta saman gado hannu can qafa can,gajeran gashinta maras tsawo wanda bai hadu da mace mai gyara ba duk ya hautsine ya tashi yayi cako cako kamar bishiyar qaya(don ko baki da tsawon gashi matuqar ke mai gyara ce to zai bada sha'awa,amma komai tsawonsa indai ba gyara abin qyamata zai zama),sosai iyyu ya tsani irin wannan kwanciyar tata,don kuwa insha Allahu kuka hada gado daya da samira to ranar fa ka shieya zaka daku da hannu da qafa,haka kullum yake fama da ita,shi yasa ya gwammace ya matseta a jikinsa ayi baccin haka Ya dan taba qafarta yana kiran sunanta,saidai kamar gawa ko motsi bata yi ba bare yasa ran zata tashi jan minsharinta kawai take,yasan hali dama bata motsa din ba kuwa har sai da ya dage ya daki daki qafar da hannu sannan ta miqe a zabure tana cono baki gami da mutsitstsika ido,sai da ta gama mutstsike idanun sannan ta dubeshi,ganin aliyyu a tsaye ya sata shiga taitayinta,addu'a take cikin ranta Allah yasa maganar laifinta yazo yayi mata,don tasan halinshi shirunsa ba abu mai dadi yake haifarwa ba,fuska a murtuke yace "hala ko sallar asuba bakiyi ba?" Nan ta hau kame kame "zan....zanyi....yanzu ne na tashi ai..." "good" yace da ita cikin takaici yana gayada kai,ya juya zai fita "zan fita sai na dawo" "to" tace kaar wadda aka tilasta ta sai ta fadi hakan,Allah Allah take ya fitan taja bargo ta koma barcinta,bata sani ba shi din ma Allah Allah yake ya bar dakin,don zarnin bandakinta dake cikin bedroom din shi ke busowa har cikin dakin gadon,sai taga kuma ya juyo hadi da cewa "bani key din motarki da wayarki" cikin marairaita tace "don Allah kayi haquri bazan sake ba" a zafafe ya kalleta "will you keep quiet or not? Da baki iya bada haqurin ba kenan sai yanzu?common bani key da phone nace"nuni tayi masa kan hargitsatstsen dressing mirror dinta,ya juya ya kalli kan madubin saboda hargitsewarsa ma shi bai hango wata waya ba ballantana maqulli "ok...ni zanje ma na dauko miki ko?" Dolenta ta sauka daga kan gadon ta dauko ta miqa masa tamakar zata yi ihu,ya amsa ya fice da sauri ba tare da yace mata qala ba don zarnin sake busowa yake,kuma ko yace ta gyara ba zata yi din ba don sau nawa yana fama da ita kan hakan sai tave masa yau fa sati daya kacal da wanke shi ba wani dadewa yayi ba Salima ma na bisa gadon a nade bacci na dibarta sama sama,ita din ma sai lokacin bakwai da wani abu ta yi tata sallar,saidai yana sallamar ta amsa gami da miqewa zaune kan gadon,murmushi take masa wanda hakan ya sanyashi rage daurin fuskarsa"kar daiace har ka fito" ta soma cewa,ya kalleta yace "eh"yana mamakin yadda basu iya gaisuwa wa mijinsu ba,babu wadda ta fado masa sai fadilan,duk safiya sai ya gaidashi kamar yadda ya zame mata qajibi sannu da zuwa da adawo lafiya duk da sai yaso yake amsawa amma hakan bai dameta ba haqqinta take saukewa, "amma yaci ace yau a gida zaka wuni ko" ta sake shigowa da wani qorafin "a hakan kuna batan ran babu wani caring bare a faranta maka"yayi zancqn cikin zuciyarsa,a fili sai yace "maiduguri zani zuwa anjima zan dawo insha Allah"cikin tuhuma tace "maiduguri?gurin wa?...." "stop your suspicion,sai na dawo" ya katseta, "madalla"tave tana binsa da cike da kishi har ya fice Cikin motarsa qirar 4matics fara ya zabi yin tafiyar shi kadai,bayan yin addu'o'in matafiyi ya kunna motar ya fice daga gidan cikin tsammani mai yawa da fata na gari akan kanshi *mrs muhammad ce* [10/16, 2:10 PM] Salma *WA YASAN GOBE?...* *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* *PART 3* Cikin
Chapter 59 · 0% Book details